• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Sudan Zai Tilasta Sama Da Mutum 800,000 Gudun Hijira –MDD

•Rashin Tabbas Da Ake Ciki A Kasar

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Rahotonni
0
Rikicin Sudan Zai Tilasta Sama Da Mutum 800,000 Gudun Hijira –MDD
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadin cewa mutum sama da 800,000 ka iya tserewa daga Sudan sakamon kazamin fadan da ake yi tsakanin bangarorin soji biyu da ke gaba da juna.

Ana ci gaba da gwabza fada a Khartoum babban birnin kasar duk da alkawarin dakatar da bude wuta tsakanin bangarorin biyu.

  • Sudan: Rukunin Farko Na Daliban Nijeriya Sun Sauka A Abuja

Tuni dubban ‘yan kasar da ma suka fice daga kasar ta gabashin Afirka.

Kazamin fadan wanda ya barke tun sama da mako biyu da ya gabata tuni daman ya riga ya haifar da kwararar dubban ‘yan kasar ta Sudan zuwa kasashe makwabta da suka hada da Masar da Chadi da Jamhuriyar Tsakiyar Afirka.

Haka suma ‘yan kasashen waje gwamnatocin kasashensu da sauran hukumomi na ci gaba da kokarin kwashe su daga kasar, inda tuni suma dubbai suka fice.

Labarai Masu Nasaba

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

Dambarwar 2027 Da Kalubalen Da Ke Gaban Jam’iyyun Siyasa

A wani taron manema labarai kakakin ma’aikatar harkokin kasashen waje ta Amurka Bedant Patel, ya ce Amurkawa sama da 700 da ‘yan wasu kasashen aka kwashe ta tashar jirgin ruwa da ke garin Port Sudan a cikin kwana ukun da suka gabata, inda yawan Amurkawan da ake fitarwa daga kasar ya karu tun lokacin da aka fara rikicin.

Ya ce; ”A kokarin hadaka na kasashe, gwamnatin Amurka da hadin gwiwar kawayenta da abokan hadin gwiwa ta fitar da ‘yan Amurka sama da 1,000 daga Sudan tun lokacin da aka fara tashin hankalin.”
Sai dai wasu Amurkawa ‘yan asalin kasar ta Sudan a tashar jirgin ruwa ta Port Sudan da ke jiran a kwashe su sun ce suna nan zaune zaman jiran da ba su san takamaimai halin da ake ciki ba game da shirin tserad da su ba.

Suna kokawa da rashin samun wasu cikakkun bayanai daga hukumomi, inda har ta kai suna sayen abinci da ruwan sha da kudadensu a cewarsu.

Wani daga cikinsu ya ce kusan sa’a biyar suna zaman jiran tsammani babu wani bayani illa dai tun da farko an ce musu su yi hakuri.

Mohamed Madany ya ce shi bai ma sani ba ta jirgin ruwa za a kwashe su ko ta jirgin sama ba shi da masaniyar lokacin da zai bar wannan wuri.

Ya ce kusan kwana biyu bai ko runtsa ba, halin da suke ciki na da tsanani amma duk da haka sun jure.

Rikicin da ya shiga mako na uku, a tsakanin rundunar sojin kasar bisa jagorancin shugaban mulkin soja Janar Abdel Fattah al-Burhan da jagoran dakarun kar-ta-kwana na Rapid Support Forces, ko RSF, Janar Mohamed Hamdan Dagalo, wanda aka fi sani da Hemedti, na ci gaba da tsananta a sassan kasar daban-daban.

A babban birnin kasar Khartoum ya fi tsanani a babban filin jirgin sama na kasar da fadar shugaban kasa da kuma shelkwatar sojoji.
Fadan da ya barke ranar 15 ga watan Afirilu da ya kare zuwa yanzu a kiyasin hukumomi ya hallaka mutum sama da 600, da jikkata sama da 5000.

Na ga manyan motocin dakon kaya makare da gawarwaki A Yankin Darfur
Fada yana ci gaba da kamari a yankin Darfur da ke Yammacin Sudan, duk da tsagaita wutar da aka yi, inda Larabawa masu gwagwarmaya da makamai ke kai hari a kan manyan dakunan ajiyar kayayyaki, da kasuwanni da gidaje.

An kashe wani babban jami’in ‘yan sanda kuma wani ma’aikacin agaji dan kasar Sudan ya shaida wa BBC cewa yana nan boye a karkashin gado saboda tashin hankalin da ke faruwa.

“Ko ban-daki ba na iya yunkurawa na je,” cewar Abdallalateif ta wayar tarho daga birnin El Geneina.

Wutar rikici ta riga ta ruru inda ta haddasa zaman dar-dar na kabilanci, kamar yadda ya yi bayani.

Shekara da shekaru Darfur tana fama da tashin hankali tsakanin al’umominta daban-daban na Afirka da Larabawa.
A lokacin da wadanda ba Larabawa ba suka dauki makamai suna fada da gwamnati cikin shekara ta 2003, suna korafin cewa ana nuna musu wariya.

Gwamnati ta mayar da martani ta hanyar daukar mafiya yawa Larabawa ‘yan bindiga, wadanda aka zarga da ta’asa da cin zarafi da tursasawa.

Har zuwa zancen da muke yi da ku a yanzu, kungiyoyin ‘yan Afirka da dama da ke yankin Darfur suna zaune a sansanonin ‘yan gudun hijira don tsira da ransu.

A yanzu Larabawa masu dauke makamai da ke da alaka dakarun kai daukin gaggawa na RSF, wato jami’an tsaro masu kayan sarki da ke artabu da sojoji ga alamu suna amfani da gibin tsaro da ake da shi.

“Na ga manyan motocin dakon kaya makare da gawawwakin mutane, sannan Larabawa dauke da makamai, suna rike da bindigogi suna daka mana harara.

Iyaye Na Guduwa Suna Barin ‘Ya’yansu
Wata ‘yar Burtaniya da ta tsere wa rikicin Sudan ta bayyana yadda aka dauke ta daga kasar lokacin da take tsakiyar ‘ya’yan yayyenta wadanda suke kuka, suna rirrike ta domin kada ta tafi, ta bar su.

Waafa Salim ta tattauna da BBC a filin jirgin Larnaca da ke Cyprus, inda jiragen Burtaniya ke sauka bayan sun taso daga Sudan gabanin su karasa kasarsu.

Ba a amince mata ta tafi da yaran ba saboda dokokin da Burtaniyan ta shimfida na kwaso mutanen.

“Ala dole, na mika su ga mahaifinsu. Wani mummunan lokaci ne da ba zan manta da shi ba,” in ji ta.

‘‘Kananan yara ne da ba su da kariya, kamata ya yi a ce an bari ni na taho da su cikin jirgi.
‘‘Sun shaida min cewa ba zan iya dauko su ba saboda ka’idar da aka sanya, sai mai fasfo din Burtaniya ne kawai za a dauka.
Na roke su na ce ‘ya’yana ne, amma suka ce hakan ba zai yiwu ba.”

Fadar mulki ta Downing Street ta zayyana wasu sharudda wadanda ta ce ba za a sauya su ba, amma an bai wa jami’an da ke Sudan, wuka da nama game da yanke shawara kan abin da suke gani ya fi zama daidai bisa la’akari da abin da ke faruwa zahiri a Sudan.
Ofishin wajen Burtaniya ya ce jirage takwas da suka tashi sun kwaso mutum 897 daga kasar wadda ke gabashin Afrika zuwa Cyprus a ranar Alhamis.

Amma duk da haka wannan wani adadi ne da bai taka kara ya karya ba bisa la’akari da yawan ‘yan Burtaniya da ke Sudan.

Waafa Salim wadda ma’aikaciyar tsare-tsare ce a wani ofis a Buckinghamshire, ta je Arewacin Sudan ne, inda ta ce mutane na samun tallafi daga Kungiyar Ba Da Agajin ta Red Cross.

Ta je Sudan ne da danta Hasan mai shekara 12, wata ziyara da ta kai wa ‘yan uwanta a lokacin Sallah karama.
Ya kamata a ce sun koma Burtaniya a makon jiya, amma yakin da aka fara ya haifar musu da tsaiko.

Ana Ganin Abubuwan Firgici Da Tashin Hankali
Ta samu damar tsallake shingen duba ababen hawa da yawa da danta ga kuma dan’uwanta, tare da ‘ya’yansa da ke tsakanin shekara 3 -10.

Sai dai, bayan ta tattauna da jami’an Burtaniya ne sai aka mayar da dan’uwanta da ‘ya’yan nasa.

“A dokar da suka bayar sun ce ‘ya’yan cikinmu kawai za mu iya fita da su,” in ji ta.
“Wadannan yaran da ba su san komai ba, ku bar su tare da ni. Shi dan’uwana ya zauna, amma suka ki.”

Ta ce yanzu dan’uwan nata da iyalansa na kokarin barin Sudan ta kan iyakar Masar, ta kara da cewa da babu yara da tafiyar ta fiye masa sauki.

A yanzu haka, duk wani mai fasfo din Birtaniya da iyalansa ko kuma mai shaidar zama a kasar zai iya samun damar a dauke shi.

Da yake magana tun da farko, sakataren wajen Burtaniya James Cleberly ya ce kada a bar duk dan Sudan din da ba shi da takardun zama a Burtaniya ya wuce shingen tantance mutane.

“Lokacin da aka samu dan Burtaniya na auren ‘yar Sudan kuma suna da ‘ya’ya, sai mu rasa yadda za mu yi,” in ji shi.

“Ya shawarci ‘yan Burtaniya su gaggauta tattara nasu ya nasu su fice daga Sudan domin ba a san me zai faru ba, idan lokacin yarjejeniyar tsagaita wuta ya kare.

Jami’ai a Burtaniya suna ci gaba da tuntubar bangarorin biyu da ke gaba da juna, a kan su daure su tsawaita wannan yarjejeniya ta tsagaita wuta tsakaninsu.

Da yake magana a gaban majalisa, sakataren waje na jam’iyyar adawa, Dabid Lammy ya yi kira ga gwamnati ta bari a kwashe ‘yan Sudan masu shaidar zama a Burtaniya.
A tare da Waafa Salim akwai danta mai shekara 12 Hasan, wanda ya rika fama da karancin barci a makon jiya saboda tashin bam da karar harbe-harben bindiga.
Ta ce abin takaici ne ka bar ‘yan’uwanka, cikin wannan matsala.

An shaida wa BBC cewa sai da aka kai Waafa Salim asibiti saboda rashin lafiya da ta kama ta a cikin jirgin sama.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

GORON JUMA’A

Next Post

Da Dumi-Dumi: An Yanke Wa Ekweremadu Hukuncin Daurin Shekara 10 A Birtaniya

Related

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari
Rahotonni

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

7 hours ago
Dambarwar 2027 Da Kalubalen Da Ke Gaban Jam’iyyun Siyasa
Rahotonni

Dambarwar 2027 Da Kalubalen Da Ke Gaban Jam’iyyun Siyasa

7 days ago
Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya
Rahotonni

Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

1 week ago
Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda
Rahotonni

Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda

1 week ago
Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
Rahotonni

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

4 weeks ago
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

4 weeks ago
Next Post
Da Dumi-Dumi: An Yanke Wa Ekweremadu Hukuncin Daurin Shekara 10 A Birtaniya

Da Dumi-Dumi: An Yanke Wa Ekweremadu Hukuncin Daurin Shekara 10 A Birtaniya

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

August 23, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

August 23, 2025
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

August 23, 2025
2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

August 23, 2025
Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.