• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sanata Yari Ya Samar Da Taki Ga Manoman Zamfara A Kan Naira 20,000

by Sadiq
1 year ago
Yari

Tsohon gwamnan Jihar Zamfara, Sanata Abdulaziz Yari, ya samar da manyan motocin takin zamani 76 da za a raba su ga manoma tare sa zaftare kashi 50 cikin 100 na farashinsa a matsayin tallafi. 

Ibrahim Muhammad, shugaban kwamitin yada labaransa ne, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya aike wa manema labarai a Gusau ranar Talata.

  • Neja: An Ceto Mutane 7 Da Suka Makale Wajen Hakar Ma’adanai
  • Gwamna Dauda Lawal Ya Jaddada Ƙudirinsa Na Tsaron Rayukan Al’ummar Zamfara

A cewar sanarwar, shugaban kwamitin, Alhaji Lawal Liman ne, ya bayyana hakan a wani taro da mambobin kwamitin rabon takin.

Ya bayyana cewa, kowane daga cikin kananan hukumomi takwas na gundumar Zamfara ta Tsakiya da Arewa za su karbi manyan motocin takin guda biyar.

Sanarwar ta ce yankuna shida na gundumar Zamfara ta Yamma da Sanatan ke wakilta, kowanensu zai karbi manyan motocin takin zamani shida.

LABARAI MASU NASABA

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

Liman ya ce ana sayar da takin tsakanin Naira 40,000 zuwa Naira 45,000 a kasuwa kan kowane buhu mai nauyin kilogiram 50, amma za su sayar wa manoma kan kudi Naira 20,000 kan kowane buhu.

Ya ce manufar tallafin shi ne ceto manoma a fadin jihar daga karancin taki da kuma rage hauhawar farashinsa.

Ya ce tallafin na da nufin zagaya wa mazabu 147 da ke kananan hukumomin jihar 14 ba tare da la’akari da bambancin jam’iyya ba.

Ya bukaci mambobin kwamitin rabon da su tabbatar da bin ka’ida wajen rabon takin.

Shugaban ya kuma sanar da cewa Sanata Yari, ya samar da manyan motoci 28 na shinkafa don raba wa mutane a fadin jihar a lokacin bikin sallah.

Ya ce tallafin zai shafi marasa galihu a fadin jihar.

“A karkashin tsarin da kwamitin malamai zai kula da shi wanda ya gudanar da ayyukan Sanatan a baya, an ware wa kowace karamar hukuma manyan motoci biyu na buhun shinkafa mai nauyin kilogiram 50,”.

Ya sake jaddada kudurin tsohon gwamnan wajen bayar da taimako ga al’ummar Jihar Zamfara.

Ya roki wadanda da aka bai wa amanar rabon kayan tallafin, da su rike amana su yi aiki da gaskiya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista
Labarai

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

November 5, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Labarai

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

November 5, 2025
An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai
Manyan Labarai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Next Post
Kotu Ta Hana Miji Magana Da Matarsa Tsawon Mako Biyu

Saurayi Da Budurwarsa Sun Sace Kayan Lefen ’Yar Uwarsa A Kano

LABARAI MASU NASABA

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

November 5, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

November 5, 2025
An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Sanata Barau Ya Tsaya Takarar Shugaban Majalisar Dattawa

Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio

November 5, 2025
CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

November 5, 2025
Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.