• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawarar Da Na Ba Tinubu Kan Tsadar Rayuwa A Nijeriya – Shugabar WTO

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Labarai
0
Irin Ministocin Da ‘Yan Nijeriya Ke Tsammani Daga Gwamnatin Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

Darakta Janar na hukumar kasuwanci ta duniya (WTO), Dakta Ngozi Okonlo-Iweala ta ce Nijeriya na bukatar bullo da shirye-shiryen da za su taimaka wa al’umma wajen samar da ayyukan yi ga matasa da mata.

Okonlo-Iweala ta bayyana hakan ne da take yi wa manema labarai jawabi a fadar shugaban kasa bayan ganawarta da Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu a ranar Talata, ta ce bullo da shirye-shirye na al’ummar kasa zai magance wasu matsalolin da ke addabar ‘yan Nijeriya a halin yanzu.

  • Gwamnatin Gombe Za Ta Dauki Sababbin Ma’aikatan Lafiya 200
  • Fasahar Zane-zane Na Iya Bunƙasa Samar Da Kuɗaɗen Waje Ga Nijeriya – CIS James 

“Mun ga shugaban kasa, kuma mun tattauna kan yadda za mu tallafa wa ‘yan Najeriya a wannan lokaci na bukata. Duk mun san cewa ‘yan Nijeriya na cikin matsanancin halin, kowa yana kokawa. Hakan ne ma ya sa na kawo wannan ziyara da kaina. Wannan ba aikin WTO ba ne a hukumance, amma mun sami damar tattaunawa da shugaban kasa kan irin shirye-shiryen da za a iya yi don tabbatar da cewa ana rage radadin da’yan Nijeriya ke sha.

“Mun gudanar da tattaunawa mai matukar muhimmanci kan kokarin bullo da tsare-tsare da za su taimaka wa al’umma wajen samar da ayyukan yi ga matasa, kuma tallafa wa mata da kananan yara, wadanda za su rage wasu wahalhalun da ake fama da su a cikin kasa.

“Mun yi magana na tsawon lokaci, muna bukatar samun damar saka hannun jari da Nijeriya za ta iya dogaro da kanta, ciki har da habaka masana’antar sarrafa magunguna. Mun kuma yi magana kan irin tallafin da hukumar kasuwanci ta duniya za ta iya kawowa.

“Mun yi aiki a Nijeriya tare da mata, musamman wadanda suka mallaki kanana da matsakaitan masana’antu don kokarin taimaka musu wajen inganta kayayyakinsu ta fannin noma, masaku da sauran fannoni domin su samu damar sayar da su da daraja a kasashen duniya.

“Muna kokarin taimaka musu ta fannin fasahar zamani, domin mu horar da matan Nijeriya da masu kananan sana’o’i da matsakaitan masana’antu wajen kara habaka kasuwancinsu da samar da ayyukan yi.

“Abin da muka tattauna da mai girma shugaban kasa kenan a matsayina ta darakta janar ta kungiyar kasuwanci ta duniya, za mu yi kokarin iya bakin  kokarinmu don tallafa wa ‘yan Nijeriya a wannan lokaci,” in ji ta.

An Cafke Masu Safarar Kwaya 214 Cikin Wata Bakwai A Gombe

Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa reshen Jihar Gombe, ta ce ta kama mutum akalla 214 da take zargi da laifin safarar miyagun kwayoyi a jihar tsakanin watan Janairu zuwa Yuli.

Haka nan, an kama ‘Cannabis Satiba’ mai nauyin kilo giram 93.95, da kuma Kilo giram 257.5 na abubuwan da suka shafi ‘Psychotropic’ da Methamphetamine daga hannun wadanda ake zargin a wannan lokaci.

Kamfanin Dillancin Labarun Nijeriya ya ruwaito cewa Mataimakin Kwamandan Hukumar na Jihar, Bello Mumini ne ya bayyana hakan a wani taro da kungiyar kwararrun masu ba da shawara a Nijeriya ta shirya.

Da yake gabatar da kasidarsa mai taken “Halin da ake fama da shi game da ta’ammali da muggan kwayoyi a Jihar Gombe,” Mumini ya ce wadanda ake zargin 214 sun hada da maza 200 da mata 14.

Ya ce daga cikin mutum 214 da aka kama, 137 daga cikinsu an gurfanar da su a gaban kotu.

Jami’in Hukumar na NDLEA, ya yi tir da yadda ake fama da matsalar shaye-shayen miyagun kwayoyi a jihar, inda ya kara da cewa hakan yana tasir a tsakanin jinsi, cikin shekaru da kuma yin illa a zamantakewar al’umma.

Ya ce abin takaici ne yadda ake samun mata da dama suna shiga harkar shan miyagun kwayoyi a jihar.

 Ya kuma ce abin takaici ne da ya zamto ba a yin amfani da cibiyar gyaran hali ta NDLEA a jihar yadda ya kamata duk da yawaitar shan miyagun kwayoyi a jihar.

Ya ce, “Cibiyar gyaran hali ta NDLEA tana aiki amma ba a amfani da ita kamar yadda ya kamata.

“Muna da daki mai gadaje 24 amma mafi girman abin da muke samu shi ne mutum bakwai da ake tsarewa domin kula da gyaran hallaya da dabi’unsu.

“Wannan shi ne dalilin da ya sa nake kira ga gwamnatin jihar da gwamnatin tarayya da su tallafa wa cibiyar tare da tallafa wa ake kai wa wurin don inganta rayuwarsu.”

Mumini ta yaba wa kungiyar ta APROCON bisa gudanar da gangamin yaki da hana shaye-shayen miyagun kwayoyi a yayin da take yi wa matasa nasiha akan illar shan muggan kwayoyi da sauran abubuwan sa maye.

A nata bangaren, Shugabar Kungiyar ta APROCON, Dakta Habiba Isah, ta ce shaye-shayen miyagun kwayoyi ya zama wata barazana da ya kamata ta da mu da duk masu ruwa da tsaki mu shigo ciki domin ganin an magance irin illar da ke tattare da ita da kuma rayuwar matasa.

Ta ce kungiyarta ta kaddamar da yaki da wannan barna kuma za ta je wasu manyan makarantun jihar domin jawo hankalin matasa da kuma hana su shan miyagun kwayoyi ta hanyar nusar da su hanyoyin illar abin.

Isah, wacce kuma ita ce Shugabar Sashen, Gidauniyar Ilimi ta Tsangayar Ilimi ta Jami’ar Jihar Gombe, ta bukaci iyaye da su yi taka-tsan-tsan tare da kare ‘ya’yansu daga shan ta’ammali da miyagun kwayoyi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Gaggauta Gyara Kura-Kurai Da Bin Ka’idojin WTO

Next Post

’Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina

Related

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

3 hours ago
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

4 hours ago
Ganduje Ba Zai Hana Kwankwaso Shiga APC Ba
Labarai

Murabus Ɗin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin Ɗaukar Wani Mataki

5 hours ago
Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

8 hours ago
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

17 hours ago
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu
Labarai

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

19 hours ago
Next Post
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

June 30, 2025
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

June 30, 2025
Sin Ta Kalubalanci Kasashen Yammacin Duniya Da Su Tuna Da Laifinsu Na Mulkin Mallaka

Cikar MDD Shekara 80: Nasarorinmu Sun Kara Mana Kaimi Da Kyakkyawar Makoma A Nan Gaba

June 30, 2025
Ganduje Ba Zai Hana Kwankwaso Shiga APC Ba

Murabus Ɗin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin Ɗaukar Wani Mataki

June 30, 2025
Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

June 30, 2025
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

June 29, 2025
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

June 29, 2025
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

June 29, 2025
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.