ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikici Ya Barke Wajen Jana’izar Dan Wasan Da Ya Kashe Kansa

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Rikici

Dan wasan kwallon kafar Tunisia Nizar Issaoui ya mutu sakamakon kunar da ya samu a lokacin wata zanga-zangar adawa da rashin adalcin ‘yan sanda, kamar yadda iyalinsa suka bayyana, lamarin da ya sa ya cinna wa kansa wuta.

Tun da farko dai an hango Issaoui cikin wani bidiyo da aka wallafa a intanet inda a ciki yake ihu cewa dan sanda sun zarge shi da ta’addanci bayan wata rashin jituwa tsakaninsa da wani mai sayar da kayan marmari.

  • Yadda Uwargida Za Ta Yi Kwalliyar Gida Da Sallah
  • Buhari Ya Dakatar Da Kwamishinan Zaben Jihar Adamawa

A wani sako na daban, ya ce ya yanke wa kansa hukuncin kisa ta hanyar wuta sai dai an samu kaurewar arangama a wajen jana’izar matashin mai shekara 35 ranar Juma’a a kauyensa Haffouz, kamar yadda kafafen yada labarai suka sanar.

ADVERTISEMENT

Dan sanda sun zargi Issaoui da aikata ta’addanci bayan da ya yi korafin cewa bai iya siyan ayaba kan kasa da dinare 10 ba kan kilo daya, ninki biyu na farashin da gwamnati ta saka, a cewar rahotanni.

A wani sakon Facebook, dan kwallon ya rubuta saboda sabani da wani mai sayar da ayaba kan dinare 10, ‘yan sanda suka zarge shi da ta’addanci saboda yin korafi a kan ayaba. An samu tashin hankali a jana’izar dan wasan yayin da masu zanga-zanga

LABARAI MASU NASABA

Shakirat Ta Tsallaka Mataki Na Ƙarshe Na Zama Gwarzuwar Ƴar Wasan Afrika

Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe

suka rika jefa wa ‘yan sanda duwatsu ya yin da su kuma jami’an suke watsa musu hayaki mai sa hawaye.

Tsohon dan wasan kungiyar US Monastir ta kasar Tunisia ne, kuma mahaifi ga ‘ya’ya hudu sannan dan uwansa ya fada wa ‘yan jarida cewa Issauoi ya kone sosai kuma likitoci ba su iya yin wani abu na ceto rayuwarsa ba.

Matakin da ya dauka ya yi daidai da wata zanga-zanga da aka yi a 2010 lokacin da wani mai siyar da kaya a bakin titi Mohamed Bouazizi ya cinna wa kansa wuta lamarin ya janyo zanga-zanga da ta kai ga hambarar da Shugaba Zine al-Abidine Ben Ali.

Shugaba Kais Saied mai ci, ya janyo ce-ce-ku-ce a 2021 lokacin da ya kori firaminista tare da dakatar da majalisar dokokin kasar kuma tun daga lokacin ya yi amfani da sabon kundin tsarin mulki wanda ya tabbatar da ikonsa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shakirat Ta Tsallaka Mataki Na Ƙarshe Na Zama Gwarzuwar Ƴar Wasan Afrika
Wasanni

Shakirat Ta Tsallaka Mataki Na Ƙarshe Na Zama Gwarzuwar Ƴar Wasan Afrika

November 15, 2025
Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe
Wasanni

Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe

November 14, 2025
Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati
Wasanni

Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati

November 14, 2025
Next Post
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

LABARAI MASU NASABA

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama

November 15, 2025
Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

November 15, 2025
Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

November 15, 2025
Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

November 15, 2025
Shakirat Ta Tsallaka Mataki Na Ƙarshe Na Zama Gwarzuwar Ƴar Wasan Afrika

Shakirat Ta Tsallaka Mataki Na Ƙarshe Na Zama Gwarzuwar Ƴar Wasan Afrika

November 15, 2025
Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

November 15, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

November 15, 2025
Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

November 15, 2025
Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

November 15, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.