ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawarwarin Kwamitin Ma’aikatar Bunkasa Kiwon Dabbobi Ga Gwamnatin Tarayya

by Abubakar Abba
2 years ago
Gwamnatin

A ci gaba da kokarin dakile yawaitar samun rikice-rikice a tsakanin manoma da makiyaya, musamman a Arewacin Nijeriya; a watan Yulin 2024, gwamnatin tarayya ta kaddamar da sabuwar ma’aikatar bunkasa kiwon dabbobi.

Haka zalika, domin dakile kaluabelen da ake fuskanta tare da bunkasa fannin na kiwo; Shugaban Kasa Bola Tinubu, ya kafa kwamitin mutum 23 don bayar da shawarwari ga sabuwar ma’aikatar ta bunkasa kiwon dabbobi.

  • Kashi 67 Cikin 100 Na Ɗaliban Kaduna Sun Samu Nasara A WAEC – Kwamishinan Ilimi
  • Ronaldo Da Messi Ne Kan Gaba A Jerin ‘Yan Wasan Da Suka Fi Karbar Albashi

Ko shakka babu, wannan fanni na kiwo a fadin Nijeriya na matukar bayar da gagarumar gudunmawa, wajen kokarin ci gaba da wadata wannan kasa da abinci.

ADVERTISEMENT

Sai dai, daya daga cikin manyan kalubalen da fannin ke ci gaba da fuskanata a fadin kasar shi ne, yawan samun rikici tsakanin manoma da makiyya, wanda hakan ke ci gaba da shafar ayyukan aikin noma na kasar.

Wani rahoto na Afirka da ke bibiyar hada-hadar kasuwanni da kuma fannin tsaro (SBM) ya bayyana cewa, sama da manoma 1,356 ne suka rasa rayukansu a Arewacin Nijeriya, sakamakon hare-haren ‘yan bindigar daji a tsakanin 2020 zuwa 2024.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Wadannan rikice-rikice da aka saba yi shekaru da dama, sun haifar da rikici iri-iri tare da tarwatsa al’umma daga matsugunansu da kuma lalata gonakai da dama.

Jaridar BusinessDay’s, ta yi nazari a kan shawarwarin da kwamtin ya bayar da suka hada da:

1- Kirkiro Da Shirin Zaunar Da Makiyayan Wuri Guda:

Akwai bukatar jawo makiyayan a jiki tare da taimaka musu, domin su rungumi tsarin kiwo na zamani.

Kwamitin ya kuma bayar da shawarar kirkiro da warin kiwo na zamani, musamman domin a zaunar da makiyayan wuri guda.

A cewar kwamtin, ya kamata a fara gyaran kowane wajen kiwon, wanda hakan zai taimaka wajen tattara makiyayan wuri guda.

Ya kuma kamata a samar wa da makiyayan dabarun zamani kan yadda za su rika kula da dabbobinsu.

2- Bunkasa Hada-hadar Kasuwancin Sayar Da Naman Shanu Da Madara:

Kwamitin ya sanar da cewa, ta hanyar samar musu da wajen yin kiwo na zamani, hakan zai taimaka wa makiyayan wajen hada-hadar kasuwancin sayar da naman dabbobinsu da madara da kuma noma abincin Shanunsu da kwamda suke bukata; don ciyar da iyalansu.

A cewar rahoton, za a iya samun nasara akalla a jihohi 20; kuma a cikin shekaru biyar, domin samar da akalla wajen kiwo 5,000; wanda za a ajiye Shanu 50 a cikin kowanne, wanda kuma hakan zai sanya a samar da madara da dabbobin da za a yanka a karkashin shirin.

3 Hada-hadar Kasuwancin Fatar Shanu:

Kwamitin ya bayar da tabbacin cewa, zai magance kalubalen da ake fuskanta a fannin hada-hadar Fatar Shanu; ta yadda za a rika samar da kudaden shiga a fannin.

Gwamnatin
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

An Bukaci Gwamnain Tarayya Ta Sake Inganta Harkokin Amfanin Gona

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.