• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabannin Togo Da Cote d’Ivoire Sun Gana Da Ministan Harkokin Wajen Sin

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Shugabannin Togo Da Cote d’Ivoire Sun Gana Da Ministan Harkokin Wajen Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasar Togo Faure Essozimna Gnassingbé da shugaban kasar Cote d’Ivoire Alassane Ouattara sun gana da mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta Sin kuma ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi dake ziyara a kasashensu jiya Laraba a birnin Lome da kuma a birnin Abidjan.

A yayin ganawar, shugaba Faure Essozimna Gnassingbé na Togo ya yi karin haske kan dangantakar dake tsakanin Togo da Sin da ma hadin gwiwarsu, ya ce bisa dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka, kasar Togo da sauran kasashen Afirka, sun samu babban ci gaba a fannin samar da kayayyakin more rayuwa. Ya kara da cewa, tattalin arzikin Afirka ya kara bunkasa, an kuma tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a nahiyar Afirka, har ma al’ummun nahiyar na smaun Moriya. Wadannan suna da nasaba da tallafin da kasar Sin ta dade tana samarwa. Togo ta yaba da yadda kasar Sin ke tabbatar da adalci a duniya, da nuna adawa da tsoma baki a harkokin cikin gidan Afirka, da taka rawar da ta kamata wajen samun ci gaban Afirka cikin lumana.

  • Kotu Ta Bai Wa Emefiele Damar Yin Tafiye-tafiye A Nijeriya
  • NIS Shiyyar Arewa Maso Gabas Ta Kaddamar Da “Operation Tsaron Iyaka”

A nasa bangare, minista Wang Yi ya isar da gaisuwar shugaban kasar Sin Xi Jinping ga shugaban kasar Togo, inda ya bayyana cewa, zumuntan dake tsakanin Sin da Togo, ya zama abin misali ga hadin gwiwar dake tsakanin kasashe masu tasowa. Sin za ta kara yin hadin gwiwa tare da kasar Togo kan manyan tsare-tsare, da nuna goyon baya ga kasar Togo wajen samun bunkasuwa mai dorewa. Ya ce, karni na 21, karni ne na farfado da kasashe masu tasowa. Kasar Sin za ta ci gaba da tsayawa tsayin daka tare da kasashen Afirka, da taimakawa kasashen Afirka wajen gaggauta samun ci gaba kansu, da sa kaimi da inganta hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afirka, da kara amfana da sakamakon hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afirka, don samun moriyar Togo da kasashen Afirka.

A wannan rana kuma, Wang Yi ya yi tattaunawa tare da firaministar kasar Togo Mme Victoire Sidémeho Tomégah Dogbé da kuma ministan harkokin wajen kasar Togo Robert Dussey.

Togo
Sannan a yayin ganawar shugaban kasar Cote d’Ivoire Alassane Ouattara da Mr. Wang Yi, Alassane Ouattara ya yaba da hadin gwiwar dake tsakanin kasashensa da Sin, inda ya bayyana cewa kasar Sin ta zama babbar abokiyar cinikayya mafi girma da kuma tushen zuba jari ga kasar ta Cote d’Ivoire.

Labarai Masu Nasaba

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Cote d’Ivoire za ta ci gaba da ba da fifiko wajen raya dangantakar dake tsakaninta da kasar Sin, a cewar shugaban.

Ya kuma jaddada cewa kasar Sin daya ce tak a duniya, kuma Taiwan wani yanki ne na kasar Sin.

Wang ya ce, bangaren kasar Sin na matukar yabawa irin goyon bayan da Cote d’Ivoire ke baiwa kasar Sin wajen kiyaye dinkuwar kasar da cikakkun yankunanta. Ya kuma bayyana cewa, kasar Sin a shirye take ta sa kaimi ga inganta hadin gwiwar moriyar juna tsakaninta da Cote d’Ivoire.

Ya ci gaba da cewa, kasar Sin a shirye take ta yi aiki tare da kasashen Afirka, wajen gano ingantattun hanyoyin da suka dace da yanayin da kasashen ke ciki, da kiyaye ‘yancin kansu, da samar da ci gaba da wadata tare, ta yadda za a cimma nasarar zamanantarwa tare.

Wang ya kuma tattauna da ministan harkokin wajen Cote d’Ivoire a ranar Larabar.

Kasar Cote d’Ivoire ita ce kasa ta karshe a Afirka na ziyarar farko da ministan harkokin wajen kasar Sin ya kai a ketare a bana. Wang ya kuma ziyarci Masar da Tunisiya da kuma Togo yayin ziyarar da ta fara a ranar Asabar. (Zainab Zhang, Yahaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Shugaban kasar Cote d’IvoireShugaban kasar TogoWang yi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsaro: Gwamnatin Zamfara Ta Haramta Wa Sarakuna Bada Izinin Hakar Ma’adanai

Next Post

Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Mai Dorewa Da Inganci Na Kara Ba Da Gudummawa Ga Ci Gaban Duniya

Related

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

5 hours ago
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata
Daga Birnin Sin

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

6 hours ago
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

8 hours ago
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya
Daga Birnin Sin

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

9 hours ago
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

16 hours ago
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

18 hours ago
Next Post
Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Mai Dorewa Da Inganci Na Kara Ba Da Gudummawa Ga Ci Gaban Duniya

Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Mai Dorewa Da Inganci Na Kara Ba Da Gudummawa Ga Ci Gaban Duniya

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.