• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sanata Yari Ya Samar Da Taki Ga Manoman Zamfara A Kan Naira 20,000

by Sadiq
1 year ago
in Labarai
0
Sanata Yari Ya Samar Da Taki Ga Manoman Zamfara A Kan Naira 20,000
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon gwamnan Jihar Zamfara, Sanata Abdulaziz Yari, ya samar da manyan motocin takin zamani 76 da za a raba su ga manoma tare sa zaftare kashi 50 cikin 100 na farashinsa a matsayin tallafi. 

Ibrahim Muhammad, shugaban kwamitin yada labaransa ne, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya aike wa manema labarai a Gusau ranar Talata.

  • Neja: An Ceto Mutane 7 Da Suka Makale Wajen Hakar Ma’adanai
  • Gwamna Dauda Lawal Ya Jaddada Ƙudirinsa Na Tsaron Rayukan Al’ummar Zamfara

A cewar sanarwar, shugaban kwamitin, Alhaji Lawal Liman ne, ya bayyana hakan a wani taro da mambobin kwamitin rabon takin.

Ya bayyana cewa, kowane daga cikin kananan hukumomi takwas na gundumar Zamfara ta Tsakiya da Arewa za su karbi manyan motocin takin guda biyar.

Sanarwar ta ce yankuna shida na gundumar Zamfara ta Yamma da Sanatan ke wakilta, kowanensu zai karbi manyan motocin takin zamani shida.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

Liman ya ce ana sayar da takin tsakanin Naira 40,000 zuwa Naira 45,000 a kasuwa kan kowane buhu mai nauyin kilogiram 50, amma za su sayar wa manoma kan kudi Naira 20,000 kan kowane buhu.

Ya ce manufar tallafin shi ne ceto manoma a fadin jihar daga karancin taki da kuma rage hauhawar farashinsa.

Ya ce tallafin na da nufin zagaya wa mazabu 147 da ke kananan hukumomin jihar 14 ba tare da la’akari da bambancin jam’iyya ba.

Ya bukaci mambobin kwamitin rabon da su tabbatar da bin ka’ida wajen rabon takin.

Shugaban ya kuma sanar da cewa Sanata Yari, ya samar da manyan motoci 28 na shinkafa don raba wa mutane a fadin jihar a lokacin bikin sallah.

Ya ce tallafin zai shafi marasa galihu a fadin jihar.

“A karkashin tsarin da kwamitin malamai zai kula da shi wanda ya gudanar da ayyukan Sanatan a baya, an ware wa kowace karamar hukuma manyan motoci biyu na buhun shinkafa mai nauyin kilogiram 50,”.

Ya sake jaddada kudurin tsohon gwamnan wajen bayar da taimako ga al’ummar Jihar Zamfara.

Ya roki wadanda da aka bai wa amanar rabon kayan tallafin, da su rike amana su yi aiki da gaskiya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ManomaSanata YariTakiTallafiZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Neja: An Ceto Mutane 7 Da Suka Makale Wajen Hakar Ma’adanai

Next Post

Saurayi Da Budurwarsa Sun Sace Kayan Lefen ’Yar Uwarsa A Kano

Related

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

1 hour ago
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

3 hours ago
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

6 hours ago
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
Labarai

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

6 hours ago
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

8 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Labarai

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

9 hours ago
Next Post
Kotu Ta Hana Miji Magana Da Matarsa Tsawon Mako Biyu

Saurayi Da Budurwarsa Sun Sace Kayan Lefen ’Yar Uwarsa A Kano

LABARAI MASU NASABA

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

September 17, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

September 17, 2025
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

September 17, 2025
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

September 17, 2025
Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

September 17, 2025
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

September 17, 2025
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

September 17, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

September 17, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.