• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Kawo Karshen Yi Wa Mata Kaciya Nan Da 2030

by Leadership Hausa
2 years ago
in Rahotonni
0
Shirin Kawo Karshen Yi Wa Mata Kaciya Nan Da 2030
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kididdigar Majalisar Dinkin Duniya ta tabbatar da cewa, mata fiye da miliyan 200 a fadin duniya suka fuskanci yi masu kaciya abin da ake kira da ‘Female Genital Mutilation’ (FGM) a turance.

Rahoto ya nuna cewa a wannan shekarar ta 2023 akwai mata fiye da Miliyan 4.2 da ke fuskantar yiwuwar a yi masu kaciyar.

  • Za A Kira Taruka Biyu A Farkon Wata Mai Zuwa
  • Sin: Ya Zama Wajibi A Binciki Fashewar Bututun Nord Stream 

Haka kuma majalisar ta kiyasata cewa, katsewar zuwa makaranta da matsalar cutar korona ta haifar zai iya jefa wasu matan fiye da miliyan 2 suka fada komar masu yi wa mata kaciya a cikin shekaru masu zuwa in har ba a dauki kwakkwaran matakin da ya kamata ba.

Nijeriya ce kasa ta uku a duniya da ke tattare da mafi yawan mata a da aka taba yi wa kaciya, kamar yadda cibiyar majalisar dinkin duniya ta UNICEF ta bayyana a rahotonta. Hukumar ta kuma kara da cewa, yi wa mata kaciya yana kara karuwa a Nijeriya musamman ma a kan ‘yan mata masu shekaru 0 zuwa 14 a duniya. Abin takaicin kuma shi ne alkalumman sun tashi daga kashi 16.9 a shekarar 2013 zuwa kashi 19.2 a shekarar 2018, ‘‘Wannan abin damuwa ne matuka,”. UNICEF ta bayyana cewa, mata fiye miliyan 68 a fadin duniya suke fuskantar yiwuwar a yi masu kaciya a tsakanin shekarar 2015 zuwa shekarar 2030.

A shekarar 2012, babban zauren majalisar dinkin duniya (UNGA) ya bayyana ranar 6 ga watan Fabrairu na kowace shekara a mastayin ranar yekuwa da yaki da yi wa mata kaciya a duk fadi duniya, ranar da za a kara jaddada aniyar yaki da wannan mummunan al’adar da kokarin kawar da ita gaba daya.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

Taken bikin wannan shekarar shi ne “Hada Hannu Da Maza da Matasa Don Kawo Karshen Yi Wa Mata Kaciya”. An kaddamar da shirin ne tare da hadin gwiwar UNFPA-UNICEF da hadadiyyar Kungiyar yaki da yi wa mata kaciya ta Duniya.

An kirkiro da shirin ne a shekarar 2022 don bada gudummawa ga al’ummar duniya don kawar da yi wa mata kaciya a fadinn duniya nan da shekarar 2030. Abin jin dadi a nan shi ne wannan shiri yana da alaka da tsarin cimma muradun karni mai lamba ta 5.3, wanda ke neman a daina kawo abubuwan da za su iya cutar da al’umma daga nan  zuwa shekarar 2030. Bangaren shirin ya bayar da karfi ne a kan kasashen da suka fi yawan wadanda ake ganin za a yi wa kaciyar a ‘yan shekaru masu zuwa.

Yi wa mata kaciya ya yi kamari a Nijeriya inda ake samun fiye da mata Miliyan 19.9 da aka yi wa kaciyar. Lamarin na Nijeriya yana kara samun wurin musammman ma tsakanin mata masu shekara 15 zuwa 49 amma ya yi kasa daga kashi 25 a shekarar 2013 zuwa kashi 20 a shekarar 2018, binciken ya kuma nuna yadda lamarin ya sake karuwa a tsakanin yara ‘yan shekara 0 zuwa 14 daga kashi 16.9 zuwa kashi 19.2 a daidai wannan lokacin da ake magana. An gano cewa kashi 86 na matan da aka yi wa kaciyar ana yi masu ne a tsakanin shekara 5 yayin da kashi 8 kuma an yi masu ne a tsakanin shekara 5 zuwa 14.

Tuni wakilin cibiyar majalisar dinkin duniya ta UNICEF a Nijeriya, Peter Hawkins ya bayyana cewa, yi wa mata kaciya bashi da wani tasiri a bangaren lafiya. Bayani daga kafafaen yada labarai ya nuna cewa, an yi wa mata kaciyar ne a yankin kudu maso yammancin kasar nan in da ake da kashi 35 yayin da kuma ake da karancin wadanda ake yi wa kaciyar a yankin Arewa maso gabas inda suke da kashi 6 kacal.

Jihohi biyar da aka fi yi wa mata kaciya a Nijeriya sune: Ebonyi, Ekiti, Imo, Osun da Oyo. Inda fiye da ‘yan mata da mata Miliyan 3 suka samu kansu da kaciya a tsakanin shekara 5 kamar yadda kididdiga ya nuna a shekarar 2022.

Ana yi wa matan kaciyar ne a mastayin karya dokokin hakkinsu na yara da mata kamar yadda dokokin kare hakkin yara ya nuna, haka kuma karyar hakkinsu ne na abin da ya shafi sirrinsu da kuma hakkinsu na kasancewa cikin ‘yanci, hanyoyin da ke bi wajen yi wa matan kaciya yana kai wa ga mutuwar wasu a sassan Nijeriya.

Bayani daga wani littafi da wata sharariyar mai fafuftukar yaki da yi wa mata kaciya mai suna Frances A. Althaus, ta sanar da yadda a shekarar 1984 suka yi taron a garin Dakar ta kasar Senegal, inda suka tattauana lamarin yi wa mata kaciya da sauran miyagun al’adu da ke cutar da rayuwar mata a sassan Afrika, daga nan suka kafa wata karkaffar kwamitin wanda zai yi aikin wayar da kan al’umma aka wannan mummuna al’ada.

An kuma bayyani a cikin littafin inda aka bayyana yadda kwamitin ya jagoranci kafa rassan kwamitoci a kasashe fiye 20 a sassan Afirika sun kuma bayar da gaggarumin gudumawa wajen yaki da wannan mummunar al’adar na yi wa mata kaciya, sun bayar da karfi a kan bayyana irin yadda yi wa mata kaciya yake cutar da rayuwar mata, an kuma samu babbar nasara a wannan yakin. Wanna gwagwamaryar ya haifar da wasu kananan kungiyoyi da suka yi fice a yakin da aka fuskanta na yi wa mata kaciya, sun kuma hada da ‘NOW’ a Nijeriya da kuma ‘Mandalaeo Ya Wanawake’ a kasar Kenya da ‘New Woman’ a kasar Egypt.

Littafin ya kuma fito da nasarar da aka samu a babban taro karo na 4 da aka yi a kasa Chana a shekarar 1995 inda aka samu nasarar ta yadda taron ya ayyana haramci ga wannan al’aada na yi wa mata kaciya a duniya, an kuma ayyana al’adar a matsayin tarzoma ga mata kuma karya hakkinsu ne.

Haka kuma bincike ya nuna cewa, ana wannan al’ada na yi wa mata kaciya a wasu kasase na yankin Asiya da latin Amurka abin takaici kuma shi ne wasu ‘yan gudun hijira dake zaune a yankin Turai ta Yamma, Arewacin Amurka da kasar Australia da New Zealand suna ci gaba da yi wa yaransu mata kaciya a boye.

A yayin da ranar Majalisar Dinkin Duniya ta ware na yaki da yi wa mata kaciya yake kara karatowa, a mastayinmu na jarida muna kara kira ga gwamantin tarayya ta gaggauta sanya ido a kan wuraren da ake samun rahoton karuwar yi wa mata kaciya, bai kamata a tilastawa kowa fadawa irin wannan mummunan al’adar ba. Yakamata a samar da wata karkarfar kwamiti domin fadakar da al’umma a kan bukatar kawo karshen wannan mummunan al’ada. Yakamata mu hada hannu mu fattaki al’adar yi wa mata kaciya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KaciyaMata
ShareTweetSendShare
Previous Post

Za A Kira Taruka Biyu A Farkon Wata Mai Zuwa

Next Post

Arewa An Sha Mu Mun Warke, Bai Kamata Mu Koma Gidan Jiya Ba – Matasan Arewa A Kudu

Related

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

4 weeks ago
Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar
Rahotonni

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

1 month ago
An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya
Rahotonni

An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya

1 month ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Rahotonni

Amurka Ta Sayi Kayayyakin Nijeriya Na Dala Miliyan 643 A Wata 2 – Rahoto

1 month ago
Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi
Rahotonni

Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi

1 month ago
Tinubu
Manyan Labarai

Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027

2 months ago
Next Post
Arewa An Sha Mu Mun Warke, Bai Kamata Mu Koma Gidan Jiya Ba – Matasan Arewa A Kudu

Arewa An Sha Mu Mun Warke, Bai Kamata Mu Koma Gidan Jiya Ba – Matasan Arewa A Kudu

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.