ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ribar Noman Citta A Nijeriya

by Abubakar Abba
4 years ago
Noman citta

An dade ana noman citta a kasar nan, musaman Arewacin Nijeriya, ganin yadda noman ke samar wa manonanta kudi masu yawa.

A jihar Sakkwato da Zamfara da Jigawa da Kano da Katsina da Kudancin Kaduna, ana zuwa domin siyenta.

  • Yadda Ake Noman Zaitun A Zamanance

karamar hukumar Kaciya da Kagarko da Kubaca da ke cikin karamar hukumar Kagarko da Barde da Fori da ke karamar hukumar Jama’a, sai Kwoi da ke karamar hukumar Jaba, su ne manyan garuruwan da ke samar da kaso ma fi yawa na citta.
Wadannan yakunun, a daukacin fadin kasar nan inda nan ana zuwa siyenta, inda wasu kuma ke zuwa garin Kafancan domin siyenta.

ADVERTISEMENT

Rahotannin sun bayyana cewa, a duk mako, tireloli 15 zuwa fiye da haka ke jigilarta daga Kafancan, inda a kowace jigila daya, ake dakon tan daga 26 zuwa 28.

Bugu da kari, nomanta da kasuwancinta da gyaranta na daga cikin harkoki ma fi girma da ke bunkasa harkokin arziki da zaman lafiya da hadin kai a tsakanin al’ummar Kudancin Kaduna.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Cittar da ake noma wa a Kudancin Kaduna, wadda kuma aka yi amanna tana daga cikin ma fi kyau a duniya, a kan fara dibanta daga watan Nuwamba zuwa watan Afirilun.

A lokacin da ake ganiyar aikin cittar, mutane da yawa da suka hada da manya da kananan ’yan kasuwa da dillalai da direbobi da masu dako da masu gadi da masu aikin tsinta da shika da gyaran cittar, kowane kan kama aiki gadan-gadan, baya ga manomanta da ke fito wa da ita domin siyarwa a kasuwa.

Haka kuma, matasa na daga cikin wadanda ke cin gajiyar aikinta a karamar hukumar Jama’a da kuma garin Kaciya.
Sannan,haifaffun garuruwan, akwai masu aikin cittar da musamman suke baro garuruwansu su taho yankin don aikin gyaranta a kowace shekara.

Rahotannin sun ci gaba da cewa, lokacin da gwamnatin tarayya ta bayar da umarnin a garkame iyakokin Nijerya, an ci gabna da jigilarta daga Nijeriya zuwa ketare kamar irin su, kasashen Benin da Ghana da Togo.

Sai dai, masu harkar cittar zuwa wannan yanki sun tabka asara a daidai lokacin da kasar ta rufe iyakokinta, inda hakan ya rutsa da tarin manyan motoci dauke da danyarta.

An ruwaito wata mata mai suna Jummai Jacob da ta dade tana sana’ar gyaranta a garin Kaciya ta bayyana cewa, ta fara aikin gyaranta ne a 2016.
Jummai ta ce ta fara gyaranta ne da buhu hudu a ranar farko amma a yanzu ina iya gyara buhu 30, inda ake biyanmu naira 100 a kan kowane buhu.

Jummai ta ce, da wannan aikin ne take daukar nauyin hidamar iyayenta da kula da karatun ’ya’yanta biyu.
Shi kuwa wani Sani Baba ya ce, ya kwashe fiye da shekara ashirin yana aikin cittar, inda ya kara da cewa, tun lokacin da ake biyansu naira 15 zuwa 20 a kowane buhu.

Ya kara da cewa, da aikin ne yake kula iyayensa da karatunsu, inda ya kara da cewa, aikin buhu 40 a kowace rana amma yanzu saboda leburori sun yi yawa ciki har da matan aure, hakan ya sa buhu 25 kawai take samu.

Shi ma wani mai aikin Malam Abdullahi, ya ce ya shafe shekara hudu yana sana’ar siyan da buhunan citta bayan an tsince manya da kanana an tankade ta, sai a saya domin sayar wa ’yankoli.
Ya ce da wannan aikin yake daukar nauyin karatun ’ya’yansa da kuma yin dawainiyar gidansa.

Shi kuma wani matashi da yake yin aikin Sani Musa ya bayyana cewa, da kudin da yake samu na aikin gyranta ne yake taimaka wa kansa da kuma iyayensa, inda ya ci gaba da cewa, ya fara zuwa aikin ne tun ina dan shekara 11, inda yake samun daga naira 200 zuwa naira 500.

Noman citta
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Sin: Ya Kamata Kwamitin Sulhu Ya Gaggauta Daidaitawa Da Ma Dage Takunkuman Da Aka Kakabawa Kasashen Afirka Da Ba Su Biya Bukatun Halin Da Ake Ciki Ba

Sin: Ya Kamata Kwamitin Sulhu Ya Gaggauta Daidaitawa Da Ma Dage Takunkuman Da Aka Kakabawa Kasashen Afirka Da Ba Su Biya Bukatun Halin Da Ake Ciki Ba

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.