• English
  • Business News
Sunday, May 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sha’aban Sharada Ya Roki Kotu Ta Soke Zaben Fid-Da Gwanin Gwamna A APC A Kano

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
in Siyasa
0
Sha’aban Sharada Ya Roki Kotu Ta Soke Zaben Fid-Da Gwanin Gwamna A APC A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar birni da kewaye, sannan shugaban kwamitin tsaro na majalisar wakilai ta kasa, Sha’aban Ibrahim Sharada, ya roki kotu da ta soke zaben fid-da gwanin da akayi na gwamna a jihar Kano wanda mataimakin gwamna Nasiru Yusuf Gawuna ya samu nasara.

Sha’aban, wanda ya tsaya takara a zaben fid-da gwani na gwamna a karkashin jam’iyyar APC, ya garzaya kotu ne inda yake kalubalantar yadda aka gudanar da zaben, wanda akayi a rufaffen dakin wasa na Sani Abacha dake Kano.

  • Majalisar Dokokin Kano Ta Amince Ganduje Ya Ciyo Bashin Biliyan 10 Don Sayen Na’urar CCTV

A cikin takardar korafin da dan majalisar ya shigar, ta hannun lauyansa, J.O Asoluka (SAN), a gaban babbar kotun jihar Kano a ranar Alhamis, ya ce zaben Gawuna a matsayin dan takarar gwamna a jam’iyyar APC ya sabawa sashi na 84 da karamin sashi na 1,2,8,12 da 13 na dokar zabe wadda aka yiwa kwaskwarima. A cikin kunshin korafin dai, lauyan mai gabatar da kara ya ce abinda akayi a zaben ya sabawa dokokin jam’iyyar APC sannan gwamnatin jihar Kano tayi kutse wajen zaben deliget sannan ta tursasa su wajen zaben wanda take so

Bayan kammala zaben dai an bayyana Dr. Nasiru Yusuf Gawuna a matsayin wanda yayi nasara ya yinda tsohon kwamishinan kana nan hukumomi, Murtala Sule Garo ya zama mataimakinsa.

Sha’aban Sharada dai yana rokon kotu ne da ta soke zaben saboda a cewarsa, zaben yana cike da magudi kuma ya saba da sabuwar dokar zabe ta shekara ta 2022 da aka sanyawa hannu a wannan shekarar.

Labarai Masu Nasaba

PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

Kyakkyawan Tunanin Kwankwaso Na Kafa Jami’ar Kimiyya Ta Wudil Ta Zama Alkairi Ga Al’umma – Alhaji Abdukadir

Har ila yau, sha’aban ya nuna damuwa akan yadda masu mukamin siyasa a cikin gwamnatin jihar Kano suka kada kuri’arsu a zaben na fid-da gwani wanda kuma hakan ya saba da dokar zabe sashi na 84 (13) cikin baka wanda ya hana duk wani mai mukamin siyasa yin zaben fid-da gwani.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kama Mutum Uku Da Ke Yin Takardun Mota Na Bogi A Kano

Next Post

Za A Rataye Mutumin Da Ya Kashe Matarsa Bisa Zargin Neman Maza

Related

PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe
Siyasa

PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

6 hours ago
Kyakkyawan Tunanin Kwankwaso Na Kafa Jami’ar Kimiyya Ta Wudil Ta Zama Alkairi Ga Al’umma – Alhaji Abdukadir
Ilimi

Kyakkyawan Tunanin Kwankwaso Na Kafa Jami’ar Kimiyya Ta Wudil Ta Zama Alkairi Ga Al’umma – Alhaji Abdukadir

16 hours ago
Majalisar Wakilai Ta Yi Watsi Da Kafa Dokar Karba-karba A Shugabancin Nijeriya
Siyasa

Majalisar Wakilai Ta Yi Watsi Da Kafa Dokar Karba-karba A Shugabancin Nijeriya

2 days ago
A Tsammaci Garambawul Ga Dokar Zabe Kafin Zaben 2027 — Shugaban INEC
Siyasa

A Tsammaci Garambawul Ga Dokar Zabe Kafin Zaben 2027 — Shugaban INEC

2 days ago
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC
Siyasa

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

3 days ago
Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa
Labarai

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

5 days ago
Next Post
Za A Rataye Mutumin Da Ya Kashe Matarsa Bisa Zargin Neman Maza

Za A Rataye Mutumin Da Ya Kashe Matarsa Bisa Zargin Neman Maza

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Makarantar Katsina-kwalej Zuwa Ta Horon Malamai (1)

Tarihin Makarantar Katsina-kwalej Zuwa Ta Horon Malamai (1)

May 18, 2025
Abin Da Ya Dace Ki Yi Yayin Haila Da Bayan Kin Gama?

Abin Da Ya Dace Ki Yi Yayin Haila Da Bayan Kin Gama?

May 18, 2025
Ciwon Mara Lokacin Al’ada

Ciwon Mara Lokacin Al’ada

May 18, 2025
Kasar Sin Ta Samu Bunkasar Masana’antar Harkokin Tauraron Dan Adam A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Bunkasar Masana’antar Harkokin Tauraron Dan Adam A Shekarar 2024

May 18, 2025
Yanzu-Yanzu: Ana Zargin Makiyaya Sun Kashe Mutane 15 A Benuwe

Yanzu-Yanzu: Ana Zargin Makiyaya Sun Kashe Mutane 15 A Benuwe

May 18, 2025
An Cafke Mai Garkuwa Da Mutane A Sansanin Alhazan Abuja

An Cafke Mai Garkuwa Da Mutane A Sansanin Alhazan Abuja

May 18, 2025
Kasar Sin Ta Sanya Harajin Takaita Shigo Da Kayayyakin Robobi Masu Tauri

Kasar Sin Ta Sanya Harajin Takaita Shigo Da Kayayyakin Robobi Masu Tauri

May 18, 2025
Yadda Ake Hada Danderun Kaza

Yadda Ake Hada Danderun Kaza

May 18, 2025
Ban Ɗauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa

Ban Ɗauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa

May 18, 2025
PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

May 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.