• English
  • Business News
Sunday, November 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

by Abubakar Sulaiman
4 weeks ago
Sojoji

Shalƙwatar Tsaro ta Nijeriya (DHQ) ta bayyana cewa Sojojin ƙasar da ke aiyukan cikin gida sun kama ƴan ta’adda, da ƴan fashi, da sauran miyagu 450, tare da ceto mutane 180 da aka yi garkuwa da su a cikin watan Satumba.

Daraktan yaɗa labarai na rundunar tsaro, Manjo Janar Markus Kangye, ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar, inda ya ce Sojojin sun kuma karɓi masu laifi 39 da suka mika wuya, tare da kwato ɗanyen mai da darajarsa ta kai ₦112,175,220.

  • Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP, Sun Kama Wasu Da Miyagun Ƙwayoyi
  • Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

Kangye ya ce Sojojin sun ƙwato makamai 63, da harsasai 4,475, da wasu kayan fashewa 294, motocin ƴan ta’adda, da babura, da na’urorin sadarwa da ake amfani da su wajen aikata laifuka. A yankin Kudu maso Kudu, ya ce dakarun sun kuma kwato lita 49,321 na ɗanyen mai, lita 6,970 na dizel, lita 1,900 na kerosene, da lita 1,475 na fetur, tare da lalata wuraren tace mai 41 da ba bisa ƙa’ida ba.

A cewarsa, an kuma gano manyan bindigogi, da RPG, da makaman da aka ƙera a gida, da kayan haɗa abubuwan fashewa a wuraren da aka kai farmaki.

Janar Kangye ya tabbatar da cewa aikin yaƙi da ta’addanci na ci gaba, kuma kwamandojin da ke filin daga za su ci gaba da nazarin halin da ake ciki don tabbatar da zaman lafiya da hana sake tashin tarzoma. Ya ƙara da cewa rundunar tsaro tana aiki ne cikin bin doka da ƙa’idojin ƙasa da na duniya, tare da mayar da hankali kan kare rayukan jama’a da na Sojoji a dukkan fannonin aikin.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Tsaro

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja
Tsaro

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22

October 12, 2025
Next Post
Yadda Ake Lemon Tsamiya (Tamarin Juice)

Yadda Ake Lemon Tsamiya (Tamarin Juice)

LABARAI MASU NASABA

Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Wadi Al-Salam: Maƙabartar Musulmai Mafi Girma A Duniya

November 2, 2025
An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu

An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu

November 2, 2025
Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?

Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?

November 2, 2025
A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?

A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?

November 2, 2025
Maganin Nankarwa (3)

Maganin Nankarwa (3)

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legas

November 2, 2025
Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka

Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka

November 2, 2025
Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala

Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala

November 2, 2025
Yaya Da Kani Sun Mutu A Cikin Ramin Masai A Kano

An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano

November 2, 2025
Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.