• English
  • Business News
Wednesday, August 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Samar Da Ci Gaba A Bangaren Ma’adinai: Ministan Yaɗa Labarai Ya Yaba Da Koƙarin Takwaransa Na Ma’adinai

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Samar Da Ci Gaba A Bangaren Ma’adinai: Ministan Yaɗa Labarai Ya Yaba Da Koƙarin Takwaransa Na Ma’adinai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yaba wa takwaransa na Ma’adinai kan abin da ya kira “manyan matakan cigaba da ake samu a Ma’aikatar Ma’adinai da ake ɗauka don kawo sauyi a bangaren a matsayinsa na wanda ke sahun gaba na muradun tattalin arzikin Nijeriya.”

A cikin wata sanarwa da mataimaki na musamman ga ministan kan harkokin yaɗa labarai, Malam Rabi’u Ibrahim, ya fitar ta ce,  Idris ya faɗi haka ne a lokacin da ya kai ziyarar aiki ga Ministan Ma’adinai, Mista Henry Dele Alake, a ranar Alhamis a Abuja.

  • Bayan Hukuncin Kotun Ɗaukaka Ƙara, Gwamna Uba Sani Ya Nemi Haɗa Hannu Da ‘Yan Adawa
  • NPA Ta Gargadi Masu Jibge Kwantaina Ba Bisa Ka’ida Ba

Ministan ya yi la’akari cikin gamsuwa da cewa ayyuka masu tasiri a fagen ma’adinai waɗanda ke bada sakamako a kyakkyawan sauye-sauye da ake matuƙar buƙatar su da canza muradu, wanda ya yi daidai da manyan manufofin Renewed Hope Agenda ta gwamnatin Tinubu.

A cewar Idris, Mista Alake ya na dasa ginshiƙan gudanarwa waɗanda ba a saba ganin irin su ba a sashen ma’adinai sannan su na haifar da kyakkyawar fata a zuciyar ‘yan Nijeriya game da gina ƙasa mai ƙarfin tattalin arziki.

Ya bayyana ziyarar tasa ga Alake a matsayin ziyarar aiki ta farko da ya kai wa wani takwaran sa minista, ya na faɗin cewa Alake mutum ne wanda ya samu sani daga sassa daban-daban, kuma mai basirar cimma nasara a wani sashe da ya kusa durƙushewa, wanda zai ƙarfafa hanyoyin kuɗin shiga na Nijeriya ya kuma faɗaɗa damar ɗaukar ma’aikata.

Labarai Masu Nasaba

Uwargidar Gwamnan Katsina Ta Nemi A Taimaka Wa Mata Wajen Yaƙi Da Ciwon Nono Da Na Mahaifa

Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa

Shi kuma Mista Alake sai ya ce shi da Idris sun daɗe su na hulɗar siyasa tare, kuma Idris mutum ne wanda ya yi amanna da ƙudirorin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu, musamman wajen abin da ya dace da tattalin arziki da zamantakewar Nijeriya baki ɗaya, ta hanyar Renewed Hope Agenda.

Ya ce: “Idris da ni abokai ne kuma wannan ziyarar ta na alamta burin mu na ciyar da ƙasar nan gaba domin ta zama mai faɗaɗan hanyoyin tattalin arziki kuma mu jawo hankalin duniya zuwa ga sashen ma’adinai a matsayin hanyar jawo wa Nijeriya Jari Kai-tsaye daga Waje, wato ‘Foreign Direct Investment’ (FDI).”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hakar Ma'adinaiMinistan yada labarai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasashen Da Ke Kwashe Likitocin Nijeriya Za Su Fara Biyan Diyya – Ministan Lafiya

Next Post

Labarin Ƙarya: Babu Inda Gwamna Dauda Lawal Ya Kashe Naira Miliyan 400 Don Tafiye-tafiye

Related

Uwargidar Gwamnan Katsina Ta Nemi A Taimaka Wa Mata Wajen Yaƙi Da Ciwon Nono Da Na Mahaifa
Labarai

Uwargidar Gwamnan Katsina Ta Nemi A Taimaka Wa Mata Wajen Yaƙi Da Ciwon Nono Da Na Mahaifa

2 hours ago
Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa
Labarai

Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa

4 hours ago
Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

5 hours ago
Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82
Manyan Labarai

Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

6 hours ago
Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn
Labarai

Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

8 hours ago
Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima

9 hours ago
Next Post
Labarin Ƙarya: Babu Inda Gwamna Dauda Lawal Ya Kashe Naira Miliyan 400 Don Tafiye-tafiye

Labarin Ƙarya: Babu Inda Gwamna Dauda Lawal Ya Kashe Naira Miliyan 400 Don Tafiye-tafiye

LABARAI MASU NASABA

Uwargidar Gwamnan Katsina Ta Nemi A Taimaka Wa Mata Wajen Yaƙi Da Ciwon Nono Da Na Mahaifa

Uwargidar Gwamnan Katsina Ta Nemi A Taimaka Wa Mata Wajen Yaƙi Da Ciwon Nono Da Na Mahaifa

August 6, 2025
Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa

Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa

August 6, 2025
Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

August 6, 2025
Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

August 6, 2025
Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

August 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima

Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima

August 6, 2025
Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

August 6, 2025
Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

August 5, 2025
Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

August 5, 2025
Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

August 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.