ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Dauda Lawal Ya Jaddada Ƙudirinsa Na Tsaron Rayukan Al’ummar Zamfara

by yahuzajere
2 years ago
Tsaro

A faɗi-tashin da yake yi wajen samar da ingataccen tsaro, Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya jaddada ƙudirin gwamnatinsa na tabbatar da tsaron rayuka da dukiyar al’ummar Jihar Zamfara.

A ranar Talatar nan ne gwamnan ya halarci bikin yaye wasu dakaru na musamman, waɗanda ke ƙarƙarshin Hukumar tsaro ta Sibil Difens (NSCDC) da ake kira ‘Agro Rangers’ a Jihar Zamfara.

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa, dakarun na ‘Agro Rangers’, jami’ai ne na musamman a Hukumar ta Sibil Difens, waɗanda suka samu horo mai zurfi.

ADVERTISEMENT

Ya kuma ƙara da cewa, an horar da jami’an na musamman a shirye-shiryen gudanar da aikin haɗin gwiwa a yaƙi da ’yan bindiga a Jihar Zamfara.

Tsaro

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

A yayin jawabinsa a wajen bikin, gwamna Lawal ya yaba wa hukumar NSCDC bisa wannan shiri nasu. Ya ce, “Wannan ya zo ne a wani muhimmin lokaci kuma ya yi daidai da ƙudurinmu na ɗaukar ingantattun matakan yaƙi da rashin tsaro.

“Mun ɗauki wannan a matsayin babban mataki na tunkarar ƙalubalen da ya kawo cikas ga al’ummar mu wajen ayyukan noma, sana’o’in dogaro da kai, da sauran hanyoyin samar da abinci a jihar.

“Gwamnatin Jihar Zamfara ta bayyana harkokin tsaro da noma a matsayin muhimman abubuwan da suka sa a gaba. Mun ɓullo da matakai daban-daban don magance ƙalubalen tsaro da kuma bunƙasa noma a jihar. Don haka, muna kallon wannan shiri na jami’an Hukumar Sibil Difens a matsayin wani gagarumin mataki na ci gaba da ɗaukar matakan tsaro da muke ɗauka a matsayin gwamnati tare da jami’an tsaro da ke aiki a jihar.

Tsaro

“A matsayinmu na gwamnati, za mu ci gaba da bada haɗin kai da cibiyoyi, ƙungiyoyi da ɗaiɗaikun mutane wajen yaƙi da duk wani nau’in miyagun laifuka. Mun himmatu wajen samar da tallafin da waɗannan cibiyoyi da ɗaiɗaikun mutane ke buƙata don gudanar da ayyukansu. Manufar farko ita ce tabbatar da tsaron al’ummominmu da kuma sanya su cikin aminci don ayyukan zamantakewa da tattalin arziki wanda zai sauƙaƙe ci gaban jihar da jama’a.

“Ina matuƙar fatan shirin hukumar NSCDC na samar da wani dakarun na musamman, wanda hakan zai samar da mafita mai ɗorewa ga ƙalubalen tsaro da ake fuskanta, musamman waɗanda suka shafi harkar noma.

“Ina da alfahari da ƙaddamar da wannan dakaru. Ina yi muku fatan alheri bisa sauke nauyin da aka ɗora muku. Ina roƙon Allah Ya tsare ku, sannan Ya yi muku jagoranci.”

Tun da farko, Kwamandan Rundunar Sibil Difens a Jihar Zamfara, Kwamanda Sani Mustapha, ya gode wa Gwamna Lawal da gwamnatin Jihar bisa tallafin da suka ba shirin horarwa da dakarun Agro Rangers.

Tsaro

“Yallabai, ɗimbin goyon bayan da ka ke baiwa rundunar ta sa muka kai ga haka. Muna godiya ƙwarai da gaske,” inji shi.

Kwamandan ya ƙara da cewa, Hukumar ta NSCDC ta himmatu wajen samar da zaman lafiya da magance rikice-rikice a yankunan da ake fama da rikici.

Tsaro
yahuzajere
+ postsBio
  • yahuzajere
    Da Kujerar Mulki Gara Zaman Lafiyar Kano
  • yahuzajere
    Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya
  • yahuzajere
    Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
  • yahuzajere
    Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Ruwa

Hajj 2024: Jihar Kaduna Ta Kammala Jigilar Maniyyata Fiye Da 4,000 Zuwa Saudiyya 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.