• English
  • Business News
Thursday, October 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2

by Sadiq
3 years ago
Chibok

Rundunar sojin Nijeriya ta ce ta kubutar da wasu ‘yan mata biyu da ‘yan ta’addar Boko Haram suka yi garkuwa da su a makarantar sakandaren ‘yan mata ta gwamnati a garin Chibok da ke jihar Borno a shekarar 2014.

LEADERSHIP ta tattaro cewa ‘yan matan biyu da aka bayyana sunayensu da Hannatu Musa da Kauna Luka, Sojojin Birgediya 21 na sulke ne a karamar hukumar Bama a ranar 26 ga watan Yuli, suka ceto shekaru takwas bayan sace su.

  • Jami’ar MAAUN Ta Rantsar Da Sabbin Dalibai Sama Da 500 A Kano
  • ‘Yan Bindiga Sun Kutsa Cikin Gidaje Da Dama A Kaduna, Suna Sace Jama’a

A cewar wani rahoton sirri da aka samu daga manyan majiyoyin soji na Zagazola Makama, kwararre kan yaki da tada kayar baya da kuma tsaro a tafkin Chadi, ya shaida wa wakilinmu, ‘yan matan sun tsere daga sansanin Gazuwa, hedikwatar kungiyar Jama’at Ahl-Sunnah lid-Da’wah wa’l-Jihād, kungiyar Boko Haram, wadda a da ake kira Gabchari, Mantari da Mallum Masari, da ke da nisan kilomita tara zuwa garin Bama.

LEADERSHIP ta ce wasu ‘yan matan makarantar Chibok guda biyu da aka ceto a baya sun shaida wa hukumomin sojin cewa akwai ‘yan matan makarantar Chibok kusan 20 da har yanzu ake tsare da su kuma aka yi musu auren dole a sansanin Gazuwa.

‘Yan matan makarantar Chibok guda biyun da sojoji suka ceto a baya-bayan nan sune Mary Dauda da Hauwa Joseph.

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Ƙara Raguwa Zuwa Kashi 18.02%

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

Sai dai tserewar da suka yi daga sansanin ‘yan ta’addan ya biyo bayan gagarumin farmakin da dakarun ‘Operation Hadin Kai’ suka ci gaba da kai wa wanda ya janyo yunwa ya kuma sa ‘yan ta’addan yin kaura daga yankunan.

Idan za a iya tunawa kungiyar Boko Haram ta yi garkuwa da dalibai mata 276, masu shekaru daga 16 zuwa 18 a makarantar sakandaren ’yan mata ta gwamnati da ke garin Chibok a ranar 14 ga Afrilu, 2014.

Sama da ‘yan matan makarantar 100 ne har yanzu ba a gansu ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

sallah
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Ƙara Raguwa Zuwa Kashi 18.02%

October 15, 2025
Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

October 15, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

October 15, 2025
Next Post
An Bude Taron Dandalin Kare Hakkin Dan Adam Na Beijing Na Shekarar 2022

An Bude Taron Dandalin Kare Hakkin Dan Adam Na Beijing Na Shekarar 2022

LABARAI MASU NASABA

Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan

Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan

October 15, 2025
Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 

Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 

October 15, 2025
Nazarin CGTN: Jamaar Duniya Sun Yi Ammana Amurka Za Ta Fi Jin Jiki Daga Yakin Haraji 

Nazarin CGTN: Jamaar Duniya Sun Yi Ammana Amurka Za Ta Fi Jin Jiki Daga Yakin Haraji 

October 15, 2025
Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano

Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano

October 15, 2025
Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Ƙasar Madagascar

Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Ƙasar Madagascar

October 15, 2025
Shugaban Zaunannen Kwamitin Majalisar Wakilan Jama’ar Sin Ya Gana Da Mukaddashin Shugaban Majalisar Dattawan Kasar Liberia

Shugaban Zaunannen Kwamitin Majalisar Wakilan Jama’ar Sin Ya Gana Da Mukaddashin Shugaban Majalisar Dattawan Kasar Liberia

October 15, 2025
Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 

Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 

October 15, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

October 15, 2025
An Bude Bikin Baje Kolin Kasuwanci Na Kasa Da Kasa Na 138 A Guangzhou

An Bude Bikin Baje Kolin Kasuwanci Na Kasa Da Kasa Na 138 A Guangzhou

October 15, 2025
sallah

Da Ɗumi-ɗumi: Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Ƙara Raguwa Zuwa Kashi 18.02%

October 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.