• English
  • Business News
Sunday, July 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban NIS Ya Yi Gargaɗin Biyan Kuɗin Fasfo Da Tsabar Kuɗi A Hannu

…Yayin Da Aka Buɗe Cibiyar Ingantaccen Fasfo Na Yankin Kudu Maso Kudu

by yahuzajere
3 years ago
in Rahotonni
0
Shugaban NIS Ya Yi Gargaɗin Biyan Kuɗin Fasfo Da Tsabar Kuɗi A Hannu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa, CGI Isah Jere Idris ya yi kira ga ‘Yan Nijeriya masu neman fasfo su tabbatar da cewa sun yi amfani da shafin intanet na hukumar wajen neman fasfo da biyan kuɗi ta nan, ga duk wani fasfo da suke so.

  • Yunkurin Tsige Shugaba Buhari Abin Takaici Ne Matuka —Abdullahi Adamu

Ya yi kiran ne a Fatakwal a yayin ƙaddamar da Babbar Cibiyar Samar da Ingantaccen Fasfo Ta Zamani domin kawar da fasfo na tsohon ya yi a yankin kudu-maso-kudu. Ya bayyana cewa hukumar ta mayar da matakan neman fasfon zuwa shafin intanet ne domin daƙile duk wani nau’i na hada-hadar tsabar kuɗi a hannu wanda ta hakan ne ake ‘yan ƙumbiya-ƙumbiya. Don haka ya buƙaci masu neman fasfon su rungumi amfani da intanet, kana ya yi gargaɗin cewa mahukuntan hukumar za su hukunta duk wanda aka kama yana karɓar tsabar kuɗi a hannu a kan neman fasfo.

fasfo
Jerin manyan bakin da suka halarci kaddamar da cibiyar

Sanarwar da mai Magana da yawun hukumar ta NIS, ACI Amos Okpu ya aike wa LEADERSHIP Hausa ta ƙara da cewa, shugaban hukumar ya yi ƙarin haske kamar haka; “Cibiyar Ingantaccen Fasfo da muke ƙaddamarwa a yau a nan, ɗaya ce daga cikin sauye-sauye da gyaran fuska da muke yi na ƙara inganta sha’anin fasfo ga ‘yan ƙasa. Bisa ƙaddamarwar ta yau, dukkan ofisoshin fasfo na Jihohin Akwa Ibom, Bayelsa, Kuros Riba da Ribas sun sauya daga masu bayar da tsohon fasfo zuwa sabo mafi inganci da aka samar,” in ji shi.

Bisa ƙaddamar da cibiyar dai, dukkan wani mai buƙatar fasfo a cikin waɗannan jihohin, ana sa rai ya cike takardar nema ta shafin intanet a direshin passport.immigration.gov.ng, tare da biyan kuɗi ta nan da kuma neman a ba shi ranar da zai zo a ɗauki bayanansa ta na’ura. Kuma ana buƙatar ya je ofishin fasfon ne kawai a ranar da aka sanya masa.

fasfo
CGI Isah Idris Jere yayin da ake tarbarsa a Fatakwal

Tun da farko, Ministan Cikin Gida, Ogbeni Rauf Aregbesola ya bayyana cewa ayyukan fasfo suna da matuƙar muhimmanci da ya kamata a ƙara mayar da hankali a kai sosai.

Labarai Masu Nasaba

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

“Fasfo shi ne takarda ta shaidar ƙasa mafi muhimmanci da ya kamata ɗan ƙasa ya mallaka. Ba wai kawai yana bai wa mai shi damar tsallakawa zuwa ƙasashen waje ba ne, yana kuma nuna asalin ɗan ƙasa ne da ‘yancin da yake da shi. Saboda haka, ba wai kawai matakan samun fasfon ya kamata su zama sahihai bisa gaskiya da riƙon amana ba, ya dace waɗanda ke aikin samar da shi su kula sosai da yin abubuwa kamar yadda suka dace,” in ji shi.

Ministan ya yaba wa NIS bisa sauye-sauyen ci gaba da take aiwatarwa a sashen fasfo daga tsohon yayi da ake rubutawa da hannu zuwa na zamani da ake sarrafawa ta na’ura, a yanzu kuma zuwa ingantacce da ake yayi a duniya. Ya nunar da cewa ƙoƙarin da NIS take yi na ganin fasfon Nijeriya ya cika ƙa’idar inganci da Hukumar Sufurin Jiragen Sama ta Duniya (ICAO) ta sharɗanta ba kawai abin yabawa ba ne amma gagarumin ci gaba ne abin alfahari.

Ya ƙara da cewa, sabon ingantaccen fasfon an samar da shi ne da fasahar zamani da ake ya yi a duniya wanda aka ƙawata shi da abubuwa na sirri guda 25 fiye da na wanda ake amfani da shi a yanzu. Sannan takardunsa suna da inganci ta yadda ruwa ba ya lalatawa kuma ‘yan damfara masu buga na jabu ba za su iya kwatanta irin sa ba.

fasfo
Mazaunin manyan baki a wurin taron

Aregbesola ya sake nanata ƙudirin ma’aikatarsa ta ƙin amincewa da cuwa-cuwa da ka iya kawo tarnaƙi ga sauye-sauyen da ake yi inda ya yi gargaɗin cewa duk wani jami’i da aka kama da hannu a ciki zai fuskanci fushin doka. Ya yi kira ga masu neman fasfo su riƙa amfani da shafin intanet wurin gabatar da buƙatunsu tare da tabbatar da bayar da bayanai na gaskiya game da kawunansu domin komai ya tafi daidai-wa-daida.

A halin da ake ciki kuma, Gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Ezenwo Wike wanda mataimakiyarsa, Dakta Ipalibo Banigo ta wakilta a taron, ya yaba wa NIS bisa zaɓar Fatakwal a matsayin Babbar Cibiyar Samar da Fasfo ta yankin kudu-maso-kudu.

Ya ba da tabbacin cewa, jihar ta ƙudiri aniyar bayar da goyon baya ga dukkan hukumomin gwamnati da ke jihar, kana ya yi kiran ɗorewar sauye-sauye da garambawul da ake yi a kan batun fasfo domin ya inganta sosai.

Cikin manyan al’amuran da suka gudana a taron akwai ƙaddamar da cibiyar wacce za ta karaɗe jihohin kudu-maso-kudu da Ministan Cikin Gida Aregbesola ya yi bisa rakiyar mataimakiyar gwamnan Ribas.

Manyan jami’an gwamnati na jihar da na tarayya ciki har da wakilan sojoji da sauran hukumomin tsaro da ke jihar sun halarci taron.

  • https://www.capitalpost.ng/2022/07/nis-rolls-out-enhanced-epassport-for-nigeria-citizens-in-us/

Bisa ƙaddamar da katafariyar cibiyar fasfon dai, yankin kudu-maso-kudu ya bi sahun takwarorinsa na kudu-maso-yamma da wasu cibiyoyi da ke Amurka da Birtaniya wajen sauyawa daga bayar da fasfo na tsohon yayi zuwa sabo.

 

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Me Ya Jawo Saurin Ci Gaban Cinikin Waje Na Kasar Sin?

Next Post

Rundunar PLA Tana Ci Gaba Da Atisayen Hadin Gwiwa A Kewayen Taiwan

Related

jam'iyyu
Rahotonni

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

3 weeks ago
fasfo
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

4 weeks ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

4 weeks ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

1 month ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

1 month ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

1 month ago
Next Post
Rundunar PLA Tana Ci Gaba Da Atisayen Hadin Gwiwa A Kewayen Taiwan

Rundunar PLA Tana Ci Gaba Da Atisayen Hadin Gwiwa A Kewayen Taiwan

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

July 5, 2025
Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

July 5, 2025
‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

July 5, 2025
Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

July 5, 2025
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

July 5, 2025
Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

July 5, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

July 5, 2025
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

July 5, 2025
Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

July 5, 2025
Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.