• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sanata Yari Ya Samar Da Taki Ga Manoman Zamfara A Kan Naira 20,000

by Sadiq
1 year ago
in Labarai
0
Sanata Yari Ya Samar Da Taki Ga Manoman Zamfara A Kan Naira 20,000
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon gwamnan Jihar Zamfara, Sanata Abdulaziz Yari, ya samar da manyan motocin takin zamani 76 da za a raba su ga manoma tare sa zaftare kashi 50 cikin 100 na farashinsa a matsayin tallafi. 

Ibrahim Muhammad, shugaban kwamitin yada labaransa ne, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya aike wa manema labarai a Gusau ranar Talata.

  • Neja: An Ceto Mutane 7 Da Suka Makale Wajen Hakar Ma’adanai
  • Gwamna Dauda Lawal Ya Jaddada Ƙudirinsa Na Tsaron Rayukan Al’ummar Zamfara

A cewar sanarwar, shugaban kwamitin, Alhaji Lawal Liman ne, ya bayyana hakan a wani taro da mambobin kwamitin rabon takin.

Ya bayyana cewa, kowane daga cikin kananan hukumomi takwas na gundumar Zamfara ta Tsakiya da Arewa za su karbi manyan motocin takin guda biyar.

Sanarwar ta ce yankuna shida na gundumar Zamfara ta Yamma da Sanatan ke wakilta, kowanensu zai karbi manyan motocin takin zamani shida.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

Liman ya ce ana sayar da takin tsakanin Naira 40,000 zuwa Naira 45,000 a kasuwa kan kowane buhu mai nauyin kilogiram 50, amma za su sayar wa manoma kan kudi Naira 20,000 kan kowane buhu.

Ya ce manufar tallafin shi ne ceto manoma a fadin jihar daga karancin taki da kuma rage hauhawar farashinsa.

Ya ce tallafin na da nufin zagaya wa mazabu 147 da ke kananan hukumomin jihar 14 ba tare da la’akari da bambancin jam’iyya ba.

Ya bukaci mambobin kwamitin rabon da su tabbatar da bin ka’ida wajen rabon takin.

Shugaban ya kuma sanar da cewa Sanata Yari, ya samar da manyan motoci 28 na shinkafa don raba wa mutane a fadin jihar a lokacin bikin sallah.

Ya ce tallafin zai shafi marasa galihu a fadin jihar.

“A karkashin tsarin da kwamitin malamai zai kula da shi wanda ya gudanar da ayyukan Sanatan a baya, an ware wa kowace karamar hukuma manyan motoci biyu na buhun shinkafa mai nauyin kilogiram 50,”.

Ya sake jaddada kudurin tsohon gwamnan wajen bayar da taimako ga al’ummar Jihar Zamfara.

Ya roki wadanda da aka bai wa amanar rabon kayan tallafin, da su rike amana su yi aiki da gaskiya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ManomaSanata YariTakiTallafiZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Neja: An Ceto Mutane 7 Da Suka Makale Wajen Hakar Ma’adanai

Next Post

Saurayi Da Budurwarsa Sun Sace Kayan Lefen ’Yar Uwarsa A Kano

Related

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

5 hours ago
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

6 hours ago
Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah
Labarai

Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

7 hours ago
Jihohin Da Ke Shirin Rage Kudin Wutar Lantarki Su Shirya Biyan Tallafi – Ministan Wuta
Labarai

Jihohin Da Ke Shirin Rage Kudin Wutar Lantarki Su Shirya Biyan Tallafi – Ministan Wuta

8 hours ago
majalisar kasa
Labarai

‘Yan Majalisa Sun Zargi Hukumomin Gwamnati Da Wawure Sama Da Naira Biliyan 103.8

9 hours ago
Majalisar Wakilai Ta Nemi Amurka Ta Maido Da Bizar Shekara Biyar Ga ‘Yan Nijeriya
Labarai

Majalisar Wakilai Ta Nemi Amurka Ta Maido Da Bizar Shekara Biyar Ga ‘Yan Nijeriya

10 hours ago
Next Post
Kotu Ta Hana Miji Magana Da Matarsa Tsawon Mako Biyu

Saurayi Da Budurwarsa Sun Sace Kayan Lefen ’Yar Uwarsa A Kano

LABARAI MASU NASABA

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

July 25, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

July 25, 2025
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

July 25, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga ZaÉ“en Ƙananan Hukumomi A Kebbi

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

July 25, 2025
Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

July 25, 2025
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

July 25, 2025
Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

July 25, 2025
Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

July 25, 2025
Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.