• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawarwarin Kwamitin Ma’aikatar Bunkasa Kiwon Dabbobi Ga Gwamnatin Tarayya

by Abubakar Abba
11 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Shawarwarin Kwamitin Ma’aikatar Bunkasa Kiwon Dabbobi Ga Gwamnatin Tarayya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ci gaba da kokarin dakile yawaitar samun rikice-rikice a tsakanin manoma da makiyaya, musamman a Arewacin Nijeriya; a watan Yulin 2024, gwamnatin tarayya ta kaddamar da sabuwar ma’aikatar bunkasa kiwon dabbobi.

Haka zalika, domin dakile kaluabelen da ake fuskanta tare da bunkasa fannin na kiwo; Shugaban Kasa Bola Tinubu, ya kafa kwamitin mutum 23 don bayar da shawarwari ga sabuwar ma’aikatar ta bunkasa kiwon dabbobi.

  • Kashi 67 Cikin 100 Na Ɗaliban Kaduna Sun Samu Nasara A WAEC – Kwamishinan Ilimi
  • Ronaldo Da Messi Ne Kan Gaba A Jerin ‘Yan Wasan Da Suka Fi Karbar Albashi

Ko shakka babu, wannan fanni na kiwo a fadin Nijeriya na matukar bayar da gagarumar gudunmawa, wajen kokarin ci gaba da wadata wannan kasa da abinci.

Sai dai, daya daga cikin manyan kalubalen da fannin ke ci gaba da fuskanata a fadin kasar shi ne, yawan samun rikici tsakanin manoma da makiyya, wanda hakan ke ci gaba da shafar ayyukan aikin noma na kasar.

Wani rahoto na Afirka da ke bibiyar hada-hadar kasuwanni da kuma fannin tsaro (SBM) ya bayyana cewa, sama da manoma 1,356 ne suka rasa rayukansu a Arewacin Nijeriya, sakamakon hare-haren ‘yan bindigar daji a tsakanin 2020 zuwa 2024.

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Wadannan rikice-rikice da aka saba yi shekaru da dama, sun haifar da rikici iri-iri tare da tarwatsa al’umma daga matsugunansu da kuma lalata gonakai da dama.

Jaridar BusinessDay’s, ta yi nazari a kan shawarwarin da kwamtin ya bayar da suka hada da:

1- Kirkiro Da Shirin Zaunar Da Makiyayan Wuri Guda:

Akwai bukatar jawo makiyayan a jiki tare da taimaka musu, domin su rungumi tsarin kiwo na zamani.

Kwamitin ya kuma bayar da shawarar kirkiro da warin kiwo na zamani, musamman domin a zaunar da makiyayan wuri guda.

A cewar kwamtin, ya kamata a fara gyaran kowane wajen kiwon, wanda hakan zai taimaka wajen tattara makiyayan wuri guda.

Ya kuma kamata a samar wa da makiyayan dabarun zamani kan yadda za su rika kula da dabbobinsu.

2- Bunkasa Hada-hadar Kasuwancin Sayar Da Naman Shanu Da Madara:

Kwamitin ya sanar da cewa, ta hanyar samar musu da wajen yin kiwo na zamani, hakan zai taimaka wa makiyayan wajen hada-hadar kasuwancin sayar da naman dabbobinsu da madara da kuma noma abincin Shanunsu da kwamda suke bukata; don ciyar da iyalansu.

A cewar rahoton, za a iya samun nasara akalla a jihohi 20; kuma a cikin shekaru biyar, domin samar da akalla wajen kiwo 5,000; wanda za a ajiye Shanu 50 a cikin kowanne, wanda kuma hakan zai sanya a samar da madara da dabbobin da za a yanka a karkashin shirin.

3 Hada-hadar Kasuwancin Fatar Shanu:

Kwamitin ya bayar da tabbacin cewa, zai magance kalubalen da ake fuskanta a fannin hada-hadar Fatar Shanu; ta yadda za a rika samar da kudaden shiga a fannin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DabobbiGwamnatin Tarayya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wakilin MƊD Ya Nuna Alhini Kan Fashewar Tankar Mai A Jigawa

Next Post

An Bukaci Gwamnain Tarayya Ta Sake Inganta Harkokin Amfanin Gona

Related

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

2 weeks ago
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON
Noma Da Kiwo

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

2 weeks ago
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

4 weeks ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

4 weeks ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

1 month ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

1 month ago
Next Post
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

An Bukaci Gwamnain Tarayya Ta Sake Inganta Harkokin Amfanin Gona

LABARAI MASU NASABA

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
Gwamnatin

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Xi Jinping Ya Aika Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafuwar Jam’iyyar Zhigong Ta Sin

Xi Jinping Ya Aika Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafuwar Jam’iyyar Zhigong Ta Sin

September 19, 2025
An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

September 19, 2025
Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

September 19, 2025
Gwamnatin

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

September 19, 2025
Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.