• English
  • Business News
Monday, July 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai, Da ɗumi-ɗuminsa
0
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar sojin Nijeriya ta ce ta kubutar da wasu ‘yan mata biyu da ‘yan ta’addar Boko Haram suka yi garkuwa da su a makarantar sakandaren ‘yan mata ta gwamnati a garin Chibok da ke jihar Borno a shekarar 2014.

LEADERSHIP ta tattaro cewa ‘yan matan biyu da aka bayyana sunayensu da Hannatu Musa da Kauna Luka, Sojojin Birgediya 21 na sulke ne a karamar hukumar Bama a ranar 26 ga watan Yuli, suka ceto shekaru takwas bayan sace su.

  • Jami’ar MAAUN Ta Rantsar Da Sabbin Dalibai Sama Da 500 A Kano
  • ‘Yan Bindiga Sun Kutsa Cikin Gidaje Da Dama A Kaduna, Suna Sace Jama’a

A cewar wani rahoton sirri da aka samu daga manyan majiyoyin soji na Zagazola Makama, kwararre kan yaki da tada kayar baya da kuma tsaro a tafkin Chadi, ya shaida wa wakilinmu, ‘yan matan sun tsere daga sansanin Gazuwa, hedikwatar kungiyar Jama’at Ahl-Sunnah lid-Da’wah wa’l-Jihād, kungiyar Boko Haram, wadda a da ake kira Gabchari, Mantari da Mallum Masari, da ke da nisan kilomita tara zuwa garin Bama.

LEADERSHIP ta ce wasu ‘yan matan makarantar Chibok guda biyu da aka ceto a baya sun shaida wa hukumomin sojin cewa akwai ‘yan matan makarantar Chibok kusan 20 da har yanzu ake tsare da su kuma aka yi musu auren dole a sansanin Gazuwa.

‘Yan matan makarantar Chibok guda biyun da sojoji suka ceto a baya-bayan nan sune Mary Dauda da Hauwa Joseph.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Tsara Yadda Za A Binne Buhari

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Talata A Matsayin Hutu Don Alhinin Marigayi Buhari

Sai dai tserewar da suka yi daga sansanin ‘yan ta’addan ya biyo bayan gagarumin farmakin da dakarun ‘Operation Hadin Kai’ suka ci gaba da kai wa wanda ya janyo yunwa ya kuma sa ‘yan ta’addan yin kaura daga yankunan.

Idan za a iya tunawa kungiyar Boko Haram ta yi garkuwa da dalibai mata 276, masu shekaru daga 16 zuwa 18 a makarantar sakandaren ’yan mata ta gwamnati da ke garin Chibok a ranar 14 ga Afrilu, 2014.

Sama da ‘yan matan makarantar 100 ne har yanzu ba a gansu ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan Matan ChibokBoko HaramBornoDalibaiSojoji
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jami’ar MAAUN Ta Rantsar Da Sabbin Dalibai Sama Da 500 A Kano

Next Post

An Bude Taron Dandalin Kare Hakkin Dan Adam Na Beijing Na Shekarar 2022

Related

Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Tsara Yadda Za A Binne Buhari
Manyan Labarai

Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Tsara Yadda Za A Binne Buhari

2 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Talata A Matsayin Hutu Don Alhinin Marigayi Buhari
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Talata A Matsayin Hutu Don Alhinin Marigayi Buhari

3 hours ago
Bauchi Da Gombe Sun Koka Kan Jinkirin Aikin Haƙo Mai Na Kolmani
Manyan Labarai

Bauchi Da Gombe Sun Koka Kan Jinkirin Aikin Haƙo Mai Na Kolmani

5 hours ago
An Tsaurara Matakan Tsaro A Daura Gabanin Jana’izar Buhari A Gobe Talata
Da ɗumi-ɗuminsa

Sojoji Sun Kama Mutane 50 Masu Fasa-ƙwaurin Mai Da Lalata Haramtattun Matatun Mai A Neja-Delta

6 hours ago
An Tsaurara Matakan Tsaro A Daura Gabanin Jana’izar Buhari A Gobe Talata
Da ɗumi-ɗuminsa

An Tsaurara Matakan Tsaro A Daura Gabanin Jana’izar Buhari A Gobe Talata

7 hours ago
DA ƊUMI-ƊUMI: An Ɗage Jana’izar Buhari Zuwa Gobe Talata A Mahaifarsa Ta Daura, Jihar Katsina
Da ɗumi-ɗuminsa

DA ƊUMI-ƊUMI: An Ɗage Jana’izar Buhari Zuwa Gobe Talata A Mahaifarsa Ta Daura, Jihar Katsina

7 hours ago
Next Post
An Bude Taron Dandalin Kare Hakkin Dan Adam Na Beijing Na Shekarar 2022

An Bude Taron Dandalin Kare Hakkin Dan Adam Na Beijing Na Shekarar 2022

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Maraba Da ’Yan Jaridar Duniya Da Su Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Harin Japan Da Na Tafarkin Murdiya 

Sin Na Maraba Da ’Yan Jaridar Duniya Da Su Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Harin Japan Da Na Tafarkin Murdiya 

July 14, 2025
Osimhen Na Dab Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Osimhen Na Dab Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 14, 2025
Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

July 14, 2025
Za A Iya Yarda Da Buhari Kan Kowace Irin Amana A Duniya — Abdulsalami

Za A Iya Yarda Da Buhari Kan Kowace Irin Amana A Duniya — Abdulsalami

July 14, 2025
Cinikayyar Shige Da Fice Ta Sin Ta Karu Da Kaso 2.9 Bisa Dari A Watanni Shida Na Farkon Bana

Cinikayyar Shige Da Fice Ta Sin Ta Karu Da Kaso 2.9 Bisa Dari A Watanni Shida Na Farkon Bana

July 14, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,111, Sun Yi Garkuwa Da 276 A Nijeriya Cikin Watan Yuni

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,111, Sun Yi Garkuwa Da 276 A Nijeriya Cikin Watan Yuni

July 14, 2025
Kasar Sin Ta Nuna Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Nijeriya Buhari

Kasar Sin Ta Nuna Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Nijeriya Buhari

July 14, 2025
Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Tsara Yadda Za A Binne Buhari

Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Tsara Yadda Za A Binne Buhari

July 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Talata A Matsayin Hutu Don Alhinin Marigayi Buhari

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Talata A Matsayin Hutu Don Alhinin Marigayi Buhari

July 14, 2025
Za A Yi Taron Shugabannin Matasa Na Farko Na Dandalin Zaman Lafiya Da Tsaro Na Sin Da Afirka A Nanjing

Za A Yi Taron Shugabannin Matasa Na Farko Na Dandalin Zaman Lafiya Da Tsaro Na Sin Da Afirka A Nanjing

July 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.