• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabancin Majalisa Ta 10: Ko ‘Yan Mowar APC Za Su Kai Bantensu?

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Shugabancin Majalisa Ta 10: Ko ‘Yan Mowar APC Za Su Kai Bantensu?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar APC da zababben shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu sun tabbatar da Sanata Godswill Akpabio a matsayin shugaban majalisar dattawa ta 10 da kuma Sanata Jibril Barau a matsayin mataimakinsa. 

Hakazalika, sun amince da Hon. Tajudeen Abbas a matsayin shugaban majalisar wakilai da kuma Hon. Benjamin Kalu a matsayin mataimakinsa. Sai dai wannan zabi, kamar yadda wasu dama suka yi hasashe, ya gamu da tutsun sauran masu neman shugabancin majalisun daga APC da wajenta. Yanzu haka masu nema irin su Hon. Wase, Ado Doguwa, Batare da sauransu sun ci gaba da matsa kaimi kan muradunsu.

  • Gwamnati Za Ta Kashe Biliyan 22.44 Kan Ciyar Da Fursunoni A 2023
  • Sin Ta Bukaci Jami’ar Ofishin Jakadancin Canada A Shanghai Da Ta Bar Kasar

Kafin mu duba irin tsingayen da ‘yan mowar APC da zababben shugaban kasa a kan shugabancin majalisun za su tsallaka kafin su kai bantensu, shin wane ne Sanata Akpabio? Ya yi murabus a gwamnatin Buhari a matsayin ministan kula da harkokin Neja Delta, haka nan tsohon gwamnan Jihar Akwa Ibom daga shekarar 2007 zuwa 2015. Lokacin da yake gwamnan Akwa Ibom ya kawo sauye-sauye na zamani a cikin jihar, inda nan take al’amura suka sauya a wannan jihar, wanda ya kirkiro tsarin karatu kyauta ga kowani yaro dan asalin Jihar Akwa Ibom ba tare da nuna bambancin siyasa, addini ko kabilanci ba. Ya samar da harkokin kiwon lafiya kyauta ga mata masu juna biyu da yara da kuma inganta ababen more rayuwa a cikin jihar.

Sakamakon irin namijin kokari da ya yi a matsayin gwamnan Jihar Akwa Ibom ne al’ummar mazabarsa ta Ikot Ekpene suka zabe shi a matsayin dan majalisar dattawa, inda ya zama shugaban marasa rinjaye a zauren majalisar dattawa a karkashin tsohuwar jam’iyyarsa.

A matsayinsa na shugaban marasa rinjaye a majalisar dattawa, Akpabio ya nuna kishin kasa kan yadda ya tafiyar da al’amuran gwamnati da fuskantar ‘yan adawa. Wadanda suka yi tsammanin zai gudanar da makauniyar siyasa ga ‘yan adawa sun ji takaici da salon shugabancinsa. Ya samu damar daidaita matsayinsa na jagoran adawa da bukatar tallafa wa duk wani abu da zai amfanar da ‘yan Nijeriya da jam’iyya mai mulki ta kawo a zauren majalisar dattawa.

Labarai Masu Nasaba

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

Bisa la’akari da dimbin nasarorin da ya samu wanda ba a saba gani ba, a shekarar 2019, Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya nada Sanata Akpabio a matsayin ministan ma’aikatan kula da harkokin Neja Delta (NDDC). Aikinsa na farko shi ne, tabbatar da cewa yankin ya kasance cikin kwanciyar hankali, yayin da masu ruwa da tsaki suka sha kai ruwa rana kan hanyoyin da yake bi wajen ciyar da yankin gaba.

A matsayinsa na minista mai kula da ma’aikatan harkokin Neja Delta ya yi duk mai yuwuwa wajen yin abin da ya dace don ganin ya cika buri da muradin al’ummar yankin ta hanyar gudanar da ayyuka masu inganci. Hakan ne ya sa aka fara gudanar da binciken kwakwaf kan ayyukan ma’aikatan wanda aka fara da wanda aka kammala. Tuni dai aka mika rahoton ga gwamnatin tarayya, inda ake sa ran za ta yi amfani da rahoton wajen tsara sabon tsari ga kwamitin da za a kaddamar.

A matsayinsa na ministan ma’aikatar Neja Delta, Akpabio ya samu goyon bayan Shugaba Buhari, ya ba wa yankin wasu sabbin gine-gine 13 da benaye 8 da aka kammala a matsayin hedkwatar ma’aikatan NDDC da aka kammala har ta fara aiki, ya gudanar da ayyuka 52 a yankin Neja Delta, sama da hanyoyi 77 ne ake shirin kaddamar da su a yankin, an kaddamar da rukunun gidajen ‘yansanda a Fatakwal. Sama da gadaje 1000 da ma’aikatar ta gina a jami’ar Uyo ta Jihar Akwa Ibom, yayin da aikin samar da wutar lantarki a Ilaje Ese-Odo da ke Jihar Ondo ke gab da kammalawa kuma ya fara aiki.

Sauran ayyukan da aka kammala sun hada da cibiyar koyon sana’a da ke Agadagba a Jihar Ondo mai gine-gine 38. An samar da jiragen kasa na dakon mai guda 7 na wanda aka kafa a karkashin ruwan Welding Facility a Ibeno a Jihar Akwa Ibom, kamfanin rogo mai sarrafa amfanin gona a Usugbene Irrua a Jihar Edo, cibiyar kiwon lafiya da ke Unguwar Amauzari a karamar hukumar Isiala Mbano ta Jihar Imo, cibiyar lafiya a Odi da ke karamar hukumar Kolokuma/Opokuma a Jihar Bayelsa, aikin gyaran filayeye a karamar hukumar Nsit Attai ta Jihar Akwa Ibom, cibiyar lafiya a Eworkpe da ke Emede ta karamar hukumar Isoko ta kudu a Jihar Delta, aikin gyaran hanyar Umudike-Umueze-Umuoyere kashi na daya a Jihar Ribas, aikin gyaran samar da ruwan sha a Ikot Effiong da ke kauyen  Effiong a gundumar Akasoko Clan ta karamar hukumar Akpabuyo a Jihr Kuros Ribas, aikin gina rijiyoyin burtsatse a Ndulu-Amaoba da kuma aikin samar da ruwan sha a karamar hukumar Ikwuano ta Jihar Abiya.

Shi kuwa Sanata Barau Jibrin, gogaggen dan siyasa ne wanda ya kasance mamba a majalisa ta tara daga Jihar Kano, an dai sake zabensa a karo na 3 a jere a majalisar dattawa, kuma ya kasance dan majalisar dattawa mafi matsayi a jamhuriyar tarayyar Nijeriya, ya kasance kan gaba wajen neman wanda zai zama shugaban majalisar dattawa ta 10.

Barau Jibrin, ya yi aure kuma Allah ya albarkace shi da ‘ya’ya da dama, wanda ya kasance dan asalin garin Kabo da ke karamar hukumar Kabo a Jihar Kano.

A shekarar 2017 ne kungiyar ‘yan jaridu ta Nijeriya ta bai wa Sanata Jibrin lambar yabo ta gwarzon sanatan Arewa. Bisa la’akari da irin gudunmawar da ya bayar wajen samar da zaman lafiya, hadin kai, da ci gaban kasa. A watan Oktoba na shekarar 2022, Sanata Barau Jibrin ya samu kyautar lambar girmamawa ta kasa wanda Shugaban kasar Muhammadu Buhari ya ba shi.

A lokacin zaben ‘yan majalisar tarayya na 1999, sha’awar jama’arsa ne ya zaburar da shi har ya tsaya takarar dan majalisar wakilai ta tarayya a mazabar Tarauni ta Jihar Kano, wanda ya lashe zaben.

A 2015, Sanata Barau ya sake tsayawa takarar har ya lashe zabe a matsayin sanata mai wakiltar Kano ta arewa karkashin tutar jam’iyyar APC. A 2019 da 2023 kuwa, ya sake dawowa zauren majalisar dattawa.

A lokacin da yake matsayin dan majalisar wakilai, ya kasance shugaban kwamitin rabo. Ya kuma kasance mamba a kwamitin kula da wutan lantarki na majalisar wakilai.

A matsayinsa na sanata, an zabe shi a matsayin mataimakin shugaban kwamitin kula da harkokin man fetur na majalisar dattawa, inda daga baya ya zama shugaban kwamitin gaba daya.

A ranar 20 ga watan Yulin 2016, shugaban majalisar dattawa na 8, Dakta Bukola Saraki ya sake fasalin shugabancin kwamitocin majalisar dattawa, wanda aka nada Sanata Barau a matsayin shugaban kwamitin kula da harkokin manyan makarantu.

Bugu da kari, a matsayinsa na dan majalisar dattawa ya taba zama mamba a kwamitocin Neja Delta, masana’antu, sufurin kasa, da kuma rabon kudade, kuma yana taka muhimmiyar rawa a matsayinsa na sakataren kungiyar sanatocin Arewa. A ranar 3 ga Oktobar 2019, ya kawo kudirin doka kan kwalejin kimiyya da fasaha ta Kabo.

Kasancewar Barau a matsayin dan majalisar wakilai da kuma fitaccen sanatan tarayyar Nijeriya, ya kawo sabon sabon salo ga mazabar Tarauni da kuma sanatan Kano ta Arewa, kamar yadda jama’a suka tabbatar sun fuskanci irin wakilci na gaskiya a zauren majalisar tarayyar Nijeriya.

A zaben shugaban kasa na 2023 da aka kammala, Sanata Barau yana Jam’iyyar APC da zababben shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu sun tabbatar da Sanata Godswill Akpabio a matsayin shugaban majalisar dattawa ta 10 da kuma Sanata Jibril Barau a matsayin mataimakinsa.

Hakazalika, sun amince da Hon. Tajudeen Abbas a matsayin shugaban majalisar wakilai da kuma Hon. Benjamin Kalu a matsayin mataimakinsa. Sai dai wannan zabi, kamar yadda wasu dama suka yi hasashe, ya gamu da tutsun sauran masu neman shugabancin majalisun daga APC da wajenta. Yanzu haka masu nema irin su Hon. Wase, Ado Doguwa, Batare da sauransu sun ci gaba da matsa kaimi kan muradunsu.

Kafin mu duba irin tsingayen da ‘yan mowar APC da zababben shugaban kasa a kan shugabancin majalisun za su tsallaka kafin su kai bantensu, shin wane ne Sanata Akpabio? Ya yi murabus a gwamnatin Buhari a matsayin ministan kula da harkokin Neja Delta, haka nan tsohon gwamnan Jihar Akwa Ibom daga shekarar 2007 zuwa 2015. Lokacin da yake gwamnan Akwa Ibom ya kawo sauye-sauye na zamani a cikin jihar, inda nan take al’amura suka sauya a wannan jihar, wanda ya kirkiro tsarin karatu kyauta ga kowani yaro dan asalin Jihar Akwa Ibom ba tare da nuna bambancin siyasa, addini ko kabilanci ba. Ya samar da harkokin kiwon lafiya kyauta ga mata masu juna biyu da yara da kuma inganta ababen more rayuwa a cikin jihar.

Sakamakon irin namijin kokari da ya yi a matsayin gwamnan Jihar Akwa Ibom ne al’ummar mazabarsa ta Ikot Ekpene suka zabe shi a matsayin dan majalisar dattawa, inda ya zama shugaban marasa rinjaye a zauren majalisar dattawa a karkashin tsohuwar jam’iyyarsa.

A matsayinsa na shugaban marasa rinjaye a majalisar dattawa, Akpabio ya nuna kishin kasa kan yadda ya tafiyar da al’amuran gwamnati da fuskantar ‘yan adawa. Wadanda suka yi tsammanin zai gudanar da makauniyar siyasa ga ‘yan adawa sun ji takaici da salon shugabancinsa. Ya samu damar daidaita matsayinsa na jagoran adawa da bukatar tallafa wa duk wani abu da zai amfanar da ‘yan Nijeriya da jam’iyya mai mulki ta kawo a zauren majalisar dattawa.

Bisa la’akari da dimbin nasarorin da ya samu wanda ba a saba gani ba, a shekarar 2019, Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya nada Sanata Akpabio a matsayin ministan ma’aikatan kula da harkokin Neja Delta (NDDC). Aikinsa na farko shi ne, tabbatar da cewa yankin ya kasance cikin kwanciyar hankali, yayin da masu ruwa da tsaki suka sha kai ruwa rana kan hanyoyin da yake bi wajen ciyar da yankin gaba.

A matsayinsa na minista mai kula da ma’aikatan harkokin Neja Delta ya yi duk mai yuwuwa wajen yin abin da ya dace don ganin ya cika buri da muradin al’ummar yankin ta hanyar gudanar da ayyuka masu inganci. Hakan ne ya sa aka fara gudanar da binciken kwakwaf kan ayyukan ma’aikatan wanda aka fara da wanda aka kammala. Tuni dai aka mika rahoton ga gwamnatin tarayya, inda ake sa ran za ta yi amfani da rahoton wajen tsara sabon tsari ga kwamitin da za a kaddamar.

A matsayinsa na ministan ma’aikatar Neja Delta, Akpabio ya samu goyon bayan Shugaba Buhari, ya ba wa yankin wasu sabbin gine-gine 13 da benaye 8 da aka kammala a matsayin hedkwatar ma’aikatan NDDC da aka kammala har ta fara aiki, ya gudanar da ayyuka 52 a yankin Neja Delta, sama da hanyoyi 77 ne ake shirin kaddamar da su a yankin, an kaddamar da rukunun gidajen ‘yansanda a Fatakwal. Sama da gadaje 1000 da ma’aikatar ta gina a jami’ar Uyo ta Jihar Akwa Ibom, yayin da aikin samar da wutar lantarki a Ilaje Ese-Odo da ke Jihar Ondo ke gab da kammalawa kuma ya fara aiki.

Sauran ayyukan da aka kammala sun hada da cibiyar koyon sana’a da ke Agadagba a Jihar Ondo mai gine-gine 38. An samar da jiragen kasa na dakon mai guda 7 na wanda aka kafa a karkashin ruwan Welding Facility a Ibeno a Jihar Akwa Ibom, kamfanin rogo mai sarrafa amfanin gona a Usugbene Irrua a Jihar Edo, cibiyar kiwon lafiya da ke Unguwar Amauzari a karamar hukumar Isiala Mbano ta Jihar Imo, cibiyar lafiya a Odi da ke karamar hukumar Kolokuma/Opokuma a Jihar Bayelsa, aikin gyaran filayeye a karamar hukumar Nsit Attai ta Jihar Akwa Ibom, cibiyar lafiya a Eworkpe da ke Emede ta karamar hukumar Isoko ta kudu a Jihar Delta, aikin gyaran hanyar Umudike-Umueze-Umuoyere kashi na daya a Jihar Ribas, aikin gyaran samar da ruwan sha a Ikot Effiong da ke kauyen  Effiong a gundumar Akasoko Clan ta karamar hukumar Akpabuyo a Jihr Kuros Ribas, aikin gina rijiyoyin burtsatse a Ndulu-Amaoba da kuma aikin samar da ruwan sha a karamar hukumar Ikwuano ta Jihar Abiya.

Shi kuwa Sanata Barau Jibrin, gogaggen dan siyasa ne wanda ya kasance mamba a majalisa ta tara daga Jihar Kano, an dai sake zabensa a karo na 3 a jere a majalisar dattawa, kuma ya kasance dan majalisar dattawa mafi matsayi a jamhuriyar tarayyar Nijeriya, ya kasance kan gaba wajen neman wanda zai zama shugaban majalisar dattawa ta 10.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Majalisa Ta 10Shuganacin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Za Mu Lamunci Dauki-Dora A Shugabancin Majalisa Ba —Kawu Sumaila

Next Post

Xi Ya Yi Rangadi A Shijiazhuang Dake Lardin Hebei

Related

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

1 week ago
Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa
Tambarin Dimokuradiyya

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

1 week ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

4 weeks ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

4 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

4 weeks ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

1 month ago
Next Post
Xi Ya Yi Rangadi A Shijiazhuang Dake Lardin Hebei

Xi Ya Yi Rangadi A Shijiazhuang Dake Lardin Hebei

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.