• English
  • Business News
Tuesday, July 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Sudan: Gwamna Lawal Ya Bayar Da Aiki Kai Tsaye Ga Ɗaliban Zamfara 16 Da Suka Kammala Karatun Aikin Jinya

by Sulaiman
6 months ago
in Labarai
0
Rikicin Sudan: Gwamna Lawal Ya Bayar Da Aiki Kai Tsaye Ga Ɗaliban Zamfara 16 Da Suka Kammala Karatun Aikin Jinya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya bai wa daliban jihar su 16 da suka kammala karatun aikin jinya a jami’ar Sudan ta ƙasa da ƙasa nan take.

A ranar Alhamis ne Gwamna Lawal ya miƙa wa ɗaliban Jihar Zamfara da suka kammala karatun aikin jinya takardar shaidarsu daga jami’ar Sudan a gidan gwamnati da ke Gusau.

  • Gwamnati Ta Kara Yawan Kudaden Shiga Da Ake Bukatar FIRS Ta Tara A 2025
  • Bullar Cutar Da Ke Lalata Citta Ta Sa Farashinta Ya Sake Karuwa A Karo Na Shida

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris ya fitar, ta bayyana cewa an kwashe ɗalibai 66 da gwamnatin jihar Zamfara ta ɗauki nauyin karatunsu daga ƙasar Sudan a shekarar 2023 sakamakon rikicin da ake fama da shi a ƙasar.

Sanarwar ta ƙara da cewa, 16 daga cikin 66 da aka kora ɗalibai ne na aikin jinya waɗanda suka kasa yin jarrabawar ƙarshe kafin a fara yaƙin.

“A watan Satumbar 2023, Gwamna Dauda Lawal ya ɗauki matakin jin ƙai don taimakawa ɗaliban Zamfara 66 da aka kwashe daga Sudan.

Labarai Masu Nasaba

Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

“A bisa umarnin gwamna, kwamishinan ilimi na jihar Zamfara ya haɗa hannu da mahukuntan jami’ar Sudan domin gudanar da jarrabawar ɗalibai 16 na shekarar ƙarshe, wanda aka gudanar a Nijeriya.

“Jami’ar ƙasa da ƙasa ta Sudan ta aike da takardar shaidar kammala jarrabawar ɗaliban jami’ar jinya 16 da gwamna ya ba su.

A yayin gabatar da takardar shaidar, Gwamna Lawal ya ƙara wa ɗaliban da suka kammala karatun kwarin gwiwar zama jakadu nagari a Zamfara da kuma shiga ayyukan gwamnati na ceto jihar.

“Gwamnatina ta kafa dokar ta-baci a fannin ilimi, inda ta magance matsalolin da ke addabar jihar Zamfara. A halin yanzu muna samun ci gaba mai ma’ana kuma za mu zage damtse wajen saka jari mai yawa a cikin ilimi yayin da yake zama tushen ingantacciyar al’umma.

“Kwamishinan ya bayyana abubuwan da muka fuskanta kafin kammala karatun ku. Muna alfahari da ku.

“Muna ginawa da gyara asibitoci a duk faɗin jihar, amma ba a nan gizo ke saƙa ba. Ba zai yiwu a yi gine-gine ba tare da aikin da ake buƙata ba, don haka kun zo a lokacin da ya dace.

“Kun bi wannan fanni mai ɗimbin fa’ida na aikin jinya, kuma a sakamakon haka, za a ba ku aiki kai tsaye daga gwamnatin jihar Zamfara. Shugaban ma’aikata zai tabbatar da samun aikin ku a gwamnatin Zamfara a hukumance. Ina taya ku murna.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bullar Cutar Da Ke Lalata Citta Ta Sa Farashinta Ya Sake Karuwa A Karo Na Shida

Next Post

Hanyoyi Biyar Da Gwamnatin Tarayya Ta Samar Don Dakile Karancin Abinci A 2025

Related

Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina
Manyan Labarai

Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati

33 minutes ago
Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
Da ɗumi-ɗuminsa

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

9 hours ago
Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci
Da ɗumi-ɗuminsa

Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

10 hours ago
Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

13 hours ago
Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas, Ya Yi Jimamin Rasuwar Buhari, Ya Ce Mutuwa Ce Da Ta Girgiza Shi
Da ɗumi-ɗuminsa

SDP: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Wa El-Rufai Shaguɓe Da Ayyana Shi A Matsayin Ɗan Gudun Hijirar Siyasa

15 hours ago
Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja
Manyan Labarai

Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja

17 hours ago
Next Post
Hanyoyi Biyar Da Gwamnatin Tarayya Ta Samar Don Dakile Karancin Abinci A 2025

Hanyoyi Biyar Da Gwamnatin Tarayya Ta Samar Don Dakile Karancin Abinci A 2025

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina

Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati

July 29, 2025
An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

July 28, 2025
Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

July 28, 2025
Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

July 28, 2025
Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

July 28, 2025
An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

July 28, 2025
Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

July 28, 2025
Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

July 28, 2025
Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

July 28, 2025
Gwamnatin Sakkwato Ta Ƙaddamar Da Sababbin Motoci 30, Don Bunƙasa Sha’anin Sufuri A Jihar

Super Falcons Sun Iso Abuja Ɗauke Da Kofin WAFCON

July 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.