• English
  • Business News
Sunday, August 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda 5 Da Karbar Wadanda Suka Yi Saranda 44 A Borno

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
12 months ago
in Labarai
0
Sojoji
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wasu hare-hare da dakarun sojin Nijeriya suka kai wa ‘yan ta’adda sun yi nasarar hallaka biyar tare da karbar wasu ‘yan ta’adda da iyalai 44 da suka mika wuya a jihar Borno.

 

Sojojin sun kuma kama wani kasurgumin barawon shanu da ake nema ruwa a jallo a Jihar Filato da kuma wani da ake zargin mai sayar da makamai ne a jihar Oyo.

  • Tsadar Rayuwa A Nijeriya Ta Karu Da Kashi 19 A Wata 1
  • Jihohi Sun Kashe Naira Biliyan 139.92 Wajen Biyan Bashin Kasashen Ketare A Wata 6

Sakamakon wadannan hare-hare, sojojin sun kuma kwato bama-bamai, makamai, alburusai, da shanun da aka sace.

 

Labarai Masu Nasaba

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

A wata sanarwa da rundunar sojin Najeriya ta fitar a shafinta na sada zumunta, ta bayyana cewa, a ranar 12 ga watan Agustan shekarar 2024 ne sojojin suka kai wani samame a wani sansani na ‘yan ta’addan ISWAP a karamar hukumar Bama ta jihar Borno inda suka kashe ‘yan ta’adda biyar. Sun kuma kwato Bama-bamai guda biyu, bindigogin toka guda biyu, abin durin Bomb na RPG daya, Kwanson alburushi na bindigar AK-47 Rifle daya, harsashi 23 samfurin 7.62 d 54mm, babura shida da magunguna iri-iri.

 

A ci gaba da farmakin da ake kai wa kungiyoyin ‘yan ta’adda a fagen yaki na Arewa-maso-Gabas, “’yan ta’addan Boko Haram 44 da iyalansu sun kuma mika wuya ga sojojin da aka tura a kananan hukumomin Bama, Dikwa da Gwoza na Jihar Borno”.

 

A halin da ake ciki kuma, sojoji a Jihar Filato sun kama wani da ake zargi da satar shanu, Malam Maawuya Shuaibu, a Mararaban Kantom da ke karamar hukumar Barikin Ladi a jihar.

 

An kama wanda ake zargin wanda ya kasance cikin jerin sunayen mutanen da jami’an tsaro ke nema bisa alaka da aikata miyagun laifuka a kananan hukumomin Barikin Ladi, Riyom da Mangu na jihar, yayin da sojojin suka dauki mataki bayan samun sahihan bayanan sirri a kan wanda ake zargin. Dakarun sun kwato shanu 32 daga hannun wanda ake zargin.

 

Bugu da kari, a Jihar Bayelsa, sojoji sun kai samame a maboyar miyagu da ake zargin ‘yan fashi ne a yankin Korokorosie da ke karamar hukumar kudancin Ijaw, inda suka kama wani mai suna Donald Emason tare da kwato bindigar Ribarbar guda daya da wasu bindigogi kirar gida guda biyu da wanda ake zargin ya boye.

 

Hakazalika, sojojin da aka tura karamar hukumar Akinyele ta jihar Oyo, sun kama wani da ake zargin dan bindiga ne Mohammed Bello, mai shekaru 33.

 

Sanarwar ta kuma ce wanda ake zargin, wanda aka cafko shi daga maboyarsa, “ya amsa cewa yana daya daga cikin masu aika makamai da alburusai ga gungun masu garkuwa da mutane na Bello Chikidawoje da ke aikata miyagun ayyukansu a yankin baki daya”.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnan Kano Ya Naɗa Shugaban Sabuwar Ma’aikatar Tsaro

Next Post

Dalilan Da Suka Sabbaba Karancin Abinci A Nijeriya — Masana

Related

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho
Labarai

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

29 minutes ago
Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata
Labarai

Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

1 hour ago
NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja
Manyan Labarai

NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

2 hours ago
Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto
Labarai

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

16 hours ago
An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja
Manyan Labarai

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

20 hours ago
Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi
Labarai

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

21 hours ago
Next Post
Dalilan Da Suka Sabbaba Karancin Abinci A Nijeriya — Masana

Dalilan Da Suka Sabbaba Karancin Abinci A Nijeriya — Masana

LABARAI MASU NASABA

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

August 10, 2025
Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

August 10, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

August 10, 2025
Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

August 10, 2025
Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

August 10, 2025
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

August 9, 2025
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

August 9, 2025
Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

August 9, 2025
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

August 9, 2025
Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.