• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sai A Hankali Zan Gyara Chelsea, Frank Lampard

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Lampard

Sabon mai koyar da ‘yan wasan kungiyar kwallon kafa ta Frank Lampard ya ce baya jin za’a magance matsalar Chelsea a rana daya, bayan da ya fara da kafar hagu a Wolberhampton.

Lampard wanda ya ja ragamar Chelsea a karon farko a matakin rikon kwarya, ya yi rashin nasara 1-0 a gidan Wolbes a wasan mako na 30 a Premier ranar Asabar a filin wasa na Moulined.

  • Wang Yi Da Qin Gang Sun Gana Da Ministar Harkokin Wajen Jamus 
  • Kin Amincewa Da Kwangilar Dala Miliyan 22 Ta Yi Sanadiyyar Sauke Ni Daga Shugabancin NPA –Hajiya Hadiza Bala-Usman

Wasan farko da ya shugabancin Chelsea tun bayan watanni 27 da aka kore shi a Stamford Bridge, Thomas Tuchel ya maye gurbinsa wanda shi ma daga baya aka kore shi.

Chelsea ta kasa zura kwallo a raga a wasanni uku a jere kenan, karo na 11 da aka doke ta a babbar gasar firimiyar Ingila ta kakar nan wanda hakan ba karamin ci baya bane ga kungiyar.

”Mun kwana da sani ba ma yanayi mai kyau, ba wanda muke bukata bane, amma da akwai dalilin hakan ban jin zan warware matsalar nan a kwana daya, dole sai mun kara kwazo a wasa da sa kaimi.” In ji Lampard.

LABARAI MASU NASABA

Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Wasa hudu kenan da Chelsea ba ta yi nasara ba, wadda a ranar Laraba ta je gidan Real Madrid, domin buga Champions League kuma a sati mai zuwa kungiyoyin za su sake karawa a filin wasa na Stamford Bridge.

Lampard, wanda bai da kungiya tun bayan da Eberton ta sallame shi a watan Janairun 2023, ya horar da Chelsea daga watan Yulin 2019 zuwa Janairun 2021 daga nan ta kore shi.

An nada shi kociyan rikon kwarya zuwa karshen kakar nan a makon nan, bayan da Chelsea ta kori Graham Potter a karshen watan daya gabata, wanda ya yi watanni bakwai kacal yana koyar da kungiyar.

Tun farko Chelsea ta sa Potter ya yi murabus daga aikin Brighton, sannan ta kulla yarjejeniyar shekara biyar da shi saboda rashin tabuka abin arziki ya sa kungiyar ta sallame shi.

Lampard ya buga wa Chelsea wasa a Stamford Bridge lokacin da Roberto di Matteo ya ja ragamar kungiyar ta lashe Champions League a 2012 a matakin rikon kwarya daga baya aka bashi jan ragama.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax
Wasanni

Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

November 6, 2025
Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba
Wasanni

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025
Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara
Wasanni

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

November 2, 2025
Next Post
PDP Ta Bukaci A Kama Kwamishinan Zaben Jihar Adamawa

PDP Ta Bukaci A Kama Kwamishinan Zaben Jihar Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura

November 7, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

November 7, 2025
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

November 7, 2025
Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

November 7, 2025
Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)

Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)

November 7, 2025
Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

November 7, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Hanyoyin Noma Na Gargajiya Ba Za Su Iya Wadata Abinci A Nijeriya Ba -Masanin Kimiyya

November 7, 2025
An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

November 7, 2025
Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.