• English
  • Business News
Friday, August 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Ko INEC Za Ta Samu Nasarar Sahihin Zabe A 2023?

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Sharhi: Ko INEC Za Ta Samu Nasarar Sahihin Zabe A 2023?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bisa yadda lamura suke gudana a halin yanzu, Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta Ta Kasa (INEC), tana bukatar samun cikakken goyon baya daga wurin masu ruwa da tsaki kafin ta samu hanyar gudanar da sahihin zabe a 2023.

Shekaru da dama ‘yan siyasan Nijeriya suna kokarin bin duk wata hanya domin zama kan karagar mulki tare da amfani da ofishinsu wajen ci gaba da mulkar al’umma.

  • INEC Ta Tabbatar Da Cafke Jami’inta Da Ke Karbar Na Goro Yana Wa Jama’a Rijistar Zabe A Ribas

Sahihin zabe kuma karbabbe ga mutane ya kasance yana da tushe da ke rike da dimokuradiyya a ko’ina a fadin duniya. Sai dai abun takaici a Nijeriya wadannan ginshikai na dimokuradiyya suna nema su zama tarihi.

Rashin tsari da amfani da kudade da akidar jari hujja da rabuwar kawuna da kuma kokarin ci gaba da zama a kan karagar mulki sun jefa siyasar Nijeriya cikin rashin tabbas wanda ‘yan siyasa a Nijeriya suke amfani da su a matsayin makamin zama a kan mulki.

Lallai wadannan rashin tsari a cikin siyasar Nijeriya ba za su iya samar da kyakkyawan gwamnati ba ballantana a samu bunkasan tattalin arziki a cikin kasar nan, domin suna iya zama wani bakan gizo ne da zai iya hadiye ayyukan gwamnatin da za ta hau karagar mulki na tsawan shekaru 10. Alal misali, kamar yadda ‘yan takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar APC suka biya kudin tikitin takara na naira miliyan 100 da kuma ‘yan takarar shugaban kasa karkashin PDP da suka sayi tikitin takara a kan naira miliyan 40.

Labarai Masu Nasaba

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Akwai abun mamaki a kan haka, ganin yadda mafi yawancin ‘yan Nijeriya da suke fama da yunwa, wanda wadannan kudade zai iya ciyar da su ko da na wata daya ne.

Babban abin takaicin ma dai shi ne, yadda ‘yan siyasa masu neman takara suke raba wa daliget daloli domin su zabe su a lokacin zaben fid da gwani da suka gabata.

Don haka, idan aka duba irin wadannan abubuwa a cikin siyasar Nijeriya akwai abin damuwa a kan ko INEC za ta iya gudanar da sahihin zabe a 2023?.
Idan har ‘yan siyasa za su ci gaba da gudanar da irin wadannan mugayen dabi’u a cikin siyasar Nijeriya, to ta yaya za a iya samun sahihin zabe. Idan har wanda ya ci zabe ba ta hanyar da ya inganta ba, zai kasance manufofinsa da tsare-tsarensa ba za su iya bunkasa tattalin arzikin kasar nan ba.

Wajibe ne sahihin zabe ya kasance wanda mutane suke zabe shi ya samu nasara, a nan dole ne INEC ta ci gaba da samun goyon bayan masu ruwa da tsaki domin samun nasarar gudanar da sahihin zabe a 2023.

Idan aka duba irin matsalolin da kasar nan take fuskanta, zaben 2023 zai kasance mai matukar cike da kalubale ga hukumar INEC.

Miliyoyin ‘yan Nijeriya suna nuna halin ko-in-kula game da zabe sakamakon cewa ko sun jefa kuri’a ba a amfani da ita wajen fitar da sakamakon zabe. Domin haka, sun gunmaci amsar kudade daga hannun ‘yan siyasa kafin su jefa kuri’arsu.
Wasu ‘yan siyasa suna amfani da yakin neman zabe wajen tayar da zaune-tsaye da zai iya kawo hargitsi wanda ke shafar gudanar da sahihin zabe, to dole ne hukumar INEC da dauki mataki a kan haka.

Hakazalika, ko a zaben Jihar Ekiti da gudana sai da jam’iyyar PDP ta yi korafin cewa, APC ta yi amfani da kudi wajen lashe zabe a jihar.

Hukumar INEC ta bayyana sunan dan takarar gwamna a karkashin jam’iyyar APC, Abiodun Oyebanji a matsayin wanda ya lashe zaben Jihar Ekiti da ya gudana a ranar Asabar da ta gabata.

Shi dai Oyebanji ya samu nasara ne a kananan hukumoni 15 cikin 16 da ke fadin jihar, inda ya samu kuri’u guda 187,057. Yayin da dan takarar da ke binsa, Segun Oni ya samu kuri’u 82,211, sai kuma dan takarar jam’iyyar PDP, Bisi Kolawole ya samu kuri’u 67,457.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Akalla Malamai 100 Daga Arewacin Nijeriya Suka Yi Addu’ar Samun Nasarar Zaben 2023

Next Post

Yadda Matafiya 18 Suka Rasa Rayukansu Sakamakon Hadarin Mota A Neja

Related

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

7 days ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

1 week ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga ZaÉ“en Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

1 week ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2 weeks ago
majalisar kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

2 weeks ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

3 weeks ago
Next Post
Yadda Matafiya 18 Suka Rasa Rayukansu Sakamakon Hadarin Mota A Neja

Yadda Matafiya 18 Suka Rasa Rayukansu Sakamakon Hadarin Mota A Neja

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

August 1, 2025
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

August 1, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto DimokuraÉ—iyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto DimokuraÉ—iyyar Nijeriya Daga Rugujewa

August 1, 2025
Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

August 1, 2025
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

August 1, 2025
Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

August 1, 2025
Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

August 1, 2025
An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

August 1, 2025
Zhao Leji Ya Yi Jawabi A Babban Taron Shugabannin Majalisun Kasa Da Kasa Karo Na 6

Zhao Leji Ya Yi Jawabi A Babban Taron Shugabannin Majalisun Kasa Da Kasa Karo Na 6

August 1, 2025
Sin Ta Samarwa Sassan Kasa Da Kasa Damar Shigowa Ba Tare Da Bukatar Biza Ba

Sin Ta Samarwa Sassan Kasa Da Kasa Damar Shigowa Ba Tare Da Bukatar Biza Ba

August 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.