• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabannin Togo Da Cote d’Ivoire Sun Gana Da Ministan Harkokin Wajen Sin

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Shugabannin Togo Da Cote d’Ivoire Sun Gana Da Ministan Harkokin Wajen Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasar Togo Faure Essozimna Gnassingbé da shugaban kasar Cote d’Ivoire Alassane Ouattara sun gana da mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta Sin kuma ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi dake ziyara a kasashensu jiya Laraba a birnin Lome da kuma a birnin Abidjan.

A yayin ganawar, shugaba Faure Essozimna Gnassingbé na Togo ya yi karin haske kan dangantakar dake tsakanin Togo da Sin da ma hadin gwiwarsu, ya ce bisa dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka, kasar Togo da sauran kasashen Afirka, sun samu babban ci gaba a fannin samar da kayayyakin more rayuwa. Ya kara da cewa, tattalin arzikin Afirka ya kara bunkasa, an kuma tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a nahiyar Afirka, har ma al’ummun nahiyar na smaun Moriya. Wadannan suna da nasaba da tallafin da kasar Sin ta dade tana samarwa. Togo ta yaba da yadda kasar Sin ke tabbatar da adalci a duniya, da nuna adawa da tsoma baki a harkokin cikin gidan Afirka, da taka rawar da ta kamata wajen samun ci gaban Afirka cikin lumana.

  • Kotu Ta Bai Wa Emefiele Damar Yin Tafiye-tafiye A Nijeriya
  • NIS Shiyyar Arewa Maso Gabas Ta Kaddamar Da “Operation Tsaron Iyaka”

A nasa bangare, minista Wang Yi ya isar da gaisuwar shugaban kasar Sin Xi Jinping ga shugaban kasar Togo, inda ya bayyana cewa, zumuntan dake tsakanin Sin da Togo, ya zama abin misali ga hadin gwiwar dake tsakanin kasashe masu tasowa. Sin za ta kara yin hadin gwiwa tare da kasar Togo kan manyan tsare-tsare, da nuna goyon baya ga kasar Togo wajen samun bunkasuwa mai dorewa. Ya ce, karni na 21, karni ne na farfado da kasashe masu tasowa. Kasar Sin za ta ci gaba da tsayawa tsayin daka tare da kasashen Afirka, da taimakawa kasashen Afirka wajen gaggauta samun ci gaba kansu, da sa kaimi da inganta hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afirka, da kara amfana da sakamakon hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afirka, don samun moriyar Togo da kasashen Afirka.

A wannan rana kuma, Wang Yi ya yi tattaunawa tare da firaministar kasar Togo Mme Victoire Sidémeho Tomégah Dogbé da kuma ministan harkokin wajen kasar Togo Robert Dussey.

Togo
Sannan a yayin ganawar shugaban kasar Cote d’Ivoire Alassane Ouattara da Mr. Wang Yi, Alassane Ouattara ya yaba da hadin gwiwar dake tsakanin kasashensa da Sin, inda ya bayyana cewa kasar Sin ta zama babbar abokiyar cinikayya mafi girma da kuma tushen zuba jari ga kasar ta Cote d’Ivoire.

Labarai Masu Nasaba

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Cote d’Ivoire za ta ci gaba da ba da fifiko wajen raya dangantakar dake tsakaninta da kasar Sin, a cewar shugaban.

Ya kuma jaddada cewa kasar Sin daya ce tak a duniya, kuma Taiwan wani yanki ne na kasar Sin.

Wang ya ce, bangaren kasar Sin na matukar yabawa irin goyon bayan da Cote d’Ivoire ke baiwa kasar Sin wajen kiyaye dinkuwar kasar da cikakkun yankunanta. Ya kuma bayyana cewa, kasar Sin a shirye take ta sa kaimi ga inganta hadin gwiwar moriyar juna tsakaninta da Cote d’Ivoire.

Ya ci gaba da cewa, kasar Sin a shirye take ta yi aiki tare da kasashen Afirka, wajen gano ingantattun hanyoyin da suka dace da yanayin da kasashen ke ciki, da kiyaye ‘yancin kansu, da samar da ci gaba da wadata tare, ta yadda za a cimma nasarar zamanantarwa tare.

Wang ya kuma tattauna da ministan harkokin wajen Cote d’Ivoire a ranar Larabar.

Kasar Cote d’Ivoire ita ce kasa ta karshe a Afirka na ziyarar farko da ministan harkokin wajen kasar Sin ya kai a ketare a bana. Wang ya kuma ziyarci Masar da Tunisiya da kuma Togo yayin ziyarar da ta fara a ranar Asabar. (Zainab Zhang, Yahaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Shugaban kasar Cote d’IvoireShugaban kasar TogoWang yi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsaro: Gwamnatin Zamfara Ta Haramta Wa Sarakuna Bada Izinin Hakar Ma’adanai

Next Post

Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Mai Dorewa Da Inganci Na Kara Ba Da Gudummawa Ga Ci Gaban Duniya

Related

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne
Daga Birnin Sin

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

42 minutes ago
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu
Daga Birnin Sin

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

2 hours ago
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”
Daga Birnin Sin

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

3 hours ago
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

4 hours ago
Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”
Daga Birnin Sin

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

5 hours ago
Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet

6 hours ago
Next Post
Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Mai Dorewa Da Inganci Na Kara Ba Da Gudummawa Ga Ci Gaban Duniya

Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Mai Dorewa Da Inganci Na Kara Ba Da Gudummawa Ga Ci Gaban Duniya

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

September 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

September 15, 2025
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

September 15, 2025
Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

September 15, 2025
Neja

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.