• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ta’addancin ‘Yan Ta’adda A Kan Sarakuna

by Leadership Hausa
9 months ago
in Manyan Labarai
0
Ta’addancin ‘Yan Ta’adda A Kan Sarakuna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kisan da aka yi wa Alhaji Isa Muhammad Bawa, Sarkin Gobir na Gatawa da ke Jihar Sakkwato kwanannan ya kara fito da tsanannin matsalar tsaro a Nijeriya. Lamarin da ya faru a ranar 21 ga watan Agusta 2024 ya tayar da hankali matuka a kan tsaron lafiyar Sarakunan gargajiya a Nijeriya da ma sauran ‘yan Nijeriya gaba daya ya kuma fito da iri hali da iya aiki ko akasinsa na jami’an tsaron mu.

Kasancewar Sarkin Gobir Bawa da dansa sun kasannce a hannu ‘yan ta’adda na kusan wata daya kafin su kashe shi, duk kuwa da kokarin ceto shi da aka yi ya nuna sakaci da rashin iya aiki na masu tafiyar da harkokin tsaron kasar nan a wannan irin halin tabarbarewar tsaron da ake ciki.

  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Matafiya A Babbar Hanyar Gusau-Funtua
  • Kotu Ta Bada Belin Masu Zanga-Zangar Tsadar Rayuwa Kan Naira Milyan 10 Kowanensu

An kama Sarkin Gobir Bawa ne a ranar 27 ga watan Yuli,2024, tare da dansa, Kabiru Isa, yayin da suke dawowa daga taro a fadar Sarkin Musulmi da aka yi Sakkwato. Duk kokarin da iyalansa da masarautar Gobir ta yi ga gwamatin Jihar har ma da sakon bidiyon da aka turo daga mabuyar ‘yan ta’adda hakan bai wani taimaka ba. Lokacin da aka kai kudin fansa na naira Miliyan 60 da ‘yan ta’addan suka nema lokaci ya kure domin sun dade da kashe shi inda daga baya suka sako dansa.

Bayan mutuwarsa, kamar dai kowane lokaci sai ihun tir da kisan ke fitowa daga dukkan bangarori, inda gwamati ta sha alwashin kamo wadanda suka yi kisan. Wannan bai isa ba domi tamkar shan magani ne bayan mutuwa ne, ya kamata a ce jamai’an tsaro sun bi sawun masu garkuwa kamar yadda suka bi sawun wadanda suka sace dalibai likitoci na jami’ar Benuwai.Muna jinjina ga kokarin al’umma yankin maza da mata da suka fatattaki ‘yan ta’adda inda suka kwato gawar marigayi Sarkin suka kuma kwato wasu da aka yi garkuwa da su. Wannan abin da ya faru da a wasu kasashe ne da lallai an hukunta wasu daga cikin jami’an tsaron da ke da alhakin tabbatar da tsaro a yankin.

A watan Mayun 2024, ‘yan bindiga sun kashe Chif Auwal Wali, Sarkin gargajiya na Gidan Usmanu da ke Jihar Taraba.Hakanan kuma a watan Yuli ‘yan bindiga sun yi wa Sarkin Takum, Tanimu Kunbiya da dansa kwantan bauna yayin da suke dawowa daga wata jana’iza a jihar Taraba.

Labarai Masu Nasaba

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

A watan Agusta 2024, Sarakunan gargajiya da Sarakunan kauyuka 6 a garin Umucheke Okwe da ke karamar hukumar Onuimo na Jihar Imo aka kashe yayin da suke gudanar da wani taron neman zaman lafiya. Haka kuma a watan Yuli na shekarar data gabata an kashe sarakunan gargajiya da dama ciki har da na Nguru da ke karamar hukumar Aboh Mbaise,Eze Mmirioma, da Eze Joe-Benz Ochulor, Olu 1 na Otulu Amumara na masarautar Ezinihitte Mbaise da ke Jihar Imo.

A farkon watan Agusta, ‘yan bindiga sun kashe basaraken Umuihe da ke Jihar Ebonyi State, mai martaba Umazi Ibo Ubani.

A watan Disamba na shekarar 2023, ‘yan ta’adda sun kashe hakimin Yankuzo, Alhaji Hamza Kogo, da ke masarautar Tsafe a Jihar Zamfara a lokacin da suka yi kokarin yin garkuwa da shi da iyalansa.Haka kuma a shekarar 2020 aka kashe basaraken Olufon na Ifon, Oba Israel Adeusi, a kan babbar hanyar Ifonzuwa Benin a daidai watan Nuwamba na shekarar 2020.An dade ana aikata ta’addanci a kan Sarakunan gargajiya, rahotannin sun nuna cewa, an kashe fiye da sarakuna gargajiya 53 a cikn shekara 10 da suka wuce, kamar dai yadda rahoton wata kungiya mai zaman kanta mai suna SMB 2021 ta ruwaito.

Ya kamata a kawo karshen ta’addanci a kan Sarakunan gargajiya.Dole ne gwamati da jami’an tsaro su samar da yanayi na tsaro ga Sarakunan gargajiya da ‘yan kasa baki daya. Wannan kuma ba yana nufin samar masu jami’an tsaro masu kare lafiyarsu kadai ba, harma da samar da hanyoyin tattara bayanan sirri domin katse kokari da shirin ‘yan ta’adda na kai hari da sace Sarakunan gargajiya a sassan Nijeriya.

Karfafa hanyoyin tsaro a tsakanin al’umma zai taimaka wajen tabbatar da tsaro da kuma kawo karshen harkokin ‘yan ta’adda da ta’addanci a kasa, zai kuma taimaka wajen kawo karshen yadda ake sace Sarakunan gargajiya a kasar nan.

Wani rahoto da bincikenh da aka gudanar kwanan nan ya nuna yadda aka biya fiye da naira biliyan 1 a matsayin kudin fansa a tsakanin watan Yuli na shekarar 2023 zuwa watan Yuni na shekara 2024. Wadannan kudin hana shigewa ne ta hanyar bankuna. Ya kamata ayi amfani da hanyoyi na zamani wajen bin sawun kudaden tare da kama ‘yan ta’addar da masu daukar nauyinsu.

Ya kuma kamata Nijeriya ta hada kai da kwararru daga kasashen waje wajen yaki da harkokin ta’addanci da ‘yan ta’adda musamman ma ganin matsalolin tsaron da ake fuskanta a kasar nan suna da yawan gaske.

Kisan Sarkin Gobir Bawa da yadda ayyukan ta’addanci ke kara karuwa yana nuna raunin masu tafiyar da harkokin gwamanti a kasar nan.

A yayin da muke alhinin kashe-kashen da ake yi mana, ya kamata mu hada karfi da karfe wajen kawo karshen ayyukan ‘yan ta’adda da ta’addanci a sassan kasar nan musamman ma yadda ake ci wa Sarakunan gargajiyar mutunci wadanda sune ke dauke da mutuncin mu da al’adun mu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArewaMaharaSarakunaTa'addanciTsaroYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Buɗe Hanyar Kano Zuwa Maiduguri Da Ambaliyar Ruwa Ta Lalata 

Next Post

Ibtila’in Ambaliyar Ruwa: Halin Da Birnin Maiduguri Ya Tsinci Kansa A Ciki

Related

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

15 hours ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

1 day ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

1 day ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

1 day ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

2 days ago
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 
Manyan Labarai

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

2 days ago
Next Post
Ibtila’in Ambaliyar Ruwa: Halin Da Birnin Maiduguri Ya Tsinci Kansa A Ciki

Ibtila’in Ambaliyar Ruwa: Halin Da Birnin Maiduguri Ya Tsinci Kansa A Ciki

LABARAI MASU NASABA

Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.