• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabon Albishir Ga Masu Kawo Ziyara Ko Yada Zango A Birnin Beijing Na Kasar Sin

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Sabon Albishir Ga Masu Kawo Ziyara Ko Yada Zango A Birnin Beijing Na Kasar Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Biranen kasar Sin na gudanar da gyare-gyare na ci gaban zamani a bangaren kyautata jin dadin baki masu kawo ziyara ko kuma yada zango. Inda hakan ke haifar da kyakkyawan sakamako daga irin tsokacin da baki ke yi kan sabbin tsare-tsaren da suka gani a biranen.

Wasu ‘yan uwa su biyu daga Poland da suka kawo ziyarar kwanaki hudu a birnin Beijing kwanan baya, sun bayyana cewa, kasar Sin ta burge su sosai, bisa yadda suka ga an ci gaba da raya manyan biranen kasar tare da saukaka mu’amalar biyan bukatun masu yawon bude ido na kasashen waje.

  • Kasar Sin Ta Mallaki Tashoshin Sadarwar 5G Miliyan 4.25
  • Borrusia Dortmund Ta Sallami Kocinta, Nuri Sahin

Dagmara Paszkowska, wacce ta ziyarci kasar Sin tare da dan uwanta Norbert ta ce, “Mun lura za mu iya biyan kudin hidindimu ko abubuwan da muka saya ta hanyar amfani da tsabar kudi, ko kati, ko kuma ta hanyar tambarin QR, kana mun yi mamakin cewa ana ma iya amfani da hanyar tantance fuska wajen biyan kudi.”

A wani bangare na sabon tsarin biyan kudi da tafiye-tafiye da aka kaddamar a ranar 1 ga Janairun nan don saukaka mu’amaloli ga baki, an samar da wuraren tuntuba don neman biyan bukata ta kusurwowin da bakin za su yi kacibis da su da zarar sun iso manyan filayen jiragen sama guda biyu na Beijing, wato na Beijing Capital da na Beijing Daxing.

Kaddamar da wadannan wurare da birnin Beijing ya yi a manyan tasoshinsa na jiragen sama ta zo a kan gaba, a daidai da lokacin da ake samun karuwar baki daga kasashen waje sakamakon fadada manufofin kasar Sin na shigowa ba tare da biza ba ga matafiya daga kasashe 54, da kuma damar shiga kai-tsaye ga baki masu fasfo daga kasashe 38 da ke bukatar gajeren zama a kasar.

Labarai Masu Nasaba

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

A halin yanzu, kusan a kullum, ana samun baki ‘yan kasashen waje 252 de ke shiga birnin Beijing tare da takardar izinin shiga ta wucin-gadi ta sa’o’i 240 wacce aka kara mata wa’adi daga sa’o’i 144, kamar yadda mataimakin shugaban sashen musayar waje da hadin gwiwa na ofishin al’adu da yawon bude ido na birnin Beijing, Wang Hongyan, ya tabbatar a wani taron manema labarai.

A shekarar 2024, birnin Beijing ya sami ziyarce-ziyarce miliyan 3.94, wadanda suka karu da kashi 186.8 cikin dari a mizanin shekara-shekara, inda hakan ya kara yawan kudin shiga na yawon bude ido na birnin da kashi 151.7 cikin dari, watau zuwa dala biliyan 4.91, kuma mahukuntan da abin ya shafa sun lashi takobin kara kyautata jin dadin baki masu ziyara ta hanyar inganta tsare-tsaren yawon bude ido, masaukai da sayayya da hanyoyin biyan kudi masu gamsarwa.

Tsarin amfani da katin komai-da-ruwanka na “Beijing Pass” na daga cikin abubuwan da ke saukaka mu’amalar baki a birnin ta yadda wadanda suka saye shi ba kawai za su iya amfani da shi wajen biyan kudin sufuri a cikin birane 300 na kasar Sin ba ne, har ma za su iya shiga wasu kebabbun wuraren kasuwanci, da cibiyoyin tarihi da al’adu da yawon bude ido. An bayar da wannan kati a kalla 39,000 ga baki masu ziyara daga lokacin da aka kaddamar da shi a watan Yulin bara.

Haka nan, domin bai wa baki damar sanin tarihi da al’adun Sinawa a Beijing, a ranar 27 ga Disamban da ya gabata, birnin ya yi sabon albishir ta hanyar kaddamar da tsarin kai bakin da suka yada zango a cikinsa ziyara ta rabin yini a wasu muhimman wurare kyauta. Ana gudanar da wannan tsari sau biyu a yini, da safe da kuma maraice.

Sauran biranen kasar Sin kamar Shanghai su ma suna ci gaba da janyo hankulan dubban masu kawo ziyara saboda manufar shigowa ba tare da biza ba. A watannin baya-bayan nan, alal misali, ana samun karuwar maziyartan Koriya ta Kudu dake tururuwa zuwa birnin Shanghai. (Abdulrazaq Yahuza Jere)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jagoranci Nagari: Kungiyar Lauyoyi Ta Karrama Gwamnan Zamfara Da Lambar Yabo

Next Post

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Babu Wanda Zai Ci Nasara A Yakin Cinikayya Ko Yakin Harajin Kwastam

Related

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO
Daga Birnin Sin

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

31 minutes ago
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles
Daga Birnin Sin

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

2 hours ago
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

3 hours ago
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

4 hours ago
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

23 hours ago
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

24 hours ago
Next Post
Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Babu Wanda Zai Ci Nasara A Yakin Cinikayya Ko Yakin Harajin Kwastam

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Babu Wanda Zai Ci Nasara A Yakin Cinikayya Ko Yakin Harajin Kwastam

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

August 23, 2025
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

August 23, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.