• English
  • Business News
Sunday, September 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sha’aban Sharada Ya Roki Kotu Ta Soke Zaben Fid-Da Gwanin Gwamna A APC A Kano

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
in Siyasa
0
Sha’aban Sharada Ya Roki Kotu Ta Soke Zaben Fid-Da Gwanin Gwamna A APC A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar birni da kewaye, sannan shugaban kwamitin tsaro na majalisar wakilai ta kasa, Sha’aban Ibrahim Sharada, ya roki kotu da ta soke zaben fid-da gwanin da akayi na gwamna a jihar Kano wanda mataimakin gwamna Nasiru Yusuf Gawuna ya samu nasara.

Sha’aban, wanda ya tsaya takara a zaben fid-da gwani na gwamna a karkashin jam’iyyar APC, ya garzaya kotu ne inda yake kalubalantar yadda aka gudanar da zaben, wanda akayi a rufaffen dakin wasa na Sani Abacha dake Kano.

  • Majalisar Dokokin Kano Ta Amince Ganduje Ya Ciyo Bashin Biliyan 10 Don Sayen Na’urar CCTV

A cikin takardar korafin da dan majalisar ya shigar, ta hannun lauyansa, J.O Asoluka (SAN), a gaban babbar kotun jihar Kano a ranar Alhamis, ya ce zaben Gawuna a matsayin dan takarar gwamna a jam’iyyar APC ya sabawa sashi na 84 da karamin sashi na 1,2,8,12 da 13 na dokar zabe wadda aka yiwa kwaskwarima. A cikin kunshin korafin dai, lauyan mai gabatar da kara ya ce abinda akayi a zaben ya sabawa dokokin jam’iyyar APC sannan gwamnatin jihar Kano tayi kutse wajen zaben deliget sannan ta tursasa su wajen zaben wanda take so

Bayan kammala zaben dai an bayyana Dr. Nasiru Yusuf Gawuna a matsayin wanda yayi nasara ya yinda tsohon kwamishinan kana nan hukumomi, Murtala Sule Garo ya zama mataimakinsa.

Sha’aban Sharada dai yana rokon kotu ne da ta soke zaben saboda a cewarsa, zaben yana cike da magudi kuma ya saba da sabuwar dokar zabe ta shekara ta 2022 da aka sanyawa hannu a wannan shekarar.

Labarai Masu Nasaba

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

Har ila yau, sha’aban ya nuna damuwa akan yadda masu mukamin siyasa a cikin gwamnatin jihar Kano suka kada kuri’arsu a zaben na fid-da gwani wanda kuma hakan ya saba da dokar zabe sashi na 84 (13) cikin baka wanda ya hana duk wani mai mukamin siyasa yin zaben fid-da gwani.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kama Mutum Uku Da Ke Yin Takardun Mota Na Bogi A Kano

Next Post

Za A Rataye Mutumin Da Ya Kashe Matarsa Bisa Zargin Neman Maza

Related

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa
Siyasa

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

18 hours ago
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC
Siyasa

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

1 day ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Siyasa

Ba Abin Da Zai Hana Tinubu Sake Lashe Zaɓe A 2027 – Jigon APC

4 days ago
2027: Fastocin Takarar Shugaban Ƙasa Na Gwamnan Bauchi Sun Bayyana
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Gargaɗi Magoya Bayan Wike A PDP

4 days ago
Ina Da Yaƙinin Tinubu Ne Zai Lashe Zaɓen 2027 — Wike
Siyasa

Ina Da Yaƙinin Tinubu Ne Zai Lashe Zaɓen 2027 — Wike

6 days ago
Ɗaukar Nauyin Ƴan Ta’addan Da Suka Farmake Mu A Kaduna Aka Yi – El-Rufai
Siyasa

Ɗaukar Nauyin Ƴan Ta’addan Da Suka Farmake Mu A Kaduna Aka Yi – El-Rufai

6 days ago
Next Post
Za A Rataye Mutumin Da Ya Kashe Matarsa Bisa Zargin Neman Maza

Za A Rataye Mutumin Da Ya Kashe Matarsa Bisa Zargin Neman Maza

LABARAI MASU NASABA

Hanyoyin Kare Kai Daga Cutar Basir Cikin Sauƙi

Hanyoyin Kare Kai Daga Cutar Basir Cikin Sauƙi

September 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG

Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG

September 7, 2025
Arewa

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

September 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

Kwamishinan ‘Yansandan Abuja Ya Gargadi Jami’ansa Kan Arangama Da Direbobi A Titi

September 7, 2025
Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu

Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu

September 7, 2025
ASUU

Malaman Jami’o’i Sun Zama Abin Tausayi —Kungiyar ASUU

September 7, 2025
Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya

Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya

September 7, 2025
Zulum Ya Tabbatar Da Harin Boko Haram Ya Ci Rayukan Mutane 63 

Zulum Ya Tabbatar Da Harin Boko Haram Ya Ci Rayukan Mutane 63 

September 7, 2025
Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

September 7, 2025
Fyade

Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan

September 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.