• English
  • Business News
Saturday, May 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Sake Fasalin Aikin Rundunar ‘Yansandan Nijeriya (Ra’yinmu)

by Sulaiman
3 years ago
in Rahotonni
0
'Yansandan Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsaron rayuka da dukiyoyin al’umma na daya daga cikin ginshinkin tabbatar da cigaban dukkan al’umma a ko ina a fadin duniyar nan. Haka kuma ‘yansanda ne wadanda aka dora wa nauyin samar da tsaron cikin gida a kowacce kasa a fadin duniya. Rundunar ‘yansandan Nijeriya da Turawan Mulkin Mallaka suka kafa ta gamu da manyan matsaloli tun daga farkon kafata da burin tabbatar da cikakken tsaro ga al’ummar Nijeriya.

Wannan halin da rundunar ta samu kanta ya haifar da sauye-sauye da sake fasali da kokarin kwaskwarima a lokutta daban-daban amma har zuwa yuanzu ba a kai ga samun nasarar da ake bukata ba. Wadannan na daga cikin dalilan da ya sa al’umma suka kasa gamsuwa da yadda ‘yansanda ke gudanar da ayyukansu ba kuma tare da la’akari da dinbin matsalolin da rundunar ke fuskanta ba.

Mambobin Jam’iyyar NNPP 700 Sun Koma Jam’iyyar Labour A Adamawa

Ba tare da kokwanto ba, yadda muke ganin tsananin gurbacewar rundunar ‘yansandan mu yana nuna irin yadda al’ummar mu ta gurbace ne. A Nijeriya an kafa rundunar ‘yansanda ne don kare muradun shugabannin mulkin mallaka na Turawa, sun kafa rundunar ne bayan da suka fahimci cewa, in har suka kafa wata runduna ta musamman zai taimaka musu tatsar albarkatun ma’adanai a sassan kasar nan.

A bayyane yake cin hanci da rashawa ya mamaye al’amurra a Nijeriya amma kuma tsananin cin hanci da rashawar da ake samu a rundunar ‘yansandan yana faruwa ne kai tsaye a kan yadda gwamnati da masu ruwa da tsaki suka dauki tafiyar da harkokin rundunar ‘yansandan. Abin dariya ne in har ‘yan Nijeriya za su yi tunanin cewa, ‘yansanda za su zama kamar malaiku da zarar sun sanya kayan sarki na zama ‘yansanda.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

A ra’ayinmu, bai kamata ma a zargi ‘yansanda da karbar na goro a kan hanyoyinmu ba daga ‘yan Nijeriya bayan muna sane da cewa, hatta kayan aikin dake jikinsu sune suke saya da kansu tare da dukkan kayan sarkin da suke amfani dasu a fagen gudanar da aikinsu, wadannan kadai sun isa su ingiza su karbar cin hanci da rashawa don kokarin inganta ayyukansu da rayuwarsu, amma anan ba wai muna halasta karbar cin-hancin da suke yi ba ne.
Duk da kokarin da aka yi na sake fasalin rundunar ‘yansandan Nijeriya a lokutta daban-daban, har yanzu rundunar na nan kamar yadda aka santa a shekarun baya, haka na faruwa ne saboda kokarin da aka yi baya kaiwa ga can kasa inda matsalar take. Shirin sake fasalin rundunar da aka yi a baya yana faruwa ne don biyan bukatun masu mulki a lokacin tare da kuma huce takaici da haushin a bin da suke fuskanta.

Shirin sake fasali na baya-bayan nan an yi shi ne a shekarar 1999, amma ba a kai ga cimma manufar aiwatar da sake fasalin ba, wadanda suka hada da bukatar kare rayuwa da dukiyoyin al’ummar Nijeriya ba tare da nuna banbanci ba, sai dai shirin ya gamu da cikas na rashin cikakken kayan aiki da kuma rashin hadin kai daga bangarori daban-daban.

A shekarar 1989, Admiral Murtala Nyako ya jagoranci kwamitin sake fasalin rundunar ‘yansanda amma a duk tsawon wadannan shekarun ba a kai ga cimma wani abin a zo a gani ba na samar da ingantaciyyar rundunar ‘yansanda da al’ummar Nijeriya za su yi alfahari da ita. Bayan shekara biyu kuma, Farfesa Tekena Tamuno ya mika rahonsa na sake fasalin rundunar ‘yansanda amma har yanzu ba a kai ga yin amfani da su ba.

A shekarar 2006 kuma Shugaban Kasa Olusegun Obasanjo ya kafa wani kwamitin karkashin jagorancin tsohon shugaban rundunar ‘yansadan Nijeriya, Muhammad Danmadami. A shekarar 2008 kuma an kafa sabon kwamiti wanda shima tsohon shugaban rundunar ‘yan sandan Nijeriya, Muhammadu Dikko Yusuf ya jagoranta, ya kuma samu nasarar mika rahoto tattare da shawarwari 125 na yadda za a inganta aikin ‘yansanda amma har zuwa yanzu ba a kai ga aiwatar da daya daga cikin shawarwarin da suka mika ba.

Haka kuma rahoton kwamitin sake fasalin ‘yansanda da shirin ‘Bision 2010’ ya samar bai samu karbuwa ba a hannun mahukunta. Shima kwamitin da Parry Osayande ya jagoranta a shekarar 2012 bai kai labari ba.
Cin zarafin mutane daga ‘yansanda ba abu ba ne da ya kebu ga Nijeriya, abu ne daya game duk duniya. Amma irin yadda ake sanya ido da kuma yadda ake hukunta wadanda aka samu da laifi shi ne yake banbanta, kamar yadda ake samu a kasashe kamar su Kanada Birtaniya wadanda suka yi fice wajen kare hakkin biladam. Irin rashin hukunta ‘yansanda masu cin zarafin al’umma a Nijeriya yake tayar da hankalin al’umma a dukkan lokutta har yake haifar da zanga-zanga kamar yadda muka gani a lokacin ‘EndSARS, wanda hakan kuma yana shafar mutuncin rundunar. A kan haka muke bayar da shawarar samar da rundunar ‘yansanda mai cikakken kayan aiki na zamani tare da biyansu cikakken hakokinsu ta yadda hankalinsu zai fita daga aikata cin hanci da rashawa.

Tabbas lokaci ya yi da za a sake fasalin rundunar ‘yansandan Nijeriya ta yadda za ta yi daidai da tsarin mulkin dimokradiyya, a tabbatar da sun kawo karshen cin zarafin al’umma, musamnman masu karamin karfi.

Yakamata a yi wa tsarin mulki kwaskwarima ta yadda za a iya dauka da korar shugaban rundunar ‘yansanda kai tsaye ba kamar yadda lamarin yake a halin yanzu ba inda sai abin da shugaban kasa ya ga dama, dole ya zamana majalisar kasa ta sanya hannun a kan zabo wanda zai zama shugaban rundunar ‘yansanda su kuma sanya hannu wajen korarsa in ya gaza gudanar da aikinsa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Tattauna Tsakanin Shugaba Xi Na Sin Da Biden Na Amurka

Next Post

Yajin Aikin ASUU: Ba Za Mu Sarara Ba Har Sai Gwamnati Ta Magance – NLC

Related

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

3 weeks ago
Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar
Rahotonni

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

4 weeks ago
An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya
Rahotonni

An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya

4 weeks ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Rahotonni

Amurka Ta Sayi Kayayyakin Nijeriya Na Dala Miliyan 643 A Wata 2 – Rahoto

4 weeks ago
Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi
Rahotonni

Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi

4 weeks ago
Tinubu
Manyan Labarai

Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027

2 months ago
Next Post
NLC

Yajin Aikin ASUU: Ba Za Mu Sarara Ba Har Sai Gwamnati Ta Magance – NLC

LABARAI MASU NASABA

Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

May 10, 2025
Mambobin APC Sun Buƙaci EFCC Ta Sake Buɗe Binciken Matawalle

Mambobin APC Sun Buƙaci EFCC Ta Sake Buɗe Binciken Matawalle

May 10, 2025
Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya

Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya

May 10, 2025
Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

May 9, 2025
Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

May 9, 2025
Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

May 9, 2025
Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

May 9, 2025
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.