ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Safarar Mata Zuwa Kasashen Larabawa Da Turai Ya Zama Ruwan Dare -MDD

by Rabi'u Ali Indabawa
4 years ago
Mata

Kimanin mutane 666 daga cikin wadanda suka fada tarkon masu safarar bil ‘adama ne aka ajiye a cibiyar OIM mai kula da ‘yan cirani dake Zinder daga shekarar 2017 zuwa 2021 a cewar rahoton hukumar ta IOM wanne ya kara da cewa kashi 69 daga cikinsu mata ne da ‘yan mata.

Wani rahoton hukumar Majalisar Dinkin Duniya (MDD) mai kula da hijirar jama’a wato IOM ya gano cewa galibin mutanen da ke shiga hannun masu safarar mutane a kan hanyoyin dake ratsa Jamhuriyar Nijer zuwa kasashen Larabawa da na yammacin duniya mata ne da ‘yan mata suke shiga tashin hankali.

  • Sabon Layin Dogo Da Ya Zagaye Hamada Mafi Girma A Kasar Sin Ya Fara Aiki

Wadanan mutane an yi masu rajista ne a Zinder da Agadez da Arlit da Dirkou da birnin Yamai abin da ke nunin yadda fataucin mutane ke neman zama ruwan dare a wannan kasa duk da matakan da mahukunta ke dauka.

ADVERTISEMENT

Daliba a wata makarantar ilimin kimiyar Kwamfuta, Shamsiya Sabo na mai alakanta wannan al’amari da wasu tarin dalilai.

Rahoton ya ambato wakiliyar hukumar OIM a Nijer Barbara Rijks ta na cewa kyakkyawar fahimtar da ake samu a ayyukan hadin guiwar dake tsakaninsu da hukumomin kasar ta taimaka sosai wajen gudanar da wannan bincike da zai ba da damar tallafa wa wadanan mutane. Shugabar Kungiyar Kare Hakkin Mata ta APAISE Hadjia Rabi Djibo Magaji na da irin wannan ra’ayi.

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

Haka kuma an gano cewa kashi 56 daga cikin 100 na wadanan mutane ‘yan Nijeriya ne dake neman ratsa Nijer don zuwa kasashen Yammaci yayin da kashi 23 daga cikinsu ‘yan Nijer ne sannan sauran kan fitowa ne daga kasashen yankin Kudu da sahara.

Wani mai rajin kare hakkin jama’a Dambaji Son Allah mamba ne a kwamitin hadin gwiwar hukumomi da kungiyoyi masu zaman kansu CNLTP mai yaki da fataucin mutane.

Kashi 38 daga cikin 100 na wadanda da aka ajiye a cibiyoyin kula da bakin haure mutane ne da aka saka cikin harkar kasruwanci ko kuma ake kokarin shigar da su cikin wannan harka yayin da kashi 21 daga cikinsu ana ci da guminsu ta hanyar aikatau da wasu sauran ayyukan karfi sai kashi 23 na rukunin wadanda aka tilastawa shiga sana’ar bara a cewar hukumar OIM.

Mata
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

Rikicin APC A Katsina: Idan Ba A Dauki Mataki Ba, Jam'iyyar Na Iya Zubar Da Ciki A 2023

LABARAI MASU NASABA

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.