• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban APC Ga Mambobinta: Mu Haɗa Ƙarfi Da Ƙarfe Don Samun Nasarar Jam’iyyar

by yahuzajere
3 years ago
APC

Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa, Sanata Abdullahi Adamu, ya nemi duk wani ɗan jam’iyyar ya bayar da tasa gudunmawar ta yadda za a haɗa ƙarfi da ƙarfe don ganin jam’iyyar ta samu nasara a zaɓen 2023 da ke ƙaratowa.

  • Zaben APC: Ɗaya Daga Cikin Deliget Daga Jihar Jigawa Ya Rasu A Abuja

 

Ya nunar wa mambobin APC cewa dole su kimtsa cikin muddin ana da buƙatar jam’iyyar ta ci gaba da riƙe madafun iko a 2023, yana mai cewa buƙatar jam’iyyar na gagidaba da ta kowane mamba ko ƙungiya.

Adamu ya ce sakamakon taron APC da ya gudana ranar Talata shi zai tantance nasarar da jam’iyyar za ta samu a 2023.
Shugaban jam’iyyar ya bayyana haka ne a wajen Babban Taron APC a Talatar da ta gabata a dandalin Eagle Sƙuare da ke Anuja.

Haka nan, Adamu ya yi gargaɗin cewa dole jam’iyyar ta maganace rikicin cikin gidan da take fama da shi don tabbatar a nasarar jam’iyyarsu a zaɓe mai zuwa.
Ya ce kada a sanya son-kai cikin lamarin neman tsayar da wanda zai yi wa jam’iyya takarar Shugaban ƙasa.
Don haka ya jaddada buƙatar da ke akwai a haɗa kai da fahimtar juna da sassantawa a tsakanin ɗaukacin mambobin jam’iyyar.

LABARAI MASU NASABA

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

  • Abdullahi Adamu: Babu Wani Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa Da Aka Haramta Wa Takara A APC

A nasa ɓangaren, Shugaban Kwamitin shirya taron kuma Gwamnan Jihar Kebbi, Sanata Atiku Bagudu, ya ce ‘yan takara 23 ne za su fafata a zaɓen fitar da ɗan takarar.

Ya ƙara da cewa, daliget uku-uku daga kowace ƙaramar hukuma a tsakanin ƙananan hukumomi 774 da ake da su a faɗin ƙasa za a bari su kaɗa ƙuri’a daidai da tanadin Dokar Zaɓe ta 2022 da aka yi wa gyara.

Mahalarta taron sun haɗa da: Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari a uwargidansa, Aishat da Mataimakin Shugaban Kasa, Yemi Osinbajo da Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Ahmad Lawan da sauransu.

Har ila yau akwai sauran mambobin jam’iyyar ta APC waɗanda suka yi fitar farin ɗango daga jihohinsu domin halartar babban taron jam’iyyar wanda aka kammala lami lafiya cikin nasara.

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato
Manyan Labarai

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
APC
Manyan Labarai

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta
Siyasa

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

October 24, 2025
Next Post
Atiku Zai Yi Wa Tinubu Kwab Ɗaya, Don Ba Tsaransa Ba Ne, In Ji PDP

Atiku Zai Yi Wa Tinubu Kwab Ɗaya, Don Ba Tsaransa Ba Ne, In Ji PDP

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

October 29, 2025
Asuu

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

October 29, 2025
Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

October 29, 2025
Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

October 29, 2025
An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

October 29, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Bukatar Amso Bashin Dala Biliyan 2.34 A Kasuwar Jari Ta Duniya

October 29, 2025
An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

October 29, 2025
Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

October 29, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

October 29, 2025
COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

October 29, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.