• English
  • Business News
Saturday, June 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’ar MAAUN Ta Rantsar Da Sabbin Dalibai Sama Da 500 A Kano

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Jami’ar MAAUN Ta Rantsar Da Sabbin Dalibai Sama Da 500 A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’ar Maryam Abacha ta Nijeriya (MAAUN) da ke jihar Kano a ranar Litinini ta rantsar da sabbin dalibai sama da 500 da suka samu gurbin karatu na shekarar 2021/2022.

Kididdiga ta nuna cewa MAAUN Kano ita ce jami’a mai zaman kanta daya tilo daga cikin jami’o’i masu zaman kansu guda 111 da ake da su a Nijeriya da suka fara ayyukan karatu da dalibai kusan dubu daya a lokaci guda.

  • Shin Zargin Kasar Sin Ya Fi Yaki Da Ta’Addanci Muhimmanci?
  • Harin Kuje: DSS Ta Fitar Da Rahoton Tsaro 44 Kafin Kai Harin – Wase

A jawabinsa, shugaban Jami’ar MAAUN Kano, Farfesa Mohammad Israr, ya ce daliban da suka samu gurbin karatu a jami’ar a hukumance sun shiga shirin karatu bisa amincewar hukumar kula da jami’o’i ta kasa (NUC).

“Cikin farin ciki nake yi wa daukacin dalibai barka da zuwa jami’ar, na yi imani cewa Allah zai yi amfani da wannan jami’a wajen bunkasarku da ci gabanku ta kowane fanni na rayuwa.

“Ina taya iyayenku murna kan babban rawar da suke takawa a rayuwarku, ina addu’ar ka da wannan kokarin nasu ya tafi a banza,” in ji Shugaban MAAUN.

Labarai Masu Nasaba

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai

Shugaban ya ce Jami’ar tana koyar kwasa-kwasai da ke da kimar kasuwanci ga dalibai yana mai jaddada cewa tsarin koyarwa a jami’ar ya shafi harkokin kasuwanci da kuma dogaro da kai.

“Saboda haka wadanda suka kammala karatu a wannan jami’a ba za su shiga jerin masu neman aikin yi ido rufe ba a kasar nan, za su kasance wadanda suka assasa da kuma shiga sahun gaba a harkokin kasuwanci nan da wasu shekaru masu zuwa,” in ji Farfesa Isar.

A cewarsa, MAAUN Kano jami’a ce da ta shafi dalibai domin wuri ne da zai iya gyara shugabannin da za su zo a gaba.

“Muna alfahari da horar da dalibai a ayyukan ilimi. Muna mai da hankali kan habaka halayen dalibanmu bisa tsammanin cewa idan sun kammala karatun, za su ba da gudummawa mai ma’ana ga bayanan ci gaba a duk fadin duniya,” in ji shi.

Shugaban, wanda ya taya sabbin daliban murna da samun gurbin shiga bayan sun samu tantancewa da gwaje-gwajen jarabawa, ya shawarce su da su yi koyi da malamansu ta hanyar nuna tarbiya da sauke nauyin da ya rataya a wuyansu.

Ya kuma gargadi daliban da aka rantsar da su bi ka’idojin Jami’ar da kuma zama masu kyawawan halaye tare da sanya tufafi na mutunci.

A nata jawabin, kwamishiniyar ilimi ta jihar Kano, Dakta Mariya Bunkure, ta shawarci daliban da aka rantsar da su maida hankali wajen karatunsu, duba da irin makudan kudaden da iyayensu suka biya domin yin karatu a jami’ar.

Bunkure, wanda kuma memba ce a hukumar gudanarwar Jami’ar, ta gargadi daliban da su guji yin wani abu da zai iya bata sunan su da na jami’ar.

Ta yaba wa wanda ya kafa jami’ar, Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo, bisa kafa jami’ar wadda ta kasance daya daga cikin mafi inganci a kasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DalibaIlimiJami'akanoMAUUNSabon Zangon Karatu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shin Zargin Kasar Sin Ya Fi Yaki Da Ta’Addanci Muhimmanci?

Next Post

Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2

Related

jam'iyyu
Rahotonni

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

8 hours ago
Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai

9 hours ago
Nijeriya Da Morocco Za Su Sanya Hannu Kan Kulla Yarjejeniyar Aikin Bututun Iskar Gas
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Himmatu Wajen Inganta Karfin Sashen Fetur Da Gas Na Cikin Gida

10 hours ago
Gwamnati Ta Yi Karin Haske Kan Biyan Tallafin Rage Radadi Da Mafi Karancin Albashi
Labarai

Gwamnati Ta Yi Karin Haske Kan Biyan Tallafin Rage Radadi Da Mafi Karancin Albashi

12 hours ago
Dawanau
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dukufa Wajen Karya Farashin Kayan Abinci – Minista

14 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Shahararren Ɗan Damfarar Yanar Gizo A Bauchi
Labarai

Ƴansanda Sun Kama Shahararren Ɗan Damfarar Yanar Gizo A Bauchi

15 hours ago
Next Post
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2

Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2

LABARAI MASU NASABA

Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin

Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin

June 13, 2025
jam'iyyu

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

June 13, 2025
Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai

Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai

June 13, 2025
Babban Jami’in Diflomasiyyar Kasar Sin Ya Yi Kiran Karfafa Alaka Da Afirka

Babban Jami’in Diflomasiyyar Kasar Sin Ya Yi Kiran Karfafa Alaka Da Afirka

June 13, 2025
Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Gina Kasa A Gabar Da Ake Bikin Cika Shekaru 120 Da Haihuwar Dan Mazan Jiya Chen Yun

Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Gina Kasa A Gabar Da Ake Bikin Cika Shekaru 120 Da Haihuwar Dan Mazan Jiya Chen Yun

June 13, 2025
Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi

Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi

June 13, 2025
Nijeriya Da Morocco Za Su Sanya Hannu Kan Kulla Yarjejeniyar Aikin Bututun Iskar Gas

Gwamnatin Tarayya Ta Himmatu Wajen Inganta Karfin Sashen Fetur Da Gas Na Cikin Gida

June 13, 2025
Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka

Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka

June 13, 2025
Sin Ta Bayyana Adawa Da Keta Hurumin ‘Yanci Tsaro Da Ikon Mulkin Yankunan Iran

Sin Ta Bayyana Adawa Da Keta Hurumin ‘Yanci Tsaro Da Ikon Mulkin Yankunan Iran

June 13, 2025
Gwamnati Ta Yi Karin Haske Kan Biyan Tallafin Rage Radadi Da Mafi Karancin Albashi

Gwamnati Ta Yi Karin Haske Kan Biyan Tallafin Rage Radadi Da Mafi Karancin Albashi

June 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.