ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Saraki Ga Gwamnoni Masu Barin Gado: Ku Guji Katsaladan A Mulkin Wadanda Suka Gaje Ku

by Bello Hamza
2 years ago
Saraki

Tsohon shugaban majalisar dattawa, Bukola Saraki, ya nemi gwamnoni masu barin gado su guji katsalandan a harkokin gudanar da mulki a jihohinsu yayin da suke barin gwamnati a karshen watan Mayu.

Saraki ya bayyana haka ne a taron bikin bankwana da aka shirya wa gwamnonin masu barin gado da masu kama mulki a Abuja, Saraki, wanda tsohon gwamnan Jihar Kwara ne, ya shawarci gwamnoni 18 masu barin gado su rungumi sabon rayuwar da za su fuskanta su kuma shirya bayar da gudummawarsu a bangarorin rayuwa da daban daban.

  • Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Soke Nasarar Zababben Gwamnan Jihar Abia, Alex Otti
  • Mutum 2 Sun Shiga Hannu Kan Kisan Ma’aikatan Ofishin Jakadancin Amurka

A sakon fatan alhairi ga gwamnonin, , Saraki ya yaba musu a kan yadda suka bayar da gudumawar bunkasa jihohinsu, sai dai ya karfafa bukatar da su bar gwamnonin da za su gajesu su gudanar da nasu ayyukan ba tare da katsalandan ba.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa, “A yayin da kuka kasance ba gwamnoni ba, ku bar wadanda suka gaje ku su yi aikinsu. Ku koma ga iyanlanku, na tabbatar da cewa a halihn yanzu mata da yaranku da jikokinu na nan duk sun kokasa ku koma gida ku yi ta zumunci a tsakaninsu, ku shirya fuskantar wata rayuwa daban, ku yi tanadin kudadenku don kudaden ba za su rinka shigowa kamar da ba.”

Wani tsohon gwamnan Jihar Neja, Babangida Aliyu ya nemi sabbi da tsofaffin gwamnonin su muhimmantar da jin dadin al’umma a jihohinsu ba tare da nuna banbanci siyasa ba.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

Ya yi gargadi a kan mulkin kama karya, ya ce, irin haka ba zai haifar da da mai ido ba.

“Sau da dama zaka ji wasu na cewa, wannan lokacinmu ne, kada ku yi irin wannan kuskuren, wani tsohon gwamman da ya yi irin wannan ikirarin a yanzu yana can yana yawo a titi.”

Aliyu ya kara da cewa, zamaka gwamna ba yana nufin kai ne ka fi ilimi ko nagarta ba, watakila ma kai ne na karshe a aji a lokacin da kuke karatu amma Allah ya daukaka ka a kan haka kada ku rungumi girman kai a harkokinku.”

Haka kuma tsohon gwamnan jihar Gombe, Ibrahim Dankwambo, ya nemi tsohofaffain gwamnoni su guji katsalanda a harkokin mulkin jihohin na su, su bar sabbin gwamnoni su yi aikin su ba tare da kawo musu cikas ba, ya nemi su rungumi wasu harkokin da za su taimaki rayuwar su.

Taron ya samu halartar manyan baki da dama, da suka hada da, Kayode Fayemi, Aminu Tambuwal, Aminu Masari, Charles Soludo, Bala Mohammed, Babagana Zulum, Dauda Lawal, Reb Fr Hyacinth Alia da sauransu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba
Manyan Labarai

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

November 12, 2025
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

November 8, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!
Rahotonni

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
Next Post
Kasar Sin Ta Amsa Tambayoyin Da Aka Yi Masa Kan Taron Kolin G7 A Hiroshima

Kasar Sin Ta Amsa Tambayoyin Da Aka Yi Masa Kan Taron Kolin G7 A Hiroshima

LABARAI MASU NASABA

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

November 12, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

November 12, 2025
Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 12, 2025
Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

November 12, 2025
Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

November 12, 2025
'yansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutane 4 Kan Zargin Fashi Da Makami A Bauchi

November 12, 2025
Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

November 12, 2025
Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

November 12, 2025
Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

November 12, 2025
Majalisar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Bisa Zargin Rashin Ɗa’a

Majalisar Jihar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Kan Laifin Rashin Ɗa’a

November 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.