• English
  • Business News
Saturday, October 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sake Fasalin Naira Ya Taimaka Wajen Samun  Ingantaccen Zabe A 2023 —Buhari Ya Jaddada

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Naira

Tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya bayyana cewa sauya fasalin naira ya yi matukar taimaka wa wajen samar da ingataccen zabe a 2023.

Ya kuma bayyana dalilin da ya sa bai kori tsohon gwamnan babban bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele duk da an alakanta shi da neman tikitin takarar shugaban kasa a APC a 2023.

  • Jihar Kaduna Za Ta Ƙarfafa Ƙawancen Tattalin Arziki Da Ƙasar Jamus
  • Sin Ta Riga Ta Bayar Da Gudunmawar Da Ake Bukata Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

A cewarsa, ba zai iya korar Emefiele daga ofis ba saboda bai fada masa burinsa ba na neman shugaban Nijeriya ba.

Buhari ya bayyana hakan ne a wurin kaddamar da littafin ayyukan da ya yi tun daga 2015 zuwa 2023, wanda tsohon mai magana da yawunsa, Femi Adesina ya rubuta.

An dai kaddamar da littafin ne a hukumance a Abuja ranar Talata, Buhari ya kare manufar sake fasalin naira da Emefiele ya aiwatar, inda ya tabbatar da cewa ta taimaka wajen samar da ingantaccen zabe a 2023.

LABARAI MASU NASABA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

Tsohon shugaban kasar ya ci gaba da cewa wadanda ke da matsala da manufar sake fasalin naira mutane ne da ke da kudade masu yawa.

Buhari ya ce, “Ba da gangan muka sauya fasanin naira ba da kuma samun karancin kudade da aka yi domin hukunta ‘yan Nijeriya ba. Dimokuradiyya tana ba mutane damar bayyana ra’ayinsu, kuma ba mu yi kokarin hana su ba. Mutane sun fahimci illar bin ra’ayinsu a zaben, kuma ba mu tilasta musu ba.

“Jihata ta Katsina an samu kyakkyawan tsari. A zaben shugaban kasa, APC ta sha kaye. Amma ta samu nasara a zaben gwamna. Watakila sun yi sakaci ne saboda suna tunanin ita ce jihata, kuma suna tunanin za su yi nasara cikin sauki. Mutane ba sa son a yi sakaci wajen gudanar da zabe domin haka zai sa a sha mamaki.

“Na sami Emefiele a ofis a lokacin da na zo a matsayin shugaban kasa, ban samu wasu kwararan hujjoji a kansa da sa in sallame shi daga matsayinsa na gwamnan CBN.

“Idan ka azabtar da mutum bisa zalunci, ba zai iya mantawa ba har tsawon rayuwarsa, don haka idan za ka hukunta mutum, dole ne ka sami kwararen hujjoji. Kuma ya kamata ka sani cewa ba za ka tabbtar a mukami ba har abada. Dole ne wata rana sai ka bar wannan mukamin da kake.

“Lokacin da aka alakanta shi da neman takaran shugaban kasa a 2023, ban tambaye shi ba, saboda bai fada wa kowa ba cewa yana da muradin zama shugaban kasa. In ba haka ba, da na cire shi tare da yi wa al’umma bayanin dalilin da ya sa.

“Babu shakka manufar sake fasalin naira ta ba mu zabuka mai matukar tsafta. Mutanen da ke da makudan kudade ne suka sami matsala da tsarin,” in ji Buhari.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Next Post
Ziyarar Ministan Wajen Sin A Afirka: Zumunci Mai Dadi Ba Irin Na ’Yan Ta-more Ba

Ziyarar Ministan Wajen Sin A Afirka: Zumunci Mai Dadi Ba Irin Na ’Yan Ta-more Ba

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

October 24, 2025
Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

October 24, 2025
An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 24, 2025

Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci

October 24, 2025
Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

October 24, 2025
Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

October 24, 2025
An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

October 24, 2025
Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

October 24, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

Gwamnan Bauchi Ya Naɗa Yayansa A Matsayin Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.