ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawarwarin Kwamitin Ma’aikatar Bunkasa Kiwon Dabbobi Ga Gwamnatin Tarayya

by Abubakar Abba
2 years ago
Gwamnatin

A ci gaba da kokarin dakile yawaitar samun rikice-rikice a tsakanin manoma da makiyaya, musamman a Arewacin Nijeriya; a watan Yulin 2024, gwamnatin tarayya ta kaddamar da sabuwar ma’aikatar bunkasa kiwon dabbobi.

Haka zalika, domin dakile kaluabelen da ake fuskanta tare da bunkasa fannin na kiwo; Shugaban Kasa Bola Tinubu, ya kafa kwamitin mutum 23 don bayar da shawarwari ga sabuwar ma’aikatar ta bunkasa kiwon dabbobi.

  • Kashi 67 Cikin 100 Na Ɗaliban Kaduna Sun Samu Nasara A WAEC – Kwamishinan Ilimi
  • Ronaldo Da Messi Ne Kan Gaba A Jerin ‘Yan Wasan Da Suka Fi Karbar Albashi

Ko shakka babu, wannan fanni na kiwo a fadin Nijeriya na matukar bayar da gagarumar gudunmawa, wajen kokarin ci gaba da wadata wannan kasa da abinci.

ADVERTISEMENT

Sai dai, daya daga cikin manyan kalubalen da fannin ke ci gaba da fuskanata a fadin kasar shi ne, yawan samun rikici tsakanin manoma da makiyya, wanda hakan ke ci gaba da shafar ayyukan aikin noma na kasar.

Wani rahoto na Afirka da ke bibiyar hada-hadar kasuwanni da kuma fannin tsaro (SBM) ya bayyana cewa, sama da manoma 1,356 ne suka rasa rayukansu a Arewacin Nijeriya, sakamakon hare-haren ‘yan bindigar daji a tsakanin 2020 zuwa 2024.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Wadannan rikice-rikice da aka saba yi shekaru da dama, sun haifar da rikici iri-iri tare da tarwatsa al’umma daga matsugunansu da kuma lalata gonakai da dama.

Jaridar BusinessDay’s, ta yi nazari a kan shawarwarin da kwamtin ya bayar da suka hada da:

1- Kirkiro Da Shirin Zaunar Da Makiyayan Wuri Guda:

Akwai bukatar jawo makiyayan a jiki tare da taimaka musu, domin su rungumi tsarin kiwo na zamani.

Kwamitin ya kuma bayar da shawarar kirkiro da warin kiwo na zamani, musamman domin a zaunar da makiyayan wuri guda.

A cewar kwamtin, ya kamata a fara gyaran kowane wajen kiwon, wanda hakan zai taimaka wajen tattara makiyayan wuri guda.

Ya kuma kamata a samar wa da makiyayan dabarun zamani kan yadda za su rika kula da dabbobinsu.

2- Bunkasa Hada-hadar Kasuwancin Sayar Da Naman Shanu Da Madara:

Kwamitin ya sanar da cewa, ta hanyar samar musu da wajen yin kiwo na zamani, hakan zai taimaka wa makiyayan wajen hada-hadar kasuwancin sayar da naman dabbobinsu da madara da kuma noma abincin Shanunsu da kwamda suke bukata; don ciyar da iyalansu.

A cewar rahoton, za a iya samun nasara akalla a jihohi 20; kuma a cikin shekaru biyar, domin samar da akalla wajen kiwo 5,000; wanda za a ajiye Shanu 50 a cikin kowanne, wanda kuma hakan zai sanya a samar da madara da dabbobin da za a yanka a karkashin shirin.

3 Hada-hadar Kasuwancin Fatar Shanu:

Kwamitin ya bayar da tabbacin cewa, zai magance kalubalen da ake fuskanta a fannin hada-hadar Fatar Shanu; ta yadda za a rika samar da kudaden shiga a fannin.

Gwamnatin
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

An Bukaci Gwamnain Tarayya Ta Sake Inganta Harkokin Amfanin Gona

LABARAI MASU NASABA

SAW

Ɗabi’un Annabi (SAW) Kan Abubuwa Na Al’adar Rayuwa

September 11, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Shirya Horar Da Malamai 250,000

Gwamnatin Tarayya Ta Shirya Horar Da Malamai 250,000

September 11, 2026
Gwamnatin

Sojoji Sun Ceto Mutane 13 Da ’Yan Bindiga Suka Yi Garkuwa Da Su

September 11, 2026
Taron BRICS: Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya Zuwa Indiya

Taron BRICS: Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya Zuwa Indiya

September 11, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Gwamnan Shekara na 2026 Gwamna Caleb Manasseh Mutfwang

September 11, 2026
Gwamnatin

Idan Atiku Ya Janye, Za Mu Kula Da Shi Bayan Mun Yi Nasara – Kwankwaso

September 11, 2026
Gwamnatin

ASUU Ta Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki Na Ƙasa Gaba Ɗaya

September 11, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwarzon Gwamnan Shekarar 2026 Kwamared Nasir Idris

September 11, 2026
Gwamnatin

Dalilin Da Ya Sa Ba Zan Janye Wa Atiku Ba A Zaɓen 2027 – Peter Obi

September 11, 2026
Farashin Siminti Zai Ragu Idan Farashin Kayan Aiki Ya Sauka – BUA

Gwarzon Shekarar 2026 Abdulsamad Rabiu

September 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.