• English
  • Business News
Sunday, August 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Daƙile Wani Harin Ta’addanci Tare Da Cafke Wasu Mutum Biyu A Taraba

by Muhammad
3 weeks ago
in Manyan Labarai
0
Sojoji Sun Daƙile Wani Harin Ta’addanci Tare Da Cafke Wasu Mutum Biyu A Taraba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sojojin Rundunar ta 6 ta Sojan Nijeriya, Sashen n 3 na Operation Whirl Stroke (OPWS) sun daƙile kai wani harin ta’addanci da aka shirya Taraba, bayan kama wasu mutane biyu da ake zargi da ta’addanci da kai hare-hare a wurare dabam-dabam a jihar.

Kakakin rundunar ta 6, Kyaftin Olubodunde Oni, ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis, 17 ga Yuli, 2025.

  • Sojoji Sun Kama Mutum 2 Da AK-47 A Taraba
  • Sojoji Sun Harbe Wani Ɗan Bindiga, Sun Ƙwato Makamai Bayan Artabu A Taraba

“Sojojin da ke sansanin FOB Wukari sun kama wani mai shekaru 45 mai suna Felix Myina, ɗan asalin karamar hukumar Ukum a jihar Benue.

“Bincike na farko ya nuna cewa wanda ake zargin babban mamba ne a wata ƙungiyar gungun ‘yan fashi da garkuwa da mutane da ke aiki ƙarƙashin wani mai suna Mcianan, wanda aka fi sani da Yellow,” cewar Oni.

Ya ce wannan gungun ‘yan ta’addar suna daga cikin barazana ga matafiya da mazauna yankin Jootar–Wukari.

Labarai Masu Nasaba

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 302, Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace A Katsina

Sojojin sun kwace waya kirar Tecno daga hannun Myina a lokacin da aka kama shi.

A wani ci gaban kuma, Oni ya ce wasu sojojin sun kama wani da ake zargin mamba ne a kungiyar ISWAP mai suna Abubakar Yusuf, ɗan asalin jihar Borno da ke zaune a Gassol.

“An kama shi ne yayin da yake gudanar da wasu al’adu a kofar fadar Aku-Uka a Wukari, wuri da ake ganin ISWAP na shirin kai hari,” in ji Oni.

An ce yana ƙoƙarin amfani da aljanu don sauƙaƙa wa ‘yan ta’adda kai hari.

Kayan da aka kama shi da shi sun haɗa da kaza matacciya da ƙwai tara da suka lalace da ƙahon dabba da kwalbar da ke ɗauke da garin wani abu, da ƙananan naman daji.

Ana cigaba da bincike yayin da dukkansu ke tsare a hannun rundunar sojin ta 6.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Daƙile hariNijeriyaSojojiTaraba
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kaduna: An Horar Da Sarakunan Gargajiya Kan Sasanta Rikici Da Samar Da Zaman Lafiya

Next Post

Wata Motar Tankar Mai Ta Kama Da Wuta Tare Da Kone Wasu Motoci A Ibadan, Jihar Oyo

Related

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja
Manyan Labarai

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

16 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 302, Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace A Katsina

1 day ago
Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara
Manyan Labarai

Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

2 days ago
Gwamnan Kano Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Gentle, Ya Bada Umarnin Zakulo Masu Laifin
Manyan Labarai

Gwamnan Kano Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Gentle, Ya Bada Umarnin Zakulo Masu Laifin

3 days ago
Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ɗalibin BUK A Kano
Manyan Labarai

Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ɗalibin BUK A Kano

3 days ago
Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi

3 days ago
Next Post
Wata Motar Tankar Mai Ta Kama Da Wuta Tare Da Kone Wasu Motoci A Ibadan, Jihar Oyo

Wata Motar Tankar Mai Ta Kama Da Wuta Tare Da Kone Wasu Motoci A Ibadan, Jihar Oyo

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

August 10, 2025
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

August 9, 2025
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

August 9, 2025
Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

August 9, 2025
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

August 9, 2025
Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

August 9, 2025
Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

August 9, 2025
Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

August 9, 2025
Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

August 9, 2025
An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.