• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabancin Majalisa: Abin Da Ya Sa APC Ke Kokarin Nada Na Hannun Damar Tinubu

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Lafiyata Kalau, Na Shirya Tsaf Don Shugabantar Nijeriya —Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Alamu masu karfi sun bayyana a karshen makon da ya gabata cewa zababben shugaban kasa, Bola Tinubu na nuna sha’awarsa kan wanda zai zama shugaban majalisar dattawa sakamakon yadda hakan ke da matukar muhimmanci, mu-samman la’akari da rashin tabbas sakamakon koke-koke daban-daban da ke kalubalantar nasararsa a kotun sauraron rarrakin zabe.

Manyan ‘yan takarar shugaban majalisar dattawan sun hada da tsohon shugaban marasa rinjaye na majalisar dattawa kuma tsohon ministan harkokin Neja Delta, Sanata Godswill Akpabio da tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa, Mista Ad-ams Oshiomhole da babban mai tsawatarwa na majalisar dattawa, Sanata Orji Uzor Kalu da Gwamnan Jihar Ebonyi mai barin gado, Mista Dabe Umahi, na ci gaba da fafatawa a neman zaman shugabancin majalisar dattawa.

  • ‘Daurin Dankwali Na Musamman’
  • Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

An bayyana cewa a daidai lokacin da Oshiomhole da Umahi suka dage kan cewa za su tsaya takara, akwai yunkurin yin gyaran fuska ga dokokin majalisar dattawa domin ba wa ‘yan majalisar dattijai damar tsayawa takarar manyan mukamai, saboda share wa tsohon gwamnan Jihar Edo hanya wanda ake kyautata zaton Tinubu ya fi son sa.

Wannan shi ne karo na farko da Oshiomhole da kuma Umahi za su kasance a zau-ren majalisar dattawa.

Rahotanni sun bayyana cewa jam’iyyar APC ta sadaukar da takarar shugabancin jamalisar dattawa ga yankin kudu maso kudu, yayin da yankin arewa maso yam-ma zai samar da mataimaki, dokokin majalisar dattawa sun hana fitowar sanata a karo na farko ya nemi takarar shugabancin majalisar.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

A karkashin dokokin majalisar dattawa na yanzu, ba su cancanci tsayawa takara ba, saboda dadadden sanata ne kawai ya cancanci ya rike babban mukami a zau-ren majalisar.

Sai dai wata majiya mai tushe ta bayyana cewa idan har Oshiomhole ya tsaya takara, gwamnonin APC za su iya watsi da Umahi.
An bayyana cewa fargabar yiwuwar sakamakon koke-koke da aka shigar kan na-sarar da Tinubu ya samu a kotun sauraron kararrakin zaben shugaban kasa ya sanya zababben shugaban kasar da makusantansa neman dan takarar da za su amince da shi.

Wasu majiyoyi da dama sun shaida cewa bangaren Tinubu ya neman wani amintaccen abokinsa ya zama shugaban majalisar dattawa ta yadda idan har aka soke zaben shugaban kasa da aka yi a ranar 25 ga watan Fabrairu, abokinsa zai kasance a matsayin shugaban riko na tsawon kwanaki 90.

“Akwai fargabar cewa kotun za ta iya soke zaben. Idan kotun ta soke zaben, za a bukaci shugaban majalisar dattawa ya ci gaba da rikon kwarya na tsawon kwa-naki 90,” wata majiya take shaida wa manema labarai hakan.

A halin da ake ciki kuma, kwamitin kungiyar gwamnonin APC da aka kafa ya zau-na kan batun bin tsarin karba-karba wajen raba mukaman shugabanci a majalisar dokokin kasar nan, wanda ya mika rahoto ga zababben shugaban kasa dangane da matsayin jam’iyyar APC.

Rahotannin sun bayyana cewa Tinubu ya bukaci a kafa kwamitin ne a lokacin da wasu gwamnonin suka ki amincewa da wani shiri na bai-daya da nufin karkatar da mukaman shugabannin majalisar dokokin kasar ga wasu mutane.

A cewar wata majiya, gwamnonin da ke adawa da hakan sun yi barazanar cewa za su tunkari shugabannin jam’iyyar idan har ba a bi ka’ida ba wajen zaben shugabannin majalisar tarayya.

Majiyar ta ci gaba da cewa: “Zababben shugaban kasa ya kusa kammala tsare-tsarensa na fitar da mutumin da zai shugabanci majalisar dattawa har sai da gwamnonin suka shiga tsakani suka kuma sha alwashin za su yi wa jam’iyyar aiki wajen goyon mutum na biyu a zauren majalisar a yayin kaddamar da majalisar dokokin kasar karo na 10.

“Zababben shugaban kasa wanda ba ya son ya fara gwamnatinsa da rikicin da zai iya hana shi aiki, ya bukaci kungiyar gwamnonin ta kafa wani kwamiti da zai sa-mar da tsarin da kowa zai amince da shi kan batun karba-karba wanda shugaban-nin jam’iyyar za su tattauna.”

Wata majiya da ke kusa da daya daga cikin gwamnonin, ta shaida cewa za a mika rahoton ne ranar Litinin.

Tinubu ya ki amincewa da shirin da wasu jiga-jigan sanatoci daga shiyyar Kudu maso yamma suka yi na ba shi goyon bayan ajandarsu na yin amfani da tsarin karba-karba wajen samar da shugabannin majalisa ta 10.

Wasu majiyoyi da dama sun tabbatar da cewa sanatocin da ke daukar kansu a matsayin na hannun daman Tinubu, sun yi ta aiki ba dare ba rana domin karkatar da shi kan bin tsarin karba-karba wajen zaben shugabannin majalisar dattawa na 10 ga zababbun Sanatoci biyu.

Majiyar wacce ta fito daga yankin kudu maso yamma, ta bayyana fargabar cewa matsayar da sanatocin ke yi na iya kawo cikas ga tsarin karba-karba na jam’iyyar APC a zauren majalisar a ranar da za a rantsar da sabbin shugabannin, domin akwai yiwuwar ya sake tsayawa takara karo na biyu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: majalisaSanatociTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsakanin Mace Mai Bala’in Son Kudi Da Mai Yawo, Da Namiji Mai Kulle Ko Mako, Wanne Ne Dama-dama?

Next Post

Sin Ta Yi Nasarar Gwajin Sake Amfani Da Na’urar Zirga-Zirgar Sararin Samaniya

Related

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

2 weeks ago
Tinubu
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

2 weeks ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

2 weeks ago
Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba
Tambarin Dimokuradiyya

Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya

3 weeks ago
2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara 
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Babu Dan Takarar Da Zai Iya Cin Zabe Ba Tare Da Goyon Bayan Arewa Ba – Baba Ahmed

3 weeks ago
arewa
Tambarin Dimokuradiyya

Kawunan Shugabannin Arewa Sun Rabu Kan Siyasar 2027

3 weeks ago
Next Post
Sin Ta Yi Nasarar Gwajin Sake Amfani Da Na’urar Zirga-Zirgar Sararin Samaniya

Sin Ta Yi Nasarar Gwajin Sake Amfani Da Na’urar Zirga-Zirgar Sararin Samaniya

LABARAI MASU NASABA

JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

May 14, 2025
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

May 14, 2025
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.