• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojojin Nijar Za Su Mika Mulki Nan Da Shekara 3 – Janar Tchiani

by Sadiq
2 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa, Kasashen Ketare, Manyan Labarai
0
Sojojin Nijar Za Su Mika Mulki Nan Da Shekara 3 – Janar Tchiani
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Janar Tchiani ya ce nan da wata daya za su kafa kwamitin da zai yi nazari kan sabon kundin tsarin mulki na kasar.

Shugaban sojojin da suka yi juyin mulki a Jamhuriyar Nijar Janar Abdourahamane Tchiani ya ce za su mika mulki ga gwamnatin farar-hula nan da shekaru uku masu zuwa.

  • Zantawa Da Dilma Rousseff, Shugabar Sabon Bankin Samar Da Ci Gaba
  • Kwamandojin Boko Haram 4 Da Wasu 13 Sun Mika Wuya Ga MNJTF

Ya bayyana haka ne a jawabin da ya gabatar ta gidan talabijin na kasar ranar Asabar da daddare.

Ya yi jawabin ne jim kadan bayan ya gana da tawagar kungiyar ECOWAS, karkashin jagorancin tsohon shugaban Nijeriya Janar Abdulsalami Abubakar.

Janar Tchiani ya ce nan da wata daya za su kafa kwamitin da zai yi nazari kan sabon kundin tsarin mulki na kasar.

Labarai Masu Nasaba

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

Ya kara da cewa Nijar ba ta son zuwa yaki kuma kofarsu a bude take su tattauna, amma kuma za su kare kansu idan bukatar hakan ta taso.

A gefe guda, tawagar Kungiyar ECOWAS karkashin jagorancin tsohon shugaban Nijeriya Janar Abdulsalami Abubakar ta gana da hambararren shugaban Nijar Mohamed Bazoum a Yamai, babban birnin kasar ranar Asabar.

Tawagar ta je Yamai ne domin lalubo hanyar magance rikicin siyasar da kasar ta fada a ciki tun bayan juyin mulkin da sojoji suka yi wa Bazoum ranar 26 ga watan Yuli.

Janar Abubakar ya shaida wa manema labarai cewa tawagarsa ta saurari bayani daga wurin Bazoum da kuma kalubalen da yake fuskanta tun da aka kifar da gwamnatinsa.

“Mun gan shi mun ji nashi ra’ayin da abin da aka yi mashi. Kuma akwai wasu ‘yan matsaloli wadanda ke tare da shi da ya yi mana bayani wadanda za mu gaya wa shugabanninmu,” in ji shi.

Ko da yake bai yi karin bayani game da ganawar ba, amma ya ce “wannan taro da aka yi Allah ya sa an samu mabudi ke nan da za mu ci gaba da tattaunawa don a samu a warware wannan matsala.”

Tun da fari Firaiministan kasar Ali Mahamane Laminé Zeine ya tarbi tawagar a filin jirgin sama na Diori Hamani.

Wannan tattaunawar na zuwa ne kwana guda bayan hafsoshin tsaron kasashen ECOWAS sun kammala taronsu a Ghana inda suka saka ranar da za su tura dakarunsu Jamhuriyyar Nijar idan hanyoyin diflomasiyya suka ci tura.

Wannan ne karo na biyu da wakilan ECOWAS karkashin jagorancin Abdulsalami Abubakar da Sarkin Musulmi Muhammad Sa’ad Abubakar ke zuwa Nijar domin sulhu.

A karon farko ba su samu ganawa da Janar Abdourahamane Tchiani ba inda suka koma ba tare da an cimma wata matsaya ba.

A ranar Juma’a ne kasashen Mali da Burkina Faso suka aike da jiragen yaki Nijar domin tallafa wa sojojin kasar kan duk wata barazana da za su fuskanta daga dakarun ECOWAS.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BazoumECOWASJuyin MulkiNijarSojoji
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zantawa Da Dilma Rousseff, Shugabar Sabon Bankin Samar Da Ci Gaba

Next Post

Gwamnan Katsina Ya Nuna Takaicinsa Kan ‘Yan Kasuwar Da Ke Boye Abinci 

Related

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

4 hours ago
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

7 hours ago
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

9 hours ago
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi
Manyan Labarai

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

13 hours ago
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
Manyan Labarai

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

14 hours ago
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
Manyan Labarai

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

1 day ago
Next Post
Gwamnan Katsina Ya Nuna Takaicinsa Kan ‘Yan Kasuwar Da Ke Boye Abinci 

Gwamnan Katsina Ya Nuna Takaicinsa Kan ‘Yan Kasuwar Da Ke Boye Abinci 

LABARAI MASU NASABA

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

September 17, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

September 17, 2025
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

September 17, 2025
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

September 17, 2025
Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

September 17, 2025
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

September 17, 2025
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.