• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Ahmed Musa Zai Iya Dawowa Da Rigarsa A Super Eagles Kuwa?

by Abba Ibrahim Wada
1 year ago
Musa

Kyaftin din tawagar Super Eagles ta Nijeriya kuma dan wasan da yafi buga wa kasar wasanni a tarihi Ahmed Musa na ci gaba da taka rawar gani a wasannin da yake bugawa tun bayan komawarsa tsohuwar kungiyarshi ta Kano Pillars a watan jiya, Musa ya dade bai buga wa Nijeriya wasa ba duk da cewa shi ne kyaftin din tawagar a halin yanzu sakamakon rashin kungiya na tsawon lokaci.

A gasar cin kofin nahiyoyi da hukumar kwallon kafa ta FIFA ta shirya a shekarar 2013 Musa ya fara buga wa Nijeriya kwallo, inda ya buga dukkan wasannin guda uku da Nijeriya ta buga a gasar yayin da aka fitar da su tun a matakin rukuni.

  • Wasu Matan Arewa Da Suka Yi Fice (3)
  • Tinubu Ya Naɗa Sunday Dare a Matsayin Mai Magana Da Yawunsa

Bayan buga dukkan wasannin share fage, an saka sunan Musa a cikin tawagar Nijeriya wadda Stephen Keshi ke jagoranta a wancan lokaci domin buga gasar cin kofin duniya na shekarar 2014, Musa ya zura kwallaye biyu a wasan karshe na rukunin F inda Nijeriya ta yi rashin nasara da ci 3–2 a hannun kasar Argentina.

A watan Oktobar shekarar 2015, bayan ritayar Bincent Enyeama daga buga kwallon kafa, kocin Nijeriya, Sunday Oliseh ya nada Musa a matsayin kyaftin din tawagar sai dai an sauya wannan shawarar a shekarar 2016 yayin da aka nada Mikel John Obi a matsayin kyaftin din tawagar Nijeriya Musa kuma ya koma matsayin mataimakin Kyaftin.

A watan Mayun 2018 an saka shi cikin jerin ‘yan wasa 30 na farko da za su wakilci Nijeriya a gasar cin kofin duniya ta FIFA 2018 a kasar Rasha, Musa ya matukar taka rawar gani a wasansu da kasar Iceland inda ya jefa kwallo biyu a ragar turawan, amma hakan bai hana Nijeriya ficewa daga gasar ba sakamakon rashin nasara da suka yi a hannun Argentina.

LABARAI MASU NASABA

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

A watan Yunin shekarar 2019 Musa ya zama dan wasa na uku da ya fi taka leda a tarihin tawagar Super Eagles inda ya zarce Nwankwo Kanu, Musa ya zama dan Nijeriya na farko da ya ci fiye da kwallo daya a gasar cin kofin duniya ta FIFA, bayan ya zura kwallaye biyu a ragar Argentina a gasar cin kofin duniya ta FIFA ta 2014.

Musa kuma shi ne dan Nijeriya na farko da ya zura kwallo a gasar cin kofin duniya ta FIFA guda biyu, bayan ya zura kwallaye biyu a ragar Iceland a matakin rukuni na gasar cin kofin duniya ta FIFA 2018, jimilla ya buga wasanni 108, shi ne dan wasan da ya fi buga wa Nijeriya wasa a tarihi.

Wasan karshe da Musa ya buga wa Nijeriya shi ne wanda ya shigo a minti na 94 a fafatawar neman buga gasar kasashen nahiyar Afirika a tsakaninsu da Guinea Bissau ranar 27 ga watan Maris na shekarar 2023,amma ya na cikin ‘yan wasan da suka wakilci Nijeriya a gasar kasashen nahiyar Afirika da aka buga a kasar Kwaddibowa inda aka doke Nijeriya a wasan karshe da ci 1-0,duk da cewar Musa bai buga wasa ko daya ba har aka kammala gasar ya matukar taimaka wa ‘yan wasan Nijeriya da shawarwarin irin nasu na tsoffin kanu a harkar kwallon kafa.

Tun bayan dawowarshi Kano Pillars da take leda Musa ya zura kwallaye uku ya taimaka aka zura biyu a wasanni 4 da ya bugawa Sai Masu Gida, hakan ya sa ake tunanin ya dawo da rigarshi ta tawagar Nijeriya da ya rasa na tsawon lokaci idan ya ci gaba da taka rawar gani.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba
Wasanni

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025
Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara
Wasanni

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

November 2, 2025
Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
Wasanni

Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?

November 2, 2025
Next Post
Gwamna Sani Ya Samu Karramawa Daga Igbo, Ya Bayar Da Fili Don Gina Kasuwar Kayayyakin Gyara

Gwamna Sani Ya Samu Karramawa Daga Igbo, Ya Bayar Da Fili Don Gina Kasuwar Kayayyakin Gyara

LABARAI MASU NASABA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.