ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikici Ya Barke Wajen Jana’izar Dan Wasan Da Ya Kashe Kansa

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Rikici

Dan wasan kwallon kafar Tunisia Nizar Issaoui ya mutu sakamakon kunar da ya samu a lokacin wata zanga-zangar adawa da rashin adalcin ‘yan sanda, kamar yadda iyalinsa suka bayyana, lamarin da ya sa ya cinna wa kansa wuta.

Tun da farko dai an hango Issaoui cikin wani bidiyo da aka wallafa a intanet inda a ciki yake ihu cewa dan sanda sun zarge shi da ta’addanci bayan wata rashin jituwa tsakaninsa da wani mai sayar da kayan marmari.

  • Yadda Uwargida Za Ta Yi Kwalliyar Gida Da Sallah
  • Buhari Ya Dakatar Da Kwamishinan Zaben Jihar Adamawa

A wani sako na daban, ya ce ya yanke wa kansa hukuncin kisa ta hanyar wuta sai dai an samu kaurewar arangama a wajen jana’izar matashin mai shekara 35 ranar Juma’a a kauyensa Haffouz, kamar yadda kafafen yada labarai suka sanar.

ADVERTISEMENT

Dan sanda sun zargi Issaoui da aikata ta’addanci bayan da ya yi korafin cewa bai iya siyan ayaba kan kasa da dinare 10 ba kan kilo daya, ninki biyu na farashin da gwamnati ta saka, a cewar rahotanni.

A wani sakon Facebook, dan kwallon ya rubuta saboda sabani da wani mai sayar da ayaba kan dinare 10, ‘yan sanda suka zarge shi da ta’addanci saboda yin korafi a kan ayaba. An samu tashin hankali a jana’izar dan wasan yayin da masu zanga-zanga

LABARAI MASU NASABA

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

suka rika jefa wa ‘yan sanda duwatsu ya yin da su kuma jami’an suke watsa musu hayaki mai sa hawaye.

Tsohon dan wasan kungiyar US Monastir ta kasar Tunisia ne, kuma mahaifi ga ‘ya’ya hudu sannan dan uwansa ya fada wa ‘yan jarida cewa Issauoi ya kone sosai kuma likitoci ba su iya yin wani abu na ceto rayuwarsa ba.

Matakin da ya dauka ya yi daidai da wata zanga-zanga da aka yi a 2010 lokacin da wani mai siyar da kaya a bakin titi Mohamed Bouazizi ya cinna wa kansa wuta lamarin ya janyo zanga-zanga da ta kai ga hambarar da Shugaba Zine al-Abidine Ben Ali.

Shugaba Kais Saied mai ci, ya janyo ce-ce-ku-ce a 2021 lokacin da ya kori firaminista tare da dakatar da majalisar dokokin kasar kuma tun daga lokacin ya yi amfani da sabon kundin tsarin mulki wanda ya tabbatar da ikonsa.

Rikici
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City
  • Abba Ibrahim Wada
    LeBron James Zai Bar Los Angeles Lakers 
  • Abba Ibrahim Wada
    An Raba Jadawalin Gasar Premier Ta Ingila Ta Kakar Wasan 2026/2027
  • Abba Ibrahim Wada
    Daga 1930 Zuwa 2026: Yadda Aka Buga Wasa Na Dubu Ɗaya A Gasar Kofin Duniya

MASU ALAKA

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji
Wasanni

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

July 7, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA
Wasanni

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa
Wasanni

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

July 5, 2026
Next Post
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

LABARAI MASU NASABA

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

July 7, 2026
Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

July 7, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

July 7, 2026
Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

July 7, 2026
Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

July 7, 2026
'yansanda

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

July 7, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.