• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sha’aban Sharada Ya Roki Kotu Ta Soke Zaben Fid-Da Gwanin Gwamna A APC A Kano

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
in Siyasa
0
Sha’aban Sharada Ya Roki Kotu Ta Soke Zaben Fid-Da Gwanin Gwamna A APC A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar birni da kewaye, sannan shugaban kwamitin tsaro na majalisar wakilai ta kasa, Sha’aban Ibrahim Sharada, ya roki kotu da ta soke zaben fid-da gwanin da akayi na gwamna a jihar Kano wanda mataimakin gwamna Nasiru Yusuf Gawuna ya samu nasara.

Sha’aban, wanda ya tsaya takara a zaben fid-da gwani na gwamna a karkashin jam’iyyar APC, ya garzaya kotu ne inda yake kalubalantar yadda aka gudanar da zaben, wanda akayi a rufaffen dakin wasa na Sani Abacha dake Kano.

  • Majalisar Dokokin Kano Ta Amince Ganduje Ya Ciyo Bashin Biliyan 10 Don Sayen Na’urar CCTV

A cikin takardar korafin da dan majalisar ya shigar, ta hannun lauyansa, J.O Asoluka (SAN), a gaban babbar kotun jihar Kano a ranar Alhamis, ya ce zaben Gawuna a matsayin dan takarar gwamna a jam’iyyar APC ya sabawa sashi na 84 da karamin sashi na 1,2,8,12 da 13 na dokar zabe wadda aka yiwa kwaskwarima. A cikin kunshin korafin dai, lauyan mai gabatar da kara ya ce abinda akayi a zaben ya sabawa dokokin jam’iyyar APC sannan gwamnatin jihar Kano tayi kutse wajen zaben deliget sannan ta tursasa su wajen zaben wanda take so

Bayan kammala zaben dai an bayyana Dr. Nasiru Yusuf Gawuna a matsayin wanda yayi nasara ya yinda tsohon kwamishinan kana nan hukumomi, Murtala Sule Garo ya zama mataimakinsa.

Sha’aban Sharada dai yana rokon kotu ne da ta soke zaben saboda a cewarsa, zaben yana cike da magudi kuma ya saba da sabuwar dokar zabe ta shekara ta 2022 da aka sanyawa hannu a wannan shekarar.

Labarai Masu Nasaba

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

Har ila yau, sha’aban ya nuna damuwa akan yadda masu mukamin siyasa a cikin gwamnatin jihar Kano suka kada kuri’arsu a zaben na fid-da gwani wanda kuma hakan ya saba da dokar zabe sashi na 84 (13) cikin baka wanda ya hana duk wani mai mukamin siyasa yin zaben fid-da gwani.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kama Mutum Uku Da Ke Yin Takardun Mota Na Bogi A Kano

Next Post

Za A Rataye Mutumin Da Ya Kashe Matarsa Bisa Zargin Neman Maza

Related

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 
Siyasa

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

1 day ago
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu
Siyasa

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

1 day ago
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya
Siyasa

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

1 day ago
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta
Siyasa

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

3 days ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

3 days ago
Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson
Siyasa

Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

3 days ago
Next Post
Za A Rataye Mutumin Da Ya Kashe Matarsa Bisa Zargin Neman Maza

Za A Rataye Mutumin Da Ya Kashe Matarsa Bisa Zargin Neman Maza

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.