ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban APC Ga Mambobinta: Mu Haɗa Ƙarfi Da Ƙarfe Don Samun Nasarar Jam’iyyar

by yahuzajere
4 years ago
APC

Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa, Sanata Abdullahi Adamu, ya nemi duk wani ɗan jam’iyyar ya bayar da tasa gudunmawar ta yadda za a haɗa ƙarfi da ƙarfe don ganin jam’iyyar ta samu nasara a zaɓen 2023 da ke ƙaratowa.

  • Zaben APC: Ɗaya Daga Cikin Deliget Daga Jihar Jigawa Ya Rasu A Abuja

 

Ya nunar wa mambobin APC cewa dole su kimtsa cikin muddin ana da buƙatar jam’iyyar ta ci gaba da riƙe madafun iko a 2023, yana mai cewa buƙatar jam’iyyar na gagidaba da ta kowane mamba ko ƙungiya.

ADVERTISEMENT

Adamu ya ce sakamakon taron APC da ya gudana ranar Talata shi zai tantance nasarar da jam’iyyar za ta samu a 2023.
Shugaban jam’iyyar ya bayyana haka ne a wajen Babban Taron APC a Talatar da ta gabata a dandalin Eagle Sƙuare da ke Anuja.

Haka nan, Adamu ya yi gargaɗin cewa dole jam’iyyar ta maganace rikicin cikin gidan da take fama da shi don tabbatar a nasarar jam’iyyarsu a zaɓe mai zuwa.
Ya ce kada a sanya son-kai cikin lamarin neman tsayar da wanda zai yi wa jam’iyya takarar Shugaban ƙasa.
Don haka ya jaddada buƙatar da ke akwai a haɗa kai da fahimtar juna da sassantawa a tsakanin ɗaukacin mambobin jam’iyyar.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

  • Abdullahi Adamu: Babu Wani Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa Da Aka Haramta Wa Takara A APC

A nasa ɓangaren, Shugaban Kwamitin shirya taron kuma Gwamnan Jihar Kebbi, Sanata Atiku Bagudu, ya ce ‘yan takara 23 ne za su fafata a zaɓen fitar da ɗan takarar.

Ya ƙara da cewa, daliget uku-uku daga kowace ƙaramar hukuma a tsakanin ƙananan hukumomi 774 da ake da su a faɗin ƙasa za a bari su kaɗa ƙuri’a daidai da tanadin Dokar Zaɓe ta 2022 da aka yi wa gyara.

Mahalarta taron sun haɗa da: Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari a uwargidansa, Aishat da Mataimakin Shugaban Kasa, Yemi Osinbajo da Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Ahmad Lawan da sauransu.

Har ila yau akwai sauran mambobin jam’iyyar ta APC waɗanda suka yi fitar farin ɗango daga jihohinsu domin halartar babban taron jam’iyyar wanda aka kammala lami lafiya cikin nasara.

 

APC
yahuzajere
+ postsBio
  • yahuzajere
    Da Kujerar Mulki Gara Zaman Lafiyar Kano
  • yahuzajere
    Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya
  • yahuzajere
    Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
  • yahuzajere
    Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin

MASU ALAKA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
APC
Siyasa

Muna Da Yan Takarar Gwamna A Jihohi 28 Don Shiga Zaben 2027

September 6, 2026
Next Post
Atiku Zai Yi Wa Tinubu Kwab Ɗaya, Don Ba Tsaransa Ba Ne, In Ji PDP

Atiku Zai Yi Wa Tinubu Kwab Ɗaya, Don Ba Tsaransa Ba Ne, In Ji PDP

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.