ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ribar Noman Citta A Nijeriya

by Abubakar Abba
4 years ago
Noman citta

An dade ana noman citta a kasar nan, musaman Arewacin Nijeriya, ganin yadda noman ke samar wa manonanta kudi masu yawa.

A jihar Sakkwato da Zamfara da Jigawa da Kano da Katsina da Kudancin Kaduna, ana zuwa domin siyenta.

  • Yadda Ake Noman Zaitun A Zamanance

karamar hukumar Kaciya da Kagarko da Kubaca da ke cikin karamar hukumar Kagarko da Barde da Fori da ke karamar hukumar Jama’a, sai Kwoi da ke karamar hukumar Jaba, su ne manyan garuruwan da ke samar da kaso ma fi yawa na citta.
Wadannan yakunun, a daukacin fadin kasar nan inda nan ana zuwa siyenta, inda wasu kuma ke zuwa garin Kafancan domin siyenta.

ADVERTISEMENT

Rahotannin sun bayyana cewa, a duk mako, tireloli 15 zuwa fiye da haka ke jigilarta daga Kafancan, inda a kowace jigila daya, ake dakon tan daga 26 zuwa 28.

Bugu da kari, nomanta da kasuwancinta da gyaranta na daga cikin harkoki ma fi girma da ke bunkasa harkokin arziki da zaman lafiya da hadin kai a tsakanin al’ummar Kudancin Kaduna.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Cittar da ake noma wa a Kudancin Kaduna, wadda kuma aka yi amanna tana daga cikin ma fi kyau a duniya, a kan fara dibanta daga watan Nuwamba zuwa watan Afirilun.

A lokacin da ake ganiyar aikin cittar, mutane da yawa da suka hada da manya da kananan ’yan kasuwa da dillalai da direbobi da masu dako da masu gadi da masu aikin tsinta da shika da gyaran cittar, kowane kan kama aiki gadan-gadan, baya ga manomanta da ke fito wa da ita domin siyarwa a kasuwa.

Haka kuma, matasa na daga cikin wadanda ke cin gajiyar aikinta a karamar hukumar Jama’a da kuma garin Kaciya.
Sannan,haifaffun garuruwan, akwai masu aikin cittar da musamman suke baro garuruwansu su taho yankin don aikin gyaranta a kowace shekara.

Rahotannin sun ci gaba da cewa, lokacin da gwamnatin tarayya ta bayar da umarnin a garkame iyakokin Nijerya, an ci gabna da jigilarta daga Nijeriya zuwa ketare kamar irin su, kasashen Benin da Ghana da Togo.

Sai dai, masu harkar cittar zuwa wannan yanki sun tabka asara a daidai lokacin da kasar ta rufe iyakokinta, inda hakan ya rutsa da tarin manyan motoci dauke da danyarta.

An ruwaito wata mata mai suna Jummai Jacob da ta dade tana sana’ar gyaranta a garin Kaciya ta bayyana cewa, ta fara aikin gyaranta ne a 2016.
Jummai ta ce ta fara gyaranta ne da buhu hudu a ranar farko amma a yanzu ina iya gyara buhu 30, inda ake biyanmu naira 100 a kan kowane buhu.

Jummai ta ce, da wannan aikin ne take daukar nauyin hidamar iyayenta da kula da karatun ’ya’yanta biyu.
Shi kuwa wani Sani Baba ya ce, ya kwashe fiye da shekara ashirin yana aikin cittar, inda ya kara da cewa, tun lokacin da ake biyansu naira 15 zuwa 20 a kowane buhu.

Ya kara da cewa, da aikin ne yake kula iyayensa da karatunsu, inda ya kara da cewa, aikin buhu 40 a kowace rana amma yanzu saboda leburori sun yi yawa ciki har da matan aure, hakan ya sa buhu 25 kawai take samu.

Shi ma wani mai aikin Malam Abdullahi, ya ce ya shafe shekara hudu yana sana’ar siyan da buhunan citta bayan an tsince manya da kanana an tankade ta, sai a saya domin sayar wa ’yankoli.
Ya ce da wannan aikin yake daukar nauyin karatun ’ya’yansa da kuma yin dawainiyar gidansa.

Shi kuma wani matashi da yake yin aikin Sani Musa ya bayyana cewa, da kudin da yake samu na aikin gyranta ne yake taimaka wa kansa da kuma iyayensa, inda ya ci gaba da cewa, ya fara zuwa aikin ne tun ina dan shekara 11, inda yake samun daga naira 200 zuwa naira 500.

Noman citta
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
Sin: Ya Kamata Kwamitin Sulhu Ya Gaggauta Daidaitawa Da Ma Dage Takunkuman Da Aka Kakabawa Kasashen Afirka Da Ba Su Biya Bukatun Halin Da Ake Ciki Ba

Sin: Ya Kamata Kwamitin Sulhu Ya Gaggauta Daidaitawa Da Ma Dage Takunkuman Da Aka Kakabawa Kasashen Afirka Da Ba Su Biya Bukatun Halin Da Ake Ciki Ba

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.