• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Ahmed Musa Zai Iya Dawowa Da Rigarsa A Super Eagles Kuwa?

by Abba Ibrahim Wada
10 months ago
in Wasanni
0
Shin Ahmed Musa Zai Iya Dawowa Da Rigarsa A Super Eagles Kuwa?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kyaftin din tawagar Super Eagles ta Nijeriya kuma dan wasan da yafi buga wa kasar wasanni a tarihi Ahmed Musa na ci gaba da taka rawar gani a wasannin da yake bugawa tun bayan komawarsa tsohuwar kungiyarshi ta Kano Pillars a watan jiya, Musa ya dade bai buga wa Nijeriya wasa ba duk da cewa shi ne kyaftin din tawagar a halin yanzu sakamakon rashin kungiya na tsawon lokaci.

A gasar cin kofin nahiyoyi da hukumar kwallon kafa ta FIFA ta shirya a shekarar 2013 Musa ya fara buga wa Nijeriya kwallo, inda ya buga dukkan wasannin guda uku da Nijeriya ta buga a gasar yayin da aka fitar da su tun a matakin rukuni.

  • Wasu Matan Arewa Da Suka Yi Fice (3)
  • Tinubu Ya Naɗa Sunday Dare a Matsayin Mai Magana Da Yawunsa

Bayan buga dukkan wasannin share fage, an saka sunan Musa a cikin tawagar Nijeriya wadda Stephen Keshi ke jagoranta a wancan lokaci domin buga gasar cin kofin duniya na shekarar 2014, Musa ya zura kwallaye biyu a wasan karshe na rukunin F inda Nijeriya ta yi rashin nasara da ci 3–2 a hannun kasar Argentina.

A watan Oktobar shekarar 2015, bayan ritayar Bincent Enyeama daga buga kwallon kafa, kocin Nijeriya, Sunday Oliseh ya nada Musa a matsayin kyaftin din tawagar sai dai an sauya wannan shawarar a shekarar 2016 yayin da aka nada Mikel John Obi a matsayin kyaftin din tawagar Nijeriya Musa kuma ya koma matsayin mataimakin Kyaftin.

A watan Mayun 2018 an saka shi cikin jerin ‘yan wasa 30 na farko da za su wakilci Nijeriya a gasar cin kofin duniya ta FIFA 2018 a kasar Rasha, Musa ya matukar taka rawar gani a wasansu da kasar Iceland inda ya jefa kwallo biyu a ragar turawan, amma hakan bai hana Nijeriya ficewa daga gasar ba sakamakon rashin nasara da suka yi a hannun Argentina.

Labarai Masu Nasaba

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ac Milan Na Tattaunawa Da Bayern Leverkusen Akan Yunkurin Daukar Boniface

A watan Yunin shekarar 2019 Musa ya zama dan wasa na uku da ya fi taka leda a tarihin tawagar Super Eagles inda ya zarce Nwankwo Kanu, Musa ya zama dan Nijeriya na farko da ya ci fiye da kwallo daya a gasar cin kofin duniya ta FIFA, bayan ya zura kwallaye biyu a ragar Argentina a gasar cin kofin duniya ta FIFA ta 2014.

Musa kuma shi ne dan Nijeriya na farko da ya zura kwallo a gasar cin kofin duniya ta FIFA guda biyu, bayan ya zura kwallaye biyu a ragar Iceland a matakin rukuni na gasar cin kofin duniya ta FIFA 2018, jimilla ya buga wasanni 108, shi ne dan wasan da ya fi buga wa Nijeriya wasa a tarihi.

Wasan karshe da Musa ya buga wa Nijeriya shi ne wanda ya shigo a minti na 94 a fafatawar neman buga gasar kasashen nahiyar Afirika a tsakaninsu da Guinea Bissau ranar 27 ga watan Maris na shekarar 2023,amma ya na cikin ‘yan wasan da suka wakilci Nijeriya a gasar kasashen nahiyar Afirika da aka buga a kasar Kwaddibowa inda aka doke Nijeriya a wasan karshe da ci 1-0,duk da cewar Musa bai buga wasa ko daya ba har aka kammala gasar ya matukar taimaka wa ‘yan wasan Nijeriya da shawarwarin irin nasu na tsoffin kanu a harkar kwallon kafa.

Tun bayan dawowarshi Kano Pillars da take leda Musa ya zura kwallaye uku ya taimaka aka zura biyu a wasanni 4 da ya bugawa Sai Masu Gida, hakan ya sa ake tunanin ya dawo da rigarshi ta tawagar Nijeriya da ya rasa na tsawon lokaci idan ya ci gaba da taka rawar gani.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ahmed MusaRIgaSuper EaglesWasanni
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ban Ji Dadin Abin Da Ya Faru Da Tawagar ‘Super Eagles’ A Libya Ba -Patrice Motsepe

Next Post

Gwamna Sani Ya Samu Karramawa Daga Igbo, Ya Bayar Da Fili Don Gina Kasuwar Kayayyakin Gyara

Related

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City
Wasanni

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

15 hours ago
Boniface
Wasanni

Ac Milan Na Tattaunawa Da Bayern Leverkusen Akan Yunkurin Daukar Boniface

2 days ago
Ronaldo Ya Samu Kyakkyawar Tarba A Hong Kong
Wasanni

Ronaldo Ya Samu Kyakkyawar Tarba A Hong Kong

4 days ago
Yadda Arsenal Ta Doke Manchester United Da Ci 1-0
Wasanni

Yadda Arsenal Ta Doke Manchester United Da Ci 1-0

6 days ago
Waye Zai Lashe Kyautar Ballon d’Or?
Wasanni

Waye Zai Lashe Kyautar Ballon d’Or?

6 days ago
Me Ya Sa Ciwon ACL Ya Zama Barazana Ga ‘Yan Wasan Kwallo?
Wasanni

Me Ya Sa Ciwon ACL Ya Zama Barazana Ga ‘Yan Wasan Kwallo?

6 days ago
Next Post
Gwamna Sani Ya Samu Karramawa Daga Igbo, Ya Bayar Da Fili Don Gina Kasuwar Kayayyakin Gyara

Gwamna Sani Ya Samu Karramawa Daga Igbo, Ya Bayar Da Fili Don Gina Kasuwar Kayayyakin Gyara

LABARAI MASU NASABA

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

August 23, 2025
2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

August 23, 2025
Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

August 23, 2025
Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

August 23, 2025
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.