Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Sadarwa Na Da Matukar Mahimmanci Wajen Farfado Da Tattalin Arzikin Nijeriya – Danbatta

by
1 year ago
in TATTALIN ARZIKI
1 min read
danbatta
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Shugaban hukumar kulawa da harkokin sadarwa a Nijeriya (NCC), Farfesa Umar Danbatta ya bayyana cewa, harkokin sadarwa yana da matukar mahimmanci wajen farfado da tattalin arzikin kasar nan. Farfesa Danbatta ya bayayana hakan ne lokacin da yake gabatar da jawabi a wajen wani taro da ya gudana a kwalejin tsaro ta kasa.

Ya ce, “kamfanonin sadarwa da ke karkashin kulawar hukumar NCC suna taka mahimmiyar yawa wajen bunkasa tattalin arzikin zamani. Bangaren sadarwa yana matukar samar wa gwamnatin tarayya kudaden shiga.”

Ya kara da cewa, bangaren yana taka rawa guda biyu wadanda suka hada da samar da kudaden shiga da kuma bayar da dama ga sauran bangarorin tattalin arziki.

Labarai Masu Nasaba

Akwai Isassun Kudade Ga Masu Kasuwanci, Cewar CBN

Gwamnatin Nijeriya Ta Samu Rancen Dala Biliyan 2.5 Don Aikin Jirgin Kasa Na Legas-Ibadan

“Fannin sadarwa yana da matukar mahimmanci wajen farfado da tattalin arzikin Nijeriya, inda bangaren yake samar da haraji mai yawan gaske da kuma bai wa sauran bangararorin tattalin arziki daman samun kudaden.

Ya ci gaba da cewa, bangaren sadarwa ya samu nasarar zuba kudaden haraji wadanda suka kai na naira biliyan 362.34 a asusun gwamnatin tarayya a cikin shekara biyar. Ya ce, bangaren sadarwa yana rage tazara na ababan more rayuwa wanda yake saukaka samun abubuwa cikin sauki, wanda ko mutane suka zaune a cikin gidajen su za su iya sayan katin wutar lantarki, sannan sashin ya yi kokarin magance duk irin matsalolin da ya fuskanta a baya.

A nasa bangaren, shugaban kwalejin tsaro da kasa, Rear Admiral Mackson Kadiri ya yaba wa jawabin shugaban hukumar NCC, bisa yadda ya dauki tsawon lokacin yana gudanar da jawabai masu daukan hankali da kuma rawar da fannin sadarwa ke takawa a cikin bangaren bunkasa kasa.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Gaskiyar Dalilan Buhari Na Bude Wasu Daga Cikin Iyakokin Nijeriya

Next Post

Majalisar Wakilai Ta Kara Sama Da Naira Biliyan 500 A Kasafin 2021

Labarai Masu Nasaba

Kudade

Akwai Isassun Kudade Ga Masu Kasuwanci, Cewar CBN

by
1 year ago
0

...

Gwamnatin Nijeriya Ta Samu Rancen Dala Biliyan 2.5 Don Aikin Jirgin Kasa Na Legas-Ibadan

Gwamnatin Nijeriya Ta Samu Rancen Dala Biliyan 2.5 Don Aikin Jirgin Kasa Na Legas-Ibadan

by
1 year ago
0

...

Hukumar EFCC Ta Gargadi Masu Amfani Da Na’urar ‘POS’ Kan Gurbatacciyar Hada-hada

Hukumar EFCC Ta Gargadi Masu Amfani Da Na’urar ‘POS’ Kan Gurbatacciyar Hada-hada

by
1 year ago
0

...

Karamin Albashi

Shugaba Buhari Ya Bayyana Iskar Gas A Matsayin Hanyar Cigaban Tattalin Arziki

by
1 year ago
0

...

Next Post
Majalisar Wakilai

Majalisar Wakilai Ta Kara Sama Da Naira Biliyan 500 A Kasafin 2021

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: