• English
  • Business News
Monday, May 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawarwarin Kwamitin Ma’aikatar Bunkasa Kiwon Dabbobi Ga Gwamnatin Tarayya

by Abubakar Abba
7 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Shawarwarin Kwamitin Ma’aikatar Bunkasa Kiwon Dabbobi Ga Gwamnatin Tarayya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ci gaba da kokarin dakile yawaitar samun rikice-rikice a tsakanin manoma da makiyaya, musamman a Arewacin Nijeriya; a watan Yulin 2024, gwamnatin tarayya ta kaddamar da sabuwar ma’aikatar bunkasa kiwon dabbobi.

Haka zalika, domin dakile kaluabelen da ake fuskanta tare da bunkasa fannin na kiwo; Shugaban Kasa Bola Tinubu, ya kafa kwamitin mutum 23 don bayar da shawarwari ga sabuwar ma’aikatar ta bunkasa kiwon dabbobi.

  • Kashi 67 Cikin 100 Na Ɗaliban Kaduna Sun Samu Nasara A WAEC – Kwamishinan Ilimi
  • Ronaldo Da Messi Ne Kan Gaba A Jerin ‘Yan Wasan Da Suka Fi Karbar Albashi

Ko shakka babu, wannan fanni na kiwo a fadin Nijeriya na matukar bayar da gagarumar gudunmawa, wajen kokarin ci gaba da wadata wannan kasa da abinci.

Sai dai, daya daga cikin manyan kalubalen da fannin ke ci gaba da fuskanata a fadin kasar shi ne, yawan samun rikici tsakanin manoma da makiyya, wanda hakan ke ci gaba da shafar ayyukan aikin noma na kasar.

Wani rahoto na Afirka da ke bibiyar hada-hadar kasuwanni da kuma fannin tsaro (SBM) ya bayyana cewa, sama da manoma 1,356 ne suka rasa rayukansu a Arewacin Nijeriya, sakamakon hare-haren ‘yan bindigar daji a tsakanin 2020 zuwa 2024.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

Wadannan rikice-rikice da aka saba yi shekaru da dama, sun haifar da rikici iri-iri tare da tarwatsa al’umma daga matsugunansu da kuma lalata gonakai da dama.

Jaridar BusinessDay’s, ta yi nazari a kan shawarwarin da kwamtin ya bayar da suka hada da:

1- Kirkiro Da Shirin Zaunar Da Makiyayan Wuri Guda:

Akwai bukatar jawo makiyayan a jiki tare da taimaka musu, domin su rungumi tsarin kiwo na zamani.

Kwamitin ya kuma bayar da shawarar kirkiro da warin kiwo na zamani, musamman domin a zaunar da makiyayan wuri guda.

A cewar kwamtin, ya kamata a fara gyaran kowane wajen kiwon, wanda hakan zai taimaka wajen tattara makiyayan wuri guda.

Ya kuma kamata a samar wa da makiyayan dabarun zamani kan yadda za su rika kula da dabbobinsu.

2- Bunkasa Hada-hadar Kasuwancin Sayar Da Naman Shanu Da Madara:

Kwamitin ya sanar da cewa, ta hanyar samar musu da wajen yin kiwo na zamani, hakan zai taimaka wa makiyayan wajen hada-hadar kasuwancin sayar da naman dabbobinsu da madara da kuma noma abincin Shanunsu da kwamda suke bukata; don ciyar da iyalansu.

A cewar rahoton, za a iya samun nasara akalla a jihohi 20; kuma a cikin shekaru biyar, domin samar da akalla wajen kiwo 5,000; wanda za a ajiye Shanu 50 a cikin kowanne, wanda kuma hakan zai sanya a samar da madara da dabbobin da za a yanka a karkashin shirin.

3 Hada-hadar Kasuwancin Fatar Shanu:

Kwamitin ya bayar da tabbacin cewa, zai magance kalubalen da ake fuskanta a fannin hada-hadar Fatar Shanu; ta yadda za a rika samar da kudaden shiga a fannin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DabobbiGwamnatin Tarayya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wakilin MƊD Ya Nuna Alhini Kan Fashewar Tankar Mai A Jigawa

Next Post

An Bukaci Gwamnain Tarayya Ta Sake Inganta Harkokin Amfanin Gona

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

13 hours ago
Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

2 days ago
Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet
Noma Da Kiwo

Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

2 days ago
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

2 days ago
Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma

1 week ago
Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja
Noma Da Kiwo

Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja

1 week ago
Next Post
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

An Bukaci Gwamnain Tarayya Ta Sake Inganta Harkokin Amfanin Gona

LABARAI MASU NASABA

A Koyi Darasi Daga Tarihi

A Koyi Darasi Daga Tarihi

May 11, 2025
Kada A Bata Ran Mahaifiya

Kada A Bata Ran Mahaifiya

May 11, 2025
Sojoji Sun Cafke Dillalan Sayar Da Bindigu A Filato

Sojoji Sun Cafke Dillalan Sayar Da Bindigu A Filato

May 11, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Akasarin Jama’a Da Cudanyar Cinikayya Tare Da Sin Fiye Da Amurka

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Akasarin Jama’a Da Cudanyar Cinikayya Tare Da Sin Fiye Da Amurka

May 11, 2025
Ɗan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato

Ɗan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato

May 11, 2025
Wang Yi: Ziyarar Shugaba Xi A Rasha Ta Kara Yaukaka Kawance Da Daidaito Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Wang Yi: Ziyarar Shugaba Xi A Rasha Ta Kara Yaukaka Kawance Da Daidaito Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

May 11, 2025
Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Bude Taron Ministoci Na Dandalin Sin Da CELAC Karo Na 4

Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Bude Taron Ministoci Na Dandalin Sin Da CELAC Karo Na 4

May 11, 2025
2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

INEC Na Samun Matsin Lamba Don Kar Ta Yi Wa TNN Rajista — Kakakinta

May 11, 2025
Minista Ya Ƙaddamar Da Yekuwar Wayar da Kan Ɗalibai Kan Kafofin Sadarwa

Minista Ya Ƙaddamar Da Yekuwar Wayar da Kan Ɗalibai Kan Kafofin Sadarwa

May 11, 2025
Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu

Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu

May 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.