Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Sabbin Shugabannin Majalisa: APC Na Da Goyon Bayan Kashi 90% Na ’Yan Majalisa – Doguwa

by
3 years ago
in RIGAR 'YANCI
1 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Gagarabadon Majalisar Wakilai ta Kasa, Hon. Alhasan Ado Doguwa, ya yi bugun kirjin cewa, jam’iyyar APC mai mulkin Najeriya, APC, ta na da goyon bayan kashi 90 cikin 100 na yawan ’yan majalisarta kan batun zaben sababbin shugabannin majalisar.

Diguwa ya bayyana haka ne a lokacin da ya kai ziyara sabuwar Masarautar Rano, domin yin mubayi’a ga sabon sarkin da a ka nada. A yayin da ya ke jawabi ga manema labarai, dan majalisar wakilan ya ce, dangane da sa-toka-sa-katsi da a ke yi a majalisar wakilai da ta dattawa kan zaben shugabannin majalisun guda biyu, su sama da kashi 90 cikin 100 sun amince da manufar jam’iyarsu ta APC da Shugaban Kasa Muhammadu Buhari da a zabi Hon. Femi Gbajabiamila, wanda ya fito daga jihar Lagos, don dai a samu daidaito da hada kan ’yan Najeriya wajen tafiyar da mulkin Najeriya, musamman idan a ka yi da la’akari da irin rawar da Yarabawa su ka taka a zaben APC da Buhari a 2015 da 2019.

Haka kuma sun amince da mataimakinsa ya fito daga yankin Arewa ta Tsakiya mai jihohin Nassarawa, Plateau, Benue, Niger, da Kogi kan dai wannan manufa ta APC da shugabanninta, don kauce wa matsalolin da a ka samu a shugabancin da ya gabata a majalisar.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Jihar Zamfara Ta Tabbatar Da Kama  Wasu Sojoji Masu Hulda Da ‘Yan Ta’adda

Kansila Mai Mataimaka 18 Ya Sadaukar Da Albashinsa Na Farko

Haka kuma sun amince da zaben Sanata Ahmad Lawan daga jihar Yobe a matsayin shugaban Majalisar Dattawa daidai da waccan manufar ta APC.

Sai kuma shugaban Masu Rinjaye na Majalisar Wakilai da a ka ba Kano da Jigawa su fito da shi a majalisar wakilai, ’yan Jigawa sun yarda sun bar wa shi Hon. Doguwa.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Sanata Gumau Ya Raba Buhun Shinkafa 710 Ga Masu Azumi A Mazabarsa

Next Post

Masu Nadin Sarkin Kano Sun Gayyato Lauyoyi Masu Daraja Ta Daya Don Kalubalantar Ganduje

Labarai Masu Nasaba

Zamfara

Gwamnatin Jihar Zamfara Ta Tabbatar Da Kama  Wasu Sojoji Masu Hulda Da ‘Yan Ta’adda

by
1 year ago
0

...

Kansila Mai Mataimaka 18 Ya Sadaukar Da Albashinsa Na Farko

by
1 year ago
0

...

APC

Sanata Al-Makura Ya Cancanci Rike Kujerar Shugabancin APC, Inji Gwamna Sule

by
1 year ago
0

...

Kebbi

Bagudu Ya Bukaci ’Yan Nijeriya Su Zama Masu Kishin Kasa A Shafukan Sada Zumunta

by
1 year ago
0

...

Next Post

Masu Nadin Sarkin Kano Sun Gayyato Lauyoyi Masu Daraja Ta Daya Don Kalubalantar Ganduje

Leave Comment

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: