• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Jam’iyyar NNPP Ya Kazanta A Kano

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
6 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Rikicin Jam’iyyar NNPP Ya Kazanta A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan majalisar wakilai biyu daga jihar Kano, wadanda ke wakiltar jam’iyyar NNPP, sun bayyana ficewa daga tafiyar Kwankwasiyya karkashin jagorancin tsohon gwamnan Jihar Kano kuma jigo a jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso.

‘Yan majalisar wakilai biyu da suka hada da Aliyu Sani Madakin Gini, mai wakiltar Kano Municipal da Alhassan Rurum (Rano/Kibiya/Bunkure) sun tabbatar da cewa ba za su ci gaba da tafiyar Kwankwasiyya ba, lamarin da ke nuna cewa rikicin jam’iyyar NNPP a Kano ya kara kazancewa a halin yanzu.

  • Tinubu Ya Taya Trump Murnar Lashe Zaben Shugaban Kasar Amurka
  • Shugaba Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Kasa Da Kasa Game Da Tsaffin Al’adun Wayewar Kan Al’umma

Rurum, wanda tsohon shugaban majalisar dokokin Jihar Kano ne ya bayyana ficewarsa daga Kwankwasiyya a wata gajeriyar tattaunawa ta wayar tarho da jaridar Daily Trust.

Duk da dai bai bayar da wasu takamaiman dalilan da ya sa ya yanke wannan shawarar ba kafin karshen wayar, ana ganin ficewar Rurum na da alaka da rikicin da ya barke a baya-bayan nan da gwamnatin Jihar Kano karkashin jam’iyyar NNPP, musamman biyo bayan rusa masarautun biyar da gwamnatin ta yi.

Matakin dai ya shafi Rurum ne kai tsaye, domin yana rike da sarautar gargajiya ta Turakin Rano a cikin masarautar Rano da aka rushe a yanzu.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

A nasa bangaren, Madakin Gini wanda shi ne mataimakin shugaban marasa rinjaye na majalisar wakilai ya fito fili ya nisanta kansa daga Kwankwasiyya yayin da yake jawabi ga al’ummar mazabarsa a Kano ranar Lahadi.
“Daga yau, ni Aliyu Sani Madaki, ba ni da wata alaka da tafiyar Kwankwasiyya.

“Sun kore mu, sun ce ba mu da goyon baya, amma ba ma tsoron mu tsaya mu kadai. Su sani, babu wanda ba zan iya tinkara ba a tafiyar Kwankwasiyya daga sama har kasa, idan akwai bukatar hakan,” in ji shi.

Ya soki kungiyar Kwankwasiyya, wanda aka fi sani da alamar jajayen hula, dangane da yadda take tafiyar da jagorancinta.

Madaki Gini ya ce, “Wannan kungiya ta Kwankwasiyya, idan ya kasance kamar addini ce, to mun biya man biya hakkinmu. Amma sun ce ba mu da amfani, cewa ba mu da goyon bayan al’umma. Ya kamata su gane cewa babu wani a cikin Kwankwasiyya da ba zan iya fuskantarsa ba kai tsaye.”

A wani sako kai tsaye da ya aike wa magoya bayansa, Madakin Gini ya bukace su da su yi watsi da jar hula, inda ya kira hakan alama ce ta mika wuya da ya daina amincewa da ita. “Daga yanzu duk wanda ya dauke ni shugabansa a siyasa, to ya cire jar hula. Mata su cire jajayen mayafi. Mun gama!”
Da yake jawabi kan gwamnan Jihar Kano Abba Kabir Yusuf, Madakin Gini ya bayyana damuwarsa kan yadda gwamnan ke fuskantar matsin lamba a cikin tafiyar Kwankwasiyya.

Ya ce, “Sakona ga gwamna a fili yake. Suna kokarin raunata shi. Ina kira a gare shi ya tsaya da kafafuwansa, in ba haka ba, yana iya ruftawa. Ina da basira game da tsare-tsare a kansa.”

Idan dai za a iya tunawa a kwanakin baya ne wata kungiya ta fara wani yunkuri na neman gwamnan ya tsaya da kafafuwansa, ya daina daukar umurni daga wurin uban gidansa jagoran tafiyar Kwankwasiyya, wanda suka yi zargin cewa shi ke juya gwamnan wurin harkokin yau da kullum na gwamnati.

Haka zalika, rikicin da ke cikin jam’iyyar NNPP mai mulki a Kano na neman kazancewa, inda gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf ya fara kin daga wayar mai gidansa Rabi’u Musa Kwankwaso, sannan ya ki halartar tarukan da jagoran NNPP na kasa ya shirya.

Da alama dai wannan taken na “Abba tsaya da kafarka” ya fara tasiri a gurin gwamnan bayan da wasu ke ta motsa yadda zai karbe iko da jam’iyyar da kuma Kwankwasiyya daga hannun Kwankwaso.

Wasu majiyoyi sun shaida cewa tuni Abba ya fara amsa kira bayan da aka nusar da shi cewa Kwankwaso ne ke juya gwamnatinsa, inda kusan kashi 90 na makaman da Abba ya yi daga bangaren Kwankwaso ne.

Majiyoyi sun bayyana cewa Abba ba ya jin dadin karfa-karfa da Kwankwaso yake yi masa, inda ya fara nuna alamun bore domin ci gabansa na siyasa da ma Jihar Kano baki daya.

Tun lokacin da aka ga gwamnan a bikin murnar zagayowar haihuwar Kwankwaso, har yanzu ba su sake haduwa ba. Majiyoyi sun bayyana cewa duk tarukan da Kwankwaso ya kira a Kano da Abuja, Abba bai halarta ba.

Majiyoyin sun kkara da cewa har Abuja Kwankwaso ya bi gwamnan, amma Abba bai bari sun hadu ba, kuma har dan aike ya tura masa amma ya ki ganuwa a wajen Kwankwaso.

“Yanzu haka ana shirin hada kai da wasu ‘yan APC da ‘yan kungiyar Abba tsaya da kafarka wajen samo umarnin kotu da zai kori dukka wadannan ciyamomin da aka rantsar, sai dai a bai wa tsagin da Mai Shari’a Simon Amobeda ya tabbatar ana gobe zabe,” in ji majiyar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCNNPPRikicin Siyasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zaben Gwamnan Ondo: Jam’iyyu Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Zaman Lafiya – INEC

Next Post

Gwamnan Kano Ya Gabatar Da Kasafin Kuɗin 2025 Na Naira Biliyan 549.1

Related

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

2 weeks ago
NNPP
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

2 weeks ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

2 weeks ago
Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba
Tambarin Dimokuradiyya

Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya

3 weeks ago
2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara 
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Babu Dan Takarar Da Zai Iya Cin Zabe Ba Tare Da Goyon Bayan Arewa Ba – Baba Ahmed

3 weeks ago
arewa
Tambarin Dimokuradiyya

Kawunan Shugabannin Arewa Sun Rabu Kan Siyasar 2027

3 weeks ago
Next Post
Gwamnan Kano Ya Gabatar Da Kasafin Kuɗin 2025 Na Naira Biliyan 549.1

Gwamnan Kano Ya Gabatar Da Kasafin Kuɗin 2025 Na Naira Biliyan 549.1

LABARAI MASU NASABA

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.