• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikici Ya Barke Wajen Jana’izar Dan Wasan Da Ya Kashe Kansa

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Rikici

Dan wasan kwallon kafar Tunisia Nizar Issaoui ya mutu sakamakon kunar da ya samu a lokacin wata zanga-zangar adawa da rashin adalcin ‘yan sanda, kamar yadda iyalinsa suka bayyana, lamarin da ya sa ya cinna wa kansa wuta.

Tun da farko dai an hango Issaoui cikin wani bidiyo da aka wallafa a intanet inda a ciki yake ihu cewa dan sanda sun zarge shi da ta’addanci bayan wata rashin jituwa tsakaninsa da wani mai sayar da kayan marmari.

  • Yadda Uwargida Za Ta Yi Kwalliyar Gida Da Sallah
  • Buhari Ya Dakatar Da Kwamishinan Zaben Jihar Adamawa

A wani sako na daban, ya ce ya yanke wa kansa hukuncin kisa ta hanyar wuta sai dai an samu kaurewar arangama a wajen jana’izar matashin mai shekara 35 ranar Juma’a a kauyensa Haffouz, kamar yadda kafafen yada labarai suka sanar.

Dan sanda sun zargi Issaoui da aikata ta’addanci bayan da ya yi korafin cewa bai iya siyan ayaba kan kasa da dinare 10 ba kan kilo daya, ninki biyu na farashin da gwamnati ta saka, a cewar rahotanni.

A wani sakon Facebook, dan kwallon ya rubuta saboda sabani da wani mai sayar da ayaba kan dinare 10, ‘yan sanda suka zarge shi da ta’addanci saboda yin korafi a kan ayaba. An samu tashin hankali a jana’izar dan wasan yayin da masu zanga-zanga

LABARAI MASU NASABA

Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

suka rika jefa wa ‘yan sanda duwatsu ya yin da su kuma jami’an suke watsa musu hayaki mai sa hawaye.

Tsohon dan wasan kungiyar US Monastir ta kasar Tunisia ne, kuma mahaifi ga ‘ya’ya hudu sannan dan uwansa ya fada wa ‘yan jarida cewa Issauoi ya kone sosai kuma likitoci ba su iya yin wani abu na ceto rayuwarsa ba.

Matakin da ya dauka ya yi daidai da wata zanga-zanga da aka yi a 2010 lokacin da wani mai siyar da kaya a bakin titi Mohamed Bouazizi ya cinna wa kansa wuta lamarin ya janyo zanga-zanga da ta kai ga hambarar da Shugaba Zine al-Abidine Ben Ali.

Shugaba Kais Saied mai ci, ya janyo ce-ce-ku-ce a 2021 lokacin da ya kori firaminista tare da dakatar da majalisar dokokin kasar kuma tun daga lokacin ya yi amfani da sabon kundin tsarin mulki wanda ya tabbatar da ikonsa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?
Wasanni

Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

November 1, 2025
Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray
Wasanni

Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

October 30, 2025
Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi
Wasanni

Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

October 28, 2025
Next Post
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

November 1, 2025
Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

November 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

November 1, 2025
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa

November 1, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu

Jerin Gwarazan Taurarinmu

November 1, 2025
CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.