• English
  • Business News
Thursday, May 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikici Ya Barke Kan Zaben Kananan Hukumomin Jihar Neja

by Muhammad Awwal Umar
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Rikici Ya Barke Kan Zaben Kananan Hukumomin Jihar Neja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun bayan da hukumar zabe ta Jihar Neja (NSIEC) ta fitar da jadawalin zabukan kananan hukumomin Neja aka fara tayar da jijiyoyin wuya tsakanin gamayyar jam’iyyun siyasa da majalisar dokokin jihar. 

Kamar yadda hukumar zaben NSIEC ta fitar jadawalin zaben zai kasance ne farkon watan Nuwanba, wata uku kafin babban zaben 2023.

  • Shugaba Buhari Zai Kawo Karshen Rashin Tsaro A Nijeriya -Buratai
  • Ziyarar Babbar jami’ar Lithuania A Taiwan Shirme Ne

Wanda jadawalin zaben bai yi wa wasu ‘yan siyasa dadi ba, inda aka rika shirya taruka kan kiran gwamnatin jiha ta janye kudurinta na zaben a daidai wannan lokacin.

Dan majalisar jiha mai wakiltar karamar hukumar Bosso, Hon. Malik Madawaki Bosso ya gabatar da kuduri ga majalisar, inda ya nemi majalisar da dakatar da hukumar zaben ta jiha kan zaben bisa wasu dalilan doka.

Da yake bayyana matsayar majalisar, shugaban majalisar dokokin jihar, Rt. Hon. Abdullahi Bawa Wuse, ya nemi gwamnatin jiha da ta dakatar da hukumar zaben na kudurin gudanar da zaben wanda ya zo daidai da sashe na ashirin (20) na dokar zaben kananan hukumomi na shekarar 2002 da sashe na ashirin da tara (29) (1) na dokar zabe na 2022.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

Kudurin da dan majalisar Madawaki ya gabatar ya ce wa’adin shugabannin kananan hukumomi zai kare ne ranar 12 ga watan Disambar wannan shekarar.

Dan majalisar ya ce jadawalin zaben da hukumar zaben ta jiha ta fitar domin fara shirye-shiryen zaben kananan hukumomi a jihar, wanda ta tsara zaben fitar da gwani zai kasance tsakanin ranar 20 zuwa 27 ga watan Agusta, inda kuma ta ce za a gudanar da zaben ranar 5 ga watan Nuwamba ya saba wa dokar zaben jiha.

Ya kara da cewar tsakanin ranar 27 ga watan Agusta zuwa 5 ga watan Nuwamba kwana 35 ne, ya ce dokar ta tanadi cewa tsakanin zaben fid da gwani da babban zabe kwanaki dari da tamanin (180) ne.

Dan majalisar ya ce dokar da ta samar da matsayin kananan hukumomi na 2002, ita ce ta haifar da dokokin zaben 2022 da majalisar dokokin jiha ta gabatar kuma ya zama dokar zabe kananan hukumomi a Jihar Neja da wadda aka gabatar a shekarar 2002 da ta 2001.

Madaki ya ce sashi na ashirin (20) na dokokin zaben kananan hukumomi na 2002, ya bayyana za a samar da shugabannin kananan hukumomi ne bisa tsarin zabe da kuma tabbatar da cewar an bi tsarin doka kamar yadda sashi na sha tara (19) ya tanada.

Ya kara da cewar sashi na 29 sakin layi na daya na dokar zabe 2002, ya ce ba wata jam’iyyar siyasa za ta shiga zabe kasa da kwanaki 180 tsakanin zaben fid da gwani da babban zabe, sai sun mayar wa hukumar zabe sunayen wadanda suka samu nasarar zaben fid da gwani.

Ya ce a bayyana take cewar NSIEC za ta gudanar da zaben ba bisa doka ba idan ta ci gaba da shirya yunkurin gudanar da zaben a wannan lokacin kamar yadda ta fitar da jadawalin zaben.

Da yake amsa tambayoyin manema labarai, shugaban gamayyar jam’iyyun siyasa sha takwas “IPAC” da ke yunkurin shiga zaben, Malam Muhammad Bello Maikujeri, ya ce ‘muna nan kan matsayanmu na shiga zaben kamar yadda NSIEC ta fitar jadawalin zaben.’

Ya ci gaba da cewa majalisar ce ta yi sabon kudurin da ya bai wa shugabannin kananan hukumomi wa’adin shekaru uku kan karagar mulki, sanin kowa ne shugabannin kananan hukumomi na yin wa’adin shekaru biyu ne, amma bayan wannan dokar kotu ta tabbatar wa shugabannin kananan hukumomi wa’adin shekaru ukun, kuma wa’adin mulkinsu zai kare ne a ranar 12 ga watan Disamba.

Ya ce, “Saboda haka daga ranar 12 ga watan Disamba dole ne su sauka, amma ita majalisar dokokin jiha da ke tayar da jijiyoyin wuya ta manta cewa ita ce ta yi dokar, kuma a sabon dokar da muke amfani da shi da ya bai wa shugabannin kananan hukumomi wa’adin shekaru uku, ba ta bayyana gwamnatin rikon kwarya ba. “Idan ta natsu da kyau, hukumar zabe ta NSIEC ta yi abin da ya dace, domin ba zababbiyar gwamnatin karamar hukuma da za ta mika mulki hannun wani kantoma ko rikon kwarya bisa yadda suka tsara dokar.

“Saboda haka, wannan ba hurumin majalisar dokokin jiha ba ne, kotu ce kawai za ta iya warware abin da sabon dokar ya kunsa.

Mu IPAC, mun gamsu kuma mun amince jam’iyyu su ci gaba da shirye-shiryen zaben kananan hukumomi, domin muna magana ne a kan doka ba ra’ayin wani ba.

“Dokar zaben Jihar Neja ba ta samar da wani sashen rikon kwarya ko mika mulki ga wani a karamar hukuma ba, sai dai zababben shugaba. A yau mun ziyarci shugaban hukumar zabe ta Jiha Neja (NSIEC), Alhaji Aminu Baba domin bayyana masa matsayin IPAC a kan wannan takaddamar, mun tsaya ne a kan shiga zabe, kuma mun umurci sauran jam’iyyu su ci gaba da shirye-shiryen fuskar zaben kananan hukumomi na ranar 5 ga watan Nuwamba kamar yadda jadawalin NSIEC ta tsara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: NejaRikiciSiyasaTambarin DimokuradiyyaZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Martanin El-Rufa’i: Ko Gawata Ba Za Ta Kusanci PDP Ba

Next Post

Ko Makiyan Buhari Sun San Aikin Da Ya Yi Yafi Na Gwamnatocin Baya -Minista

Related

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

3 weeks ago
Rikici
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

3 weeks ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

3 weeks ago
Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba
Tambarin Dimokuradiyya

Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya

4 weeks ago
2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara 
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Babu Dan Takarar Da Zai Iya Cin Zabe Ba Tare Da Goyon Bayan Arewa Ba – Baba Ahmed

4 weeks ago
arewa
Tambarin Dimokuradiyya

Kawunan Shugabannin Arewa Sun Rabu Kan Siyasar 2027

4 weeks ago
Next Post
Ko Makiyan Buhari Sun San Aikin Da Ya Yi Yafi Na Gwamnatocin Baya -Minista

Ko Makiyan Buhari Sun San Aikin Da Ya Yi Yafi Na Gwamnatocin Baya -Minista

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 5 Hukuncin Ɗaurin Wata 1 Saboda Awakinsu Sun Cinye Bishiyar Gwamnati A Kano

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 5 Hukuncin Ɗaurin Wata 1 Saboda Awakinsu Sun Cinye Bishiyar Gwamnati A Kano

May 22, 2025
‘Yan Majalisar Dokokin Nijeriya Sun Bukaci Karin Albashi

Yadda ‘Yan Majalisa Ke Cusa Ayyuka Marasa Amfani A Kasafin Kuɗi – Rahoto

May 22, 2025
Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum

Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum

May 22, 2025
‘Yansanda Sun Tarwatsa Wuraren Haɗa Jabun Taki A Bauchi, An Cafke Mutum 5

‘Yansanda Sun Tarwatsa Wuraren Haɗa Jabun Taki A Bauchi, An Cafke Mutum 5

May 21, 2025
Kocin Super Eagle Ya Gayyaci Ahmed Musa Buga Gasar Kofin Unity A Landan

Kocin Super Eagle Ya Gayyaci Ahmed Musa Buga Gasar Kofin Unity A Landan

May 21, 2025
Farar Dabarar Da Tsoffin Masana’antu Ke Yi A Kasar Sin Don Tafiya Da Zamani

Farar Dabarar Da Tsoffin Masana’antu Ke Yi A Kasar Sin Don Tafiya Da Zamani

May 21, 2025
Tottenham Ta Doke Manchester United A Wasan Karshe Na Europa 

Tottenham Ta Doke Manchester United A Wasan Karshe Na Europa 

May 21, 2025
Kotu Ta Soke Umarnin Kwace Filin Asibitin Tiamin, Ta Umarci Gwamnatin Kano Ta Biya Diyyar ₦2.6bn

Kotu Ta Soke Umarnin Kwace Filin Asibitin Tiamin, Ta Umarci Gwamnatin Kano Ta Biya Diyyar ₦2.6bn

May 21, 2025
Shirye-shiryen Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Minista

Shirye-shiryen Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Minista

May 21, 2025
Salon “Kasa Daya Manufa Daya” Ya Dace Da “Ayyuka Goma” Na Hadin Gwiwa Da Afirka

Salon “Kasa Daya Manufa Daya” Ya Dace Da “Ayyuka Goma” Na Hadin Gwiwa Da Afirka

May 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.