• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikici Ya Barke Kan Zaben Kananan Hukumomin Jihar Neja

by Muhammad Awwal Umar
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Rikici Ya Barke Kan Zaben Kananan Hukumomin Jihar Neja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun bayan da hukumar zabe ta Jihar Neja (NSIEC) ta fitar da jadawalin zabukan kananan hukumomin Neja aka fara tayar da jijiyoyin wuya tsakanin gamayyar jam’iyyun siyasa da majalisar dokokin jihar. 

Kamar yadda hukumar zaben NSIEC ta fitar jadawalin zaben zai kasance ne farkon watan Nuwanba, wata uku kafin babban zaben 2023.

  • Shugaba Buhari Zai Kawo Karshen Rashin Tsaro A Nijeriya -Buratai
  • Ziyarar Babbar jami’ar Lithuania A Taiwan Shirme Ne

Wanda jadawalin zaben bai yi wa wasu ‘yan siyasa dadi ba, inda aka rika shirya taruka kan kiran gwamnatin jiha ta janye kudurinta na zaben a daidai wannan lokacin.

Dan majalisar jiha mai wakiltar karamar hukumar Bosso, Hon. Malik Madawaki Bosso ya gabatar da kuduri ga majalisar, inda ya nemi majalisar da dakatar da hukumar zaben ta jiha kan zaben bisa wasu dalilan doka.

Da yake bayyana matsayar majalisar, shugaban majalisar dokokin jihar, Rt. Hon. Abdullahi Bawa Wuse, ya nemi gwamnatin jiha da ta dakatar da hukumar zaben na kudurin gudanar da zaben wanda ya zo daidai da sashe na ashirin (20) na dokar zaben kananan hukumomi na shekarar 2002 da sashe na ashirin da tara (29) (1) na dokar zabe na 2022.

Labarai Masu Nasaba

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

Kudurin da dan majalisar Madawaki ya gabatar ya ce wa’adin shugabannin kananan hukumomi zai kare ne ranar 12 ga watan Disambar wannan shekarar.

Dan majalisar ya ce jadawalin zaben da hukumar zaben ta jiha ta fitar domin fara shirye-shiryen zaben kananan hukumomi a jihar, wanda ta tsara zaben fitar da gwani zai kasance tsakanin ranar 20 zuwa 27 ga watan Agusta, inda kuma ta ce za a gudanar da zaben ranar 5 ga watan Nuwamba ya saba wa dokar zaben jiha.

Ya kara da cewar tsakanin ranar 27 ga watan Agusta zuwa 5 ga watan Nuwamba kwana 35 ne, ya ce dokar ta tanadi cewa tsakanin zaben fid da gwani da babban zabe kwanaki dari da tamanin (180) ne.

Dan majalisar ya ce dokar da ta samar da matsayin kananan hukumomi na 2002, ita ce ta haifar da dokokin zaben 2022 da majalisar dokokin jiha ta gabatar kuma ya zama dokar zabe kananan hukumomi a Jihar Neja da wadda aka gabatar a shekarar 2002 da ta 2001.

Madaki ya ce sashi na ashirin (20) na dokokin zaben kananan hukumomi na 2002, ya bayyana za a samar da shugabannin kananan hukumomi ne bisa tsarin zabe da kuma tabbatar da cewar an bi tsarin doka kamar yadda sashi na sha tara (19) ya tanada.

Ya kara da cewar sashi na 29 sakin layi na daya na dokar zabe 2002, ya ce ba wata jam’iyyar siyasa za ta shiga zabe kasa da kwanaki 180 tsakanin zaben fid da gwani da babban zabe, sai sun mayar wa hukumar zabe sunayen wadanda suka samu nasarar zaben fid da gwani.

Ya ce a bayyana take cewar NSIEC za ta gudanar da zaben ba bisa doka ba idan ta ci gaba da shirya yunkurin gudanar da zaben a wannan lokacin kamar yadda ta fitar da jadawalin zaben.

Da yake amsa tambayoyin manema labarai, shugaban gamayyar jam’iyyun siyasa sha takwas “IPAC” da ke yunkurin shiga zaben, Malam Muhammad Bello Maikujeri, ya ce ‘muna nan kan matsayanmu na shiga zaben kamar yadda NSIEC ta fitar jadawalin zaben.’

Ya ci gaba da cewa majalisar ce ta yi sabon kudurin da ya bai wa shugabannin kananan hukumomi wa’adin shekaru uku kan karagar mulki, sanin kowa ne shugabannin kananan hukumomi na yin wa’adin shekaru biyu ne, amma bayan wannan dokar kotu ta tabbatar wa shugabannin kananan hukumomi wa’adin shekaru ukun, kuma wa’adin mulkinsu zai kare ne a ranar 12 ga watan Disamba.

Ya ce, “Saboda haka daga ranar 12 ga watan Disamba dole ne su sauka, amma ita majalisar dokokin jiha da ke tayar da jijiyoyin wuya ta manta cewa ita ce ta yi dokar, kuma a sabon dokar da muke amfani da shi da ya bai wa shugabannin kananan hukumomi wa’adin shekaru uku, ba ta bayyana gwamnatin rikon kwarya ba. “Idan ta natsu da kyau, hukumar zabe ta NSIEC ta yi abin da ya dace, domin ba zababbiyar gwamnatin karamar hukuma da za ta mika mulki hannun wani kantoma ko rikon kwarya bisa yadda suka tsara dokar.

“Saboda haka, wannan ba hurumin majalisar dokokin jiha ba ne, kotu ce kawai za ta iya warware abin da sabon dokar ya kunsa.

Mu IPAC, mun gamsu kuma mun amince jam’iyyu su ci gaba da shirye-shiryen zaben kananan hukumomi, domin muna magana ne a kan doka ba ra’ayin wani ba.

“Dokar zaben Jihar Neja ba ta samar da wani sashen rikon kwarya ko mika mulki ga wani a karamar hukuma ba, sai dai zababben shugaba. A yau mun ziyarci shugaban hukumar zabe ta Jiha Neja (NSIEC), Alhaji Aminu Baba domin bayyana masa matsayin IPAC a kan wannan takaddamar, mun tsaya ne a kan shiga zabe, kuma mun umurci sauran jam’iyyu su ci gaba da shirye-shiryen fuskar zaben kananan hukumomi na ranar 5 ga watan Nuwamba kamar yadda jadawalin NSIEC ta tsara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: NejaRikiciSiyasaTambarin DimokuradiyyaZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Martanin El-Rufa’i: Ko Gawata Ba Za Ta Kusanci PDP Ba

Next Post

Ko Makiyan Buhari Sun San Aikin Da Ya Yi Yafi Na Gwamnatocin Baya -Minista

Related

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

1 day ago
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar
Tambarin Dimokuradiyya

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

1 day ago
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

1 week ago
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

4 weeks ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

4 weeks ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

4 weeks ago
Next Post
Ko Makiyan Buhari Sun San Aikin Da Ya Yi Yafi Na Gwamnatocin Baya -Minista

Ko Makiyan Buhari Sun San Aikin Da Ya Yi Yafi Na Gwamnatocin Baya -Minista

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.