• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Kubutar Da Wasu ‘Yan Matan Chibok 2 Bayan Shekara 9 A Hannun Boko Haram

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Sojoji Sun Kubutar Da Wasu ‘Yan Matan Chibok 2 Bayan Shekara 9 A Hannun Boko Haram
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dakarun Operation Hadin Kai sun ceto wasu ‘yan mata biyu da aka sace daga karamar hukumar Chibok ta Jihar Borno a watan Afrilun 2014.

Wannan ceton ya zo ne shekaru tara da ‘yan ta’addar Boko Haram suka kai hari makarantarsu a lokacin da suke rubuta jarabawar kammala sakandare.

  • A Yi Kokarin Yin Amfani Da Damammakin Da Kasar Sin Ta Samar
  • Jarin Waje Na Sin Na Bunkasa Ci Gaban Kasar Habasha

An kula da wadanda abin ya shafa – Esther Marcus da Hauwa Malta, dukkansu masu shekaru 26 – yayin da sojoji suka ceto su a Lagara, wani yanki na ‘yan Boko Haram da ke dajin Sambisa, a ranar 21 ga Afrilu, 2023.

Ceton na baya-bayan nan, adadin ‘yan matan da aka yi garkuwa da su yanzu ya kai 125, ciki har da 107 da ‘yan ta’addan suka sake su a shekarar 2018, uku da sojoji suka ceto a shekarar 2019, biyu a shekarar 2021, da kuma 11 a shekarar 2022.

A cewar kwamandan Operation Hadin Kai, Manjo Janar Ibrahim Sallau Ali, “har yanzu ba a gano 94 ba.

Labarai Masu Nasaba

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

“An ceto Esther tare da ‘yarta ‘yar shekara daya. Yayin da ake garkuwa da ita, ta auri wani Garba, wanda ake kira Garus, dan ta’adda, wanda daga baya sojoji suka kashe; sannan wani dan ta’adda mai suna Abba ya aure ta; tana tare da shi har zuwa lokacin da aka ceto ta.”

Kwamandan ya bayyana cewa an ceto Hauwa Malta da cikin wata takwas da kwana 10; ta kara da cewa ta haifi wani yaro a cibiyar lafiya ta Seven Div kwanaki 10 bayan ceto su.

Sojojin sun kuma kashe sama da mutane 70 da ake zargin ‘yan ta’adda ne a farmakin da suka kai a yankin Arewa maso Gabas.

An kuma kama sama da ‘yan ta’adda 140 a tsawon lokacin, tare da kwato makamai da dama da suka hada da nakiya, kamar yadda daraktan ayyukan yada labarai na tsaro, Manjo Janar Musa Danmadami ya shaida wa manema labarai a ranar Alhamis.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Boko HaramBornoChibokSojoji
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jarin Waje Na Sin Na Bunkasa Ci Gaban Kasar Habasha

Next Post

Masanin Kasar Afrika Ta Kudu Ya Bayyana Kwarin Gwiwa Kan Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin

Related

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki
Manyan Labarai

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

6 hours ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

8 hours ago
Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su
Manyan Labarai

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

13 hours ago
Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

13 hours ago
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja
Manyan Labarai

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

17 hours ago
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi
Daga Birnin Sin

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

1 day ago
Next Post
Masanin Kasar Afrika Ta Kudu Ya Bayyana Kwarin Gwiwa Kan Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin

Masanin Kasar Afrika Ta Kudu Ya Bayyana Kwarin Gwiwa Kan Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

June 27, 2025
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

June 27, 2025
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

June 27, 2025
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

June 27, 2025
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

June 27, 2025
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.