• English
  • Business News
Thursday, September 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban APC Ga Mambobinta: Mu Haɗa Ƙarfi Da Ƙarfe Don Samun Nasarar Jam’iyyar

by yahuzajere
3 years ago
in Siyasa
0
Shugaban APC Ga Mambobinta: Mu Haɗa Ƙarfi Da Ƙarfe Don Samun Nasarar Jam’iyyar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa, Sanata Abdullahi Adamu, ya nemi duk wani ɗan jam’iyyar ya bayar da tasa gudunmawar ta yadda za a haɗa ƙarfi da ƙarfe don ganin jam’iyyar ta samu nasara a zaɓen 2023 da ke ƙaratowa.

  • Zaben APC: Ɗaya Daga Cikin Deliget Daga Jihar Jigawa Ya Rasu A Abuja

 

Ya nunar wa mambobin APC cewa dole su kimtsa cikin muddin ana da buƙatar jam’iyyar ta ci gaba da riƙe madafun iko a 2023, yana mai cewa buƙatar jam’iyyar na gagidaba da ta kowane mamba ko ƙungiya.

Adamu ya ce sakamakon taron APC da ya gudana ranar Talata shi zai tantance nasarar da jam’iyyar za ta samu a 2023.
Shugaban jam’iyyar ya bayyana haka ne a wajen Babban Taron APC a Talatar da ta gabata a dandalin Eagle Sƙuare da ke Anuja.

Haka nan, Adamu ya yi gargaɗin cewa dole jam’iyyar ta maganace rikicin cikin gidan da take fama da shi don tabbatar a nasarar jam’iyyarsu a zaɓe mai zuwa.
Ya ce kada a sanya son-kai cikin lamarin neman tsayar da wanda zai yi wa jam’iyya takarar Shugaban ƙasa.
Don haka ya jaddada buƙatar da ke akwai a haɗa kai da fahimtar juna da sassantawa a tsakanin ɗaukacin mambobin jam’iyyar.

Labarai Masu Nasaba

Ba Abin Da Zai Hana Tinubu Sake Lashe Zaɓe A 2027 – Jigon APC

Gwamnan Bauchi Ya Gargaɗi Magoya Bayan Wike A PDP

  • Abdullahi Adamu: Babu Wani Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa Da Aka Haramta Wa Takara A APC

A nasa ɓangaren, Shugaban Kwamitin shirya taron kuma Gwamnan Jihar Kebbi, Sanata Atiku Bagudu, ya ce ‘yan takara 23 ne za su fafata a zaɓen fitar da ɗan takarar.

Ya ƙara da cewa, daliget uku-uku daga kowace ƙaramar hukuma a tsakanin ƙananan hukumomi 774 da ake da su a faɗin ƙasa za a bari su kaɗa ƙuri’a daidai da tanadin Dokar Zaɓe ta 2022 da aka yi wa gyara.

Mahalarta taron sun haɗa da: Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari a uwargidansa, Aishat da Mataimakin Shugaban Kasa, Yemi Osinbajo da Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Ahmad Lawan da sauransu.

Har ila yau akwai sauran mambobin jam’iyyar ta APC waɗanda suka yi fitar farin ɗango daga jihohinsu domin halartar babban taron jam’iyyar wanda aka kammala lami lafiya cikin nasara.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Nasarar Tinubu A Takarar Shugaban Kasa: Na Dauki Mataki Na Gaba – Lawan

Next Post

Atiku Zai Yi Wa Tinubu Kwab Ɗaya, Don Ba Tsaransa Ba Ne, In Ji PDP

Related

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Siyasa

Ba Abin Da Zai Hana Tinubu Sake Lashe Zaɓe A 2027 – Jigon APC

19 hours ago
2027: Fastocin Takarar Shugaban Ƙasa Na Gwamnan Bauchi Sun Bayyana
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Gargaɗi Magoya Bayan Wike A PDP

1 day ago
Ina Da Yaƙinin Tinubu Ne Zai Lashe Zaɓen 2027 — Wike
Siyasa

Ina Da Yaƙinin Tinubu Ne Zai Lashe Zaɓen 2027 — Wike

3 days ago
Ɗaukar Nauyin Ƴan Ta’addan Da Suka Farmake Mu A Kaduna Aka Yi – El-Rufai
Siyasa

Ɗaukar Nauyin Ƴan Ta’addan Da Suka Farmake Mu A Kaduna Aka Yi – El-Rufai

3 days ago
Ɗan Majalisa Zai Saya Wa Makinde Fam Ɗin Takarar Shugaban Ƙasa A 2027
Siyasa

Ɗan Majalisa Zai Saya Wa Makinde Fam Ɗin Takarar Shugaban Ƙasa A 2027

4 days ago
Peter Obi Ya Caccaki Gwamnati Kan Ƙarin Kuɗin Fasfo
Siyasa

Peter Obi Ya Caccaki Gwamnati Kan Ƙarin Kuɗin Fasfo

6 days ago
Next Post
Atiku Zai Yi Wa Tinubu Kwab Ɗaya, Don Ba Tsaransa Ba Ne, In Ji PDP

Atiku Zai Yi Wa Tinubu Kwab Ɗaya, Don Ba Tsaransa Ba Ne, In Ji PDP

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Zai Ƙaddamar Da Masana’antar Battirin Lithium A Nasarawa

Tinubu Zai Ƙaddamar Da Masana’antar Battirin Lithium A Nasarawa

September 4, 2025
Ƴan Siyasar Arewa Na Rigima Da Juna, Tinubu Na Murna — Jibrin

Ƴan Siyasar Arewa Na Rigima Da Juna, Tinubu Na Murna — Jibrin

September 4, 2025
Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

September 3, 2025
Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

September 3, 2025
Tinubu Ya Naɗa Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano

Tinubu Ya Naɗa Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano

September 3, 2025
Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 

Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 

September 3, 2025
Kasar Sin Ta Shirya Bikin Gala Na Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yakin Turjiyar Jama’ar Kasar Da Yaki Da Mulkin Danniya A Duniya

Kasar Sin Ta Shirya Bikin Gala Na Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yakin Turjiyar Jama’ar Kasar Da Yaki Da Mulkin Danniya A Duniya

September 3, 2025
Lookman

Kofin Duniya: Lookman Da Dessers Sun Isa Sansanin Super Eagles A Uyo

September 3, 2025
Firaministan Senegal: Yadda Sinawa Ke Girmama Tarihi Da Kiyaye Labarun Abubuwan Da Suka Faru Da Su Na Da Matukar Burgewa 

Firaministan Senegal: Yadda Sinawa Ke Girmama Tarihi Da Kiyaye Labarun Abubuwan Da Suka Faru Da Su Na Da Matukar Burgewa 

September 3, 2025
Hatsarin Jiragen Ruwa

Mutane 29 Sun Rasa Rayukansu A Wani Hatsarin Jirgin Ruwa A Jihar Neja

September 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.