• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Ahmed Musa Zai Iya Dawowa Da Rigarsa A Super Eagles Kuwa?

by Abba Ibrahim Wada
9 months ago
in Wasanni
0
Shin Ahmed Musa Zai Iya Dawowa Da Rigarsa A Super Eagles Kuwa?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kyaftin din tawagar Super Eagles ta Nijeriya kuma dan wasan da yafi buga wa kasar wasanni a tarihi Ahmed Musa na ci gaba da taka rawar gani a wasannin da yake bugawa tun bayan komawarsa tsohuwar kungiyarshi ta Kano Pillars a watan jiya, Musa ya dade bai buga wa Nijeriya wasa ba duk da cewa shi ne kyaftin din tawagar a halin yanzu sakamakon rashin kungiya na tsawon lokaci.

A gasar cin kofin nahiyoyi da hukumar kwallon kafa ta FIFA ta shirya a shekarar 2013 Musa ya fara buga wa Nijeriya kwallo, inda ya buga dukkan wasannin guda uku da Nijeriya ta buga a gasar yayin da aka fitar da su tun a matakin rukuni.

  • Wasu Matan Arewa Da Suka Yi Fice (3)
  • Tinubu Ya NaÉ—a Sunday Dare a Matsayin Mai Magana Da Yawunsa

Bayan buga dukkan wasannin share fage, an saka sunan Musa a cikin tawagar Nijeriya wadda Stephen Keshi ke jagoranta a wancan lokaci domin buga gasar cin kofin duniya na shekarar 2014, Musa ya zura kwallaye biyu a wasan karshe na rukunin F inda Nijeriya ta yi rashin nasara da ci 3–2 a hannun kasar Argentina.

A watan Oktobar shekarar 2015, bayan ritayar Bincent Enyeama daga buga kwallon kafa, kocin Nijeriya, Sunday Oliseh ya nada Musa a matsayin kyaftin din tawagar sai dai an sauya wannan shawarar a shekarar 2016 yayin da aka nada Mikel John Obi a matsayin kyaftin din tawagar Nijeriya Musa kuma ya koma matsayin mataimakin Kyaftin.

A watan Mayun 2018 an saka shi cikin jerin ‘yan wasa 30 na farko da za su wakilci Nijeriya a gasar cin kofin duniya ta FIFA 2018 a kasar Rasha, Musa ya matukar taka rawar gani a wasansu da kasar Iceland inda ya jefa kwallo biyu a ragar turawan, amma hakan bai hana Nijeriya ficewa daga gasar ba sakamakon rashin nasara da suka yi a hannun Argentina.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

A watan Yunin shekarar 2019 Musa ya zama dan wasa na uku da ya fi taka leda a tarihin tawagar Super Eagles inda ya zarce Nwankwo Kanu, Musa ya zama dan Nijeriya na farko da ya ci fiye da kwallo daya a gasar cin kofin duniya ta FIFA, bayan ya zura kwallaye biyu a ragar Argentina a gasar cin kofin duniya ta FIFA ta 2014.

Musa kuma shi ne dan Nijeriya na farko da ya zura kwallo a gasar cin kofin duniya ta FIFA guda biyu, bayan ya zura kwallaye biyu a ragar Iceland a matakin rukuni na gasar cin kofin duniya ta FIFA 2018, jimilla ya buga wasanni 108, shi ne dan wasan da ya fi buga wa Nijeriya wasa a tarihi.

Wasan karshe da Musa ya buga wa Nijeriya shi ne wanda ya shigo a minti na 94 a fafatawar neman buga gasar kasashen nahiyar Afirika a tsakaninsu da Guinea Bissau ranar 27 ga watan Maris na shekarar 2023,amma ya na cikin ‘yan wasan da suka wakilci Nijeriya a gasar kasashen nahiyar Afirika da aka buga a kasar Kwaddibowa inda aka doke Nijeriya a wasan karshe da ci 1-0,duk da cewar Musa bai buga wasa ko daya ba har aka kammala gasar ya matukar taimaka wa ‘yan wasan Nijeriya da shawarwarin irin nasu na tsoffin kanu a harkar kwallon kafa.

Tun bayan dawowarshi Kano Pillars da take leda Musa ya zura kwallaye uku ya taimaka aka zura biyu a wasanni 4 da ya bugawa Sai Masu Gida, hakan ya sa ake tunanin ya dawo da rigarshi ta tawagar Nijeriya da ya rasa na tsawon lokaci idan ya ci gaba da taka rawar gani.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ahmed MusaRIgaSuper EaglesWasanni
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ban Ji Dadin Abin Da Ya Faru Da Tawagar ‘Super Eagles’ A Libya Ba -Patrice Motsepe

Next Post

Gwamna Sani Ya Samu Karramawa Daga Igbo, Ya Bayar Da Fili Don Gina Kasuwar Kayayyakin Gyara

Related

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

2 hours ago
WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe
Wasanni

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

13 hours ago
Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa
Wasanni

Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa

3 days ago
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu
Wasanni

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu

4 days ago
Oshoala Za Ta Yi Ritaya Daga Buga Wa Nijeriya Ƙwallo
Wasanni

Oshoala Za Ta Yi Ritaya Daga Buga Wa Nijeriya Ƙwallo

5 days ago
Rashford Na Dab Da Komawa Barcelona A Matsayin Aro
Wasanni

Rashford Na Dab Da Komawa Barcelona A Matsayin Aro

5 days ago
Next Post
Gwamna Sani Ya Samu Karramawa Daga Igbo, Ya Bayar Da Fili Don Gina Kasuwar Kayayyakin Gyara

Gwamna Sani Ya Samu Karramawa Daga Igbo, Ya Bayar Da Fili Don Gina Kasuwar Kayayyakin Gyara

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

July 26, 2025
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

July 26, 2025
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

July 26, 2025
Musa

Natijojin Auren Dattijo Ga Budurwa

July 26, 2025
An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

July 26, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

July 26, 2025
Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

July 26, 2025
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.