• English
  • Business News
Tuesday, August 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Shin Tinubu Zai Iya Kai Bantensa Bisa Yadda Ya Fara?

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Labarai
0
Sharhi: Shin Tinubu Zai Iya Kai Bantensa Bisa Yadda Ya Fara?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

Biyo bayan ganawar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi da hafsoshin tsaro a makon da ya gabata bayan hawansa mulki tare da karanta masu karatun-ta-natsu, miliyoyin ‘yan Nijeriya na fatan cewa za a samu gagarumin sauyi kan yanayin rashin tsaro tare dawo da Nijeriya cikin hayyacinta.

Tun bayan da aka rantsar da shi a matsayin zababben shugaban kasar Nijeriya na 16, Tinubu ya dai gaji tsohon Shugaban kasa Muhammadu Buhari. Bayan rantsar da shi, wata tambaya daya ke ci gaba da yawo a zukatan ‘yan Nijeriya da dama shi ne, Shin ko Tinubu zai iya cika alkawarin da ya dauka na magance matsalar rashin tsaro da kasar nan ke fama da shi.

  • Jami’an Amurka Ba Za Su Iya Dakatar Da Matakan Sulhu Na Kasashen Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba
  • Tinubu Zai Gana Da Zababbun Sanatoci A Gobe Alhamis

Bisa kididdigar kashe-kashen da aka yi a Nijeriya da wata cibiyar bincike ta Amurka ta fitar, ya nuna cewa an kashe akalla mutane 89,920 a Nijeriya sakamakon tashe-tashen hankula a cikin shekaru bakwai na farko na gwamnatin Buhari daga Mayu 2015 zuwa Mayu 2022.

Ita ma wata kungiya da ta sadaukar da kai wajen bin diddigin tashe-tashen hankula a Nijeriya ta fitar da rahotonta na shekarar 2023, wanda ya nuna cewa an kashe mutane 1,230 a kasar a rubu’in farko na shekarar 2023.

Rahoton ya kuma ce jami’an tsaro 79 ne suka mutu a cikin wannan lokaci, yayin da aka yi garkuwa da mutane 658 a fadin kasar.

ko bayan rantsar da Tinubu an ci gaba da kashe mutane tare da yin garkuwa da wasu da dama a cikin Nijeriya.

A daidai lokacin da Shugaba Tinubu ya hau kan karagar mulki, idanun ‘yan Nijeriya sun koma kansa tare da yi masa fatan alkairi na ganin ya magance kalubalen da ke gaban kasar nan, nusamman ma a bangaren tsaro. ‘Yan Nijeriya dai na sha’awar samar da kasa mai cike da tsaro, domin su samu nasarar yin barci da idanuwansu guda biyu ba tare da wata fargaba ba.

Bisa kudurinsa na magance tsaro, Tinubu ya yi ganawarsa ta farko da hafsoshin tsaron kasar nan, inda ya bayyana musu cewa bu sauran bayar da uzuri a bangaren jami’an tsaro.

Ya kuma bayyana musu cewa ba zai yarda da halin da al’ummar kasa ke ci gaba da raguwa ba. A cewar shugaban, a yanayin da yake ciki a halin yanzu, dole ne a hada kan tsaron kasa wajen ceto kasar nan.

Shugaban ya umarci hukumomin tsaro da su fito da wani tsari na magance matsalar rashin tsaro a Nijeriya. Ya ce ba shi da isasshen lokaci dole ne a gudanar da sauye-sauyen da suka dace da wuri-wuri.

Taron wanda shi ne na farko da hafsoshin tsaro, ya kasance karkashin jagorancin babban hafsan tsaro, Janar Lucky Irabor. Sauran wadanda suka halarci taron sun hada da babban hafsan sojin kasa, Laftanar Janar Farouk Yahaya da babban hafsan sojin ruwa, Bice Admiral Awwal Gambo da shugaban hafsan sojan sama, Air Marshal Isiaka Amao da babban sufetan ‘yansanda, Usman Alkali Baba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Tinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Illar Kakaba Wa Majalisa Ta 10 Shugabanni Ga Gwamnatin Tinubu – Dattawan Arewa

Next Post

… A Makon Farkon Mulkin Tinubu, Mutum 78 Sun Mutu Tare Da Garkuwa Da 12

Related

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato
Labarai

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

12 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

16 hours ago
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe
Ra'ayi Riga

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

16 hours ago
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano
Manyan Labarai

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

16 hours ago
Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara
Labarai

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

18 hours ago
Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa
Labarai

Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

19 hours ago
Next Post
… A Makon Farkon Mulkin Tinubu, Mutum 78 Sun Mutu Tare Da Garkuwa Da 12

... A Makon Farkon Mulkin Tinubu, Mutum 78 Sun Mutu Tare Da Garkuwa Da 12

LABARAI MASU NASABA

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

August 4, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

August 4, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

August 4, 2025
Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

August 4, 2025
Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

August 4, 2025
Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

August 4, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

August 4, 2025
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

August 4, 2025
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

August 4, 2025
Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.