ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabannin Togo Da Cote d’Ivoire Sun Gana Da Ministan Harkokin Wajen Sin

by CGTN Hausa
2 years ago
Togo

Shugaban kasar Togo Faure Essozimna Gnassingbé da shugaban kasar Cote d’Ivoire Alassane Ouattara sun gana da mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta Sin kuma ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi dake ziyara a kasashensu jiya Laraba a birnin Lome da kuma a birnin Abidjan.

A yayin ganawar, shugaba Faure Essozimna Gnassingbé na Togo ya yi karin haske kan dangantakar dake tsakanin Togo da Sin da ma hadin gwiwarsu, ya ce bisa dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka, kasar Togo da sauran kasashen Afirka, sun samu babban ci gaba a fannin samar da kayayyakin more rayuwa. Ya kara da cewa, tattalin arzikin Afirka ya kara bunkasa, an kuma tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a nahiyar Afirka, har ma al’ummun nahiyar na smaun Moriya. Wadannan suna da nasaba da tallafin da kasar Sin ta dade tana samarwa. Togo ta yaba da yadda kasar Sin ke tabbatar da adalci a duniya, da nuna adawa da tsoma baki a harkokin cikin gidan Afirka, da taka rawar da ta kamata wajen samun ci gaban Afirka cikin lumana.

  • Kotu Ta Bai Wa Emefiele Damar Yin Tafiye-tafiye A Nijeriya
  • NIS Shiyyar Arewa Maso Gabas Ta Kaddamar Da “Operation Tsaron Iyaka”

A nasa bangare, minista Wang Yi ya isar da gaisuwar shugaban kasar Sin Xi Jinping ga shugaban kasar Togo, inda ya bayyana cewa, zumuntan dake tsakanin Sin da Togo, ya zama abin misali ga hadin gwiwar dake tsakanin kasashe masu tasowa. Sin za ta kara yin hadin gwiwa tare da kasar Togo kan manyan tsare-tsare, da nuna goyon baya ga kasar Togo wajen samun bunkasuwa mai dorewa. Ya ce, karni na 21, karni ne na farfado da kasashe masu tasowa. Kasar Sin za ta ci gaba da tsayawa tsayin daka tare da kasashen Afirka, da taimakawa kasashen Afirka wajen gaggauta samun ci gaba kansu, da sa kaimi da inganta hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afirka, da kara amfana da sakamakon hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afirka, don samun moriyar Togo da kasashen Afirka.

ADVERTISEMENT

A wannan rana kuma, Wang Yi ya yi tattaunawa tare da firaministar kasar Togo Mme Victoire Sidémeho Tomégah Dogbé da kuma ministan harkokin wajen kasar Togo Robert Dussey.

Togo
Sannan a yayin ganawar shugaban kasar Cote d’Ivoire Alassane Ouattara da Mr. Wang Yi, Alassane Ouattara ya yaba da hadin gwiwar dake tsakanin kasashensa da Sin, inda ya bayyana cewa kasar Sin ta zama babbar abokiyar cinikayya mafi girma da kuma tushen zuba jari ga kasar ta Cote d’Ivoire.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Cote d’Ivoire za ta ci gaba da ba da fifiko wajen raya dangantakar dake tsakaninta da kasar Sin, a cewar shugaban.

Ya kuma jaddada cewa kasar Sin daya ce tak a duniya, kuma Taiwan wani yanki ne na kasar Sin.

Wang ya ce, bangaren kasar Sin na matukar yabawa irin goyon bayan da Cote d’Ivoire ke baiwa kasar Sin wajen kiyaye dinkuwar kasar da cikakkun yankunanta. Ya kuma bayyana cewa, kasar Sin a shirye take ta sa kaimi ga inganta hadin gwiwar moriyar juna tsakaninta da Cote d’Ivoire.

Ya ci gaba da cewa, kasar Sin a shirye take ta yi aiki tare da kasashen Afirka, wajen gano ingantattun hanyoyin da suka dace da yanayin da kasashen ke ciki, da kiyaye ‘yancin kansu, da samar da ci gaba da wadata tare, ta yadda za a cimma nasarar zamanantarwa tare.

Wang ya kuma tattauna da ministan harkokin wajen Cote d’Ivoire a ranar Larabar.

Kasar Cote d’Ivoire ita ce kasa ta karshe a Afirka na ziyarar farko da ministan harkokin wajen kasar Sin ya kai a ketare a bana. Wang ya kuma ziyarci Masar da Tunisiya da kuma Togo yayin ziyarar da ta fara a ranar Asabar. (Zainab Zhang, Yahaya)

Togo
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Mai Dorewa Da Inganci Na Kara Ba Da Gudummawa Ga Ci Gaban Duniya

Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Mai Dorewa Da Inganci Na Kara Ba Da Gudummawa Ga Ci Gaban Duniya

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.