• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabon Albishir Ga Masu Kawo Ziyara Ko Yada Zango A Birnin Beijing Na Kasar Sin

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Sabon Albishir Ga Masu Kawo Ziyara Ko Yada Zango A Birnin Beijing Na Kasar Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Biranen kasar Sin na gudanar da gyare-gyare na ci gaban zamani a bangaren kyautata jin dadin baki masu kawo ziyara ko kuma yada zango. Inda hakan ke haifar da kyakkyawan sakamako daga irin tsokacin da baki ke yi kan sabbin tsare-tsaren da suka gani a biranen.

Wasu ‘yan uwa su biyu daga Poland da suka kawo ziyarar kwanaki hudu a birnin Beijing kwanan baya, sun bayyana cewa, kasar Sin ta burge su sosai, bisa yadda suka ga an ci gaba da raya manyan biranen kasar tare da saukaka mu’amalar biyan bukatun masu yawon bude ido na kasashen waje.

  • Kasar Sin Ta Mallaki Tashoshin Sadarwar 5G Miliyan 4.25
  • Borrusia Dortmund Ta Sallami Kocinta, Nuri Sahin

Dagmara Paszkowska, wacce ta ziyarci kasar Sin tare da dan uwanta Norbert ta ce, “Mun lura za mu iya biyan kudin hidindimu ko abubuwan da muka saya ta hanyar amfani da tsabar kudi, ko kati, ko kuma ta hanyar tambarin QR, kana mun yi mamakin cewa ana ma iya amfani da hanyar tantance fuska wajen biyan kudi.”

A wani bangare na sabon tsarin biyan kudi da tafiye-tafiye da aka kaddamar a ranar 1 ga Janairun nan don saukaka mu’amaloli ga baki, an samar da wuraren tuntuba don neman biyan bukata ta kusurwowin da bakin za su yi kacibis da su da zarar sun iso manyan filayen jiragen sama guda biyu na Beijing, wato na Beijing Capital da na Beijing Daxing.

Kaddamar da wadannan wurare da birnin Beijing ya yi a manyan tasoshinsa na jiragen sama ta zo a kan gaba, a daidai da lokacin da ake samun karuwar baki daga kasashen waje sakamakon fadada manufofin kasar Sin na shigowa ba tare da biza ba ga matafiya daga kasashe 54, da kuma damar shiga kai-tsaye ga baki masu fasfo daga kasashe 38 da ke bukatar gajeren zama a kasar.

Labarai Masu Nasaba

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

A halin yanzu, kusan a kullum, ana samun baki ‘yan kasashen waje 252 de ke shiga birnin Beijing tare da takardar izinin shiga ta wucin-gadi ta sa’o’i 240 wacce aka kara mata wa’adi daga sa’o’i 144, kamar yadda mataimakin shugaban sashen musayar waje da hadin gwiwa na ofishin al’adu da yawon bude ido na birnin Beijing, Wang Hongyan, ya tabbatar a wani taron manema labarai.

A shekarar 2024, birnin Beijing ya sami ziyarce-ziyarce miliyan 3.94, wadanda suka karu da kashi 186.8 cikin dari a mizanin shekara-shekara, inda hakan ya kara yawan kudin shiga na yawon bude ido na birnin da kashi 151.7 cikin dari, watau zuwa dala biliyan 4.91, kuma mahukuntan da abin ya shafa sun lashi takobin kara kyautata jin dadin baki masu ziyara ta hanyar inganta tsare-tsaren yawon bude ido, masaukai da sayayya da hanyoyin biyan kudi masu gamsarwa.

Tsarin amfani da katin komai-da-ruwanka na “Beijing Pass” na daga cikin abubuwan da ke saukaka mu’amalar baki a birnin ta yadda wadanda suka saye shi ba kawai za su iya amfani da shi wajen biyan kudin sufuri a cikin birane 300 na kasar Sin ba ne, har ma za su iya shiga wasu kebabbun wuraren kasuwanci, da cibiyoyin tarihi da al’adu da yawon bude ido. An bayar da wannan kati a kalla 39,000 ga baki masu ziyara daga lokacin da aka kaddamar da shi a watan Yulin bara.

Haka nan, domin bai wa baki damar sanin tarihi da al’adun Sinawa a Beijing, a ranar 27 ga Disamban da ya gabata, birnin ya yi sabon albishir ta hanyar kaddamar da tsarin kai bakin da suka yada zango a cikinsa ziyara ta rabin yini a wasu muhimman wurare kyauta. Ana gudanar da wannan tsari sau biyu a yini, da safe da kuma maraice.

Sauran biranen kasar Sin kamar Shanghai su ma suna ci gaba da janyo hankulan dubban masu kawo ziyara saboda manufar shigowa ba tare da biza ba. A watannin baya-bayan nan, alal misali, ana samun karuwar maziyartan Koriya ta Kudu dake tururuwa zuwa birnin Shanghai. (Abdulrazaq Yahuza Jere)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jagoranci Nagari: Kungiyar Lauyoyi Ta Karrama Gwamnan Zamfara Da Lambar Yabo

Next Post

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Babu Wanda Zai Ci Nasara A Yakin Cinikayya Ko Yakin Harajin Kwastam

Related

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

9 minutes ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

30 minutes ago
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

17 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

17 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

19 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

22 hours ago
Next Post
Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Babu Wanda Zai Ci Nasara A Yakin Cinikayya Ko Yakin Harajin Kwastam

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Babu Wanda Zai Ci Nasara A Yakin Cinikayya Ko Yakin Harajin Kwastam

LABARAI MASU NASABA

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Sin

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.