• Leadership Hausa
Monday, February 6, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Jami’ar MAAUN Ta Rantsar Da Sabbin Dalibai Sama Da 500 A Kano

by Khalid Idris Doya
6 months ago
in Labarai
0
Jami’ar MAAUN Ta Rantsar Da Sabbin Dalibai Sama Da 500 A Kano

Jami’ar Maryam Abacha ta Nijeriya (MAAUN) da ke jihar Kano a ranar Litinini ta rantsar da sabbin dalibai sama da 500 da suka samu gurbin karatu na shekarar 2021/2022.

Kididdiga ta nuna cewa MAAUN Kano ita ce jami’a mai zaman kanta daya tilo daga cikin jami’o’i masu zaman kansu guda 111 da ake da su a Nijeriya da suka fara ayyukan karatu da dalibai kusan dubu daya a lokaci guda.

  • Shin Zargin Kasar Sin Ya Fi Yaki Da Ta’Addanci Muhimmanci?
  • Harin Kuje: DSS Ta Fitar Da Rahoton Tsaro 44 Kafin Kai Harin – Wase

A jawabinsa, shugaban Jami’ar MAAUN Kano, Farfesa Mohammad Israr, ya ce daliban da suka samu gurbin karatu a jami’ar a hukumance sun shiga shirin karatu bisa amincewar hukumar kula da jami’o’i ta kasa (NUC).

“Cikin farin ciki nake yi wa daukacin dalibai barka da zuwa jami’ar, na yi imani cewa Allah zai yi amfani da wannan jami’a wajen bunkasarku da ci gabanku ta kowane fanni na rayuwa.

“Ina taya iyayenku murna kan babban rawar da suke takawa a rayuwarku, ina addu’ar ka da wannan kokarin nasu ya tafi a banza,” in ji Shugaban MAAUN.

Labarai Masu Nasaba

Dalilan Da Ke Hana Kwamfuta Da Wayoyin Hannu Sauri

Ko Mafarkin Samun Gwamna Mace Ta Farko A Nijeriya Zai Zama Gaskiya?

Shugaban ya ce Jami’ar tana koyar kwasa-kwasai da ke da kimar kasuwanci ga dalibai yana mai jaddada cewa tsarin koyarwa a jami’ar ya shafi harkokin kasuwanci da kuma dogaro da kai.

“Saboda haka wadanda suka kammala karatu a wannan jami’a ba za su shiga jerin masu neman aikin yi ido rufe ba a kasar nan, za su kasance wadanda suka assasa da kuma shiga sahun gaba a harkokin kasuwanci nan da wasu shekaru masu zuwa,” in ji Farfesa Isar.

A cewarsa, MAAUN Kano jami’a ce da ta shafi dalibai domin wuri ne da zai iya gyara shugabannin da za su zo a gaba.

“Muna alfahari da horar da dalibai a ayyukan ilimi. Muna mai da hankali kan habaka halayen dalibanmu bisa tsammanin cewa idan sun kammala karatun, za su ba da gudummawa mai ma’ana ga bayanan ci gaba a duk fadin duniya,” in ji shi.

Shugaban, wanda ya taya sabbin daliban murna da samun gurbin shiga bayan sun samu tantancewa da gwaje-gwajen jarabawa, ya shawarce su da su yi koyi da malamansu ta hanyar nuna tarbiya da sauke nauyin da ya rataya a wuyansu.

Ya kuma gargadi daliban da aka rantsar da su bi ka’idojin Jami’ar da kuma zama masu kyawawan halaye tare da sanya tufafi na mutunci.

A nata jawabin, kwamishiniyar ilimi ta jihar Kano, Dakta Mariya Bunkure, ta shawarci daliban da aka rantsar da su maida hankali wajen karatunsu, duba da irin makudan kudaden da iyayensu suka biya domin yin karatu a jami’ar.

Bunkure, wanda kuma memba ce a hukumar gudanarwar Jami’ar, ta gargadi daliban da su guji yin wani abu da zai iya bata sunan su da na jami’ar.

Ta yaba wa wanda ya kafa jami’ar, Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo, bisa kafa jami’ar wadda ta kasance daya daga cikin mafi inganci a kasar nan.

Tags: DalibaIlimiJami'akanoMAUUNSabon Zangon Karatu
Previous Post

Shin Zargin Kasar Sin Ya Fi Yaki Da Ta’Addanci Muhimmanci?

Next Post

Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2

Related

Dalilan Da Ke Hana Kwamfuta Da Wayoyin Hannu Sauri
Rahotonni

Dalilan Da Ke Hana Kwamfuta Da Wayoyin Hannu Sauri

4 hours ago
Ko Mafarkin Samun Gwamna Mace Ta Farko A Nijeriya Zai Zama Gaskiya?
Labarai

Ko Mafarkin Samun Gwamna Mace Ta Farko A Nijeriya Zai Zama Gaskiya?

5 hours ago
NAHCON Ta Rarraba Kujerun Aikin Hajjin Bana Ga Jihohi 36 Da Abuja
Labarai

NAHCON Ta Rarraba Kujerun Aikin Hajjin Bana Ga Jihohi 36 Da Abuja

7 hours ago
Matar Sufeto Ta Gurfanar Da Kurtun Dan Sanda A Kotu Kan Kashe Mijinta
Kotu Da Ɗansanda

Ya Kashe Makocinsa Don Ya Haske Idon Mahaifiyarsa Da Cocila

10 hours ago
Majalisar Dinkin Duniya Ta Yi Tir Da Kisan Fulani 40 A Jihar Nasarawa
Labarai

Majalisar Dinkin Duniya Ta Yi Tir Da Kisan Fulani 40 A Jihar Nasarawa

11 hours ago
Sojoji Sun Kama Mutum 116 Da Ke Yin Laifuka Daban-daban A Legas
Kotu Da Ɗansanda

Sojoji Sun Kama Mutum 116 Da Ke Yin Laifuka Daban-daban A Legas

13 hours ago
Next Post
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2

Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2

LABARAI MASU NASABA

Afirka Ba Ta Bukatar Lakca

Afirka Ba Ta Bukatar Lakca

February 5, 2023
Manoman Kwakwa 50 Sun Samu Horo Kan Noman Zamani

Manoman Kwakwa 50 Sun Samu Horo Kan Noman Zamani

February 5, 2023
Sin Na Matukar Adawa Da Matakin Amurka Na Harbo Babban Balan-balan Din Kasar Sin

Sin Na Matukar Adawa Da Matakin Amurka Na Harbo Babban Balan-balan Din Kasar Sin

February 5, 2023
Dalilan Da Ke Hana Kwamfuta Da Wayoyin Hannu Sauri

Dalilan Da Ke Hana Kwamfuta Da Wayoyin Hannu Sauri

February 5, 2023
Ko Mafarkin Samun Gwamna Mace Ta Farko A Nijeriya Zai Zama Gaskiya?

Ko Mafarkin Samun Gwamna Mace Ta Farko A Nijeriya Zai Zama Gaskiya?

February 5, 2023
Shirin Fim Na Tallata Shagalin Murnar Bikin Kunna Fitilu Da CMG Ya Tsara Ya Jawo Hankulan Al’ummar Afirka

Shirin Fim Na Tallata Shagalin Murnar Bikin Kunna Fitilu Da CMG Ya Tsara Ya Jawo Hankulan Al’ummar Afirka

February 5, 2023
An Gudanar Da Jerin Ayyuka Don Murnar Cika Shekara 1 Da Samun Nasarar Gudanar Da Wasannin Olympics Na Lokacin Sanyi Na Beijing

An Gudanar Da Jerin Ayyuka Don Murnar Cika Shekara 1 Da Samun Nasarar Gudanar Da Wasannin Olympics Na Lokacin Sanyi Na Beijing

February 5, 2023
NAHCON Ta Rarraba Kujerun Aikin Hajjin Bana Ga Jihohi 36 Da Abuja

NAHCON Ta Rarraba Kujerun Aikin Hajjin Bana Ga Jihohi 36 Da Abuja

February 5, 2023
Matar Sufeto Ta Gurfanar Da Kurtun Dan Sanda A Kotu Kan Kashe Mijinta

Ya Kashe Makocinsa Don Ya Haske Idon Mahaifiyarsa Da Cocila

February 5, 2023
Gwamnan Jigawa Ya Nada Hameem Nuhu Sanusi Matsayin Sabon Sarkin Dutse

Gwamnan Jigawa Ya Nada Hameem Nuhu Sanusi Matsayin Sabon Sarkin Dutse

February 5, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.