• English
  • Business News
Friday, October 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tabbas Mun Samu Tangarda Wurin Shigar Da Sakamakon Zaben 2023 –INEC

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
INEC

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta bayyana cewa tabbas ta samu matsala wurin saka sakamakon zaben shugaban kasa a na’ura, sannan kuma ba ta samu wani taimakon kuda ba daga wurin kowa sai dai gwamnatin tarayya wacce ita ce doka ya daura mata alhakkin yin hakan.

Shughaban hukumar INEC, Farfesa Mahmood Yakubu shi ya bayyana hakan a yayin da yake bayar da ba’asi kan na’urar da aka yi amfani da su a lokacin zaben 2023, a lokacin da yake yi wa kungiyoyin fararen huda bayanai kan nazarin zaben 2023.

  • ’Yan Bindiga Sun Kashe Shugaban JIBWIS, Sun Sace Mutane 50 A Kaduna
  • Badakala A Kano: An Gano Biliyan 4 Da Ta Yi Batan-Dabo A KASCO

Ya kara jaddada cewa abokan hulda sun bayar da tallafi ne kai tsaye ta hanyar kungiyoyin fararen huda wajen gudanar da ayyukan zabe.

Shugaban INEC ya gode wa kungiyoyin farar hula da abokan huda ci bisa gagarumin goyon bayan da suka bai wa hukumar a zaben 2023.

Shugaban na INEC ya tunatar da cewa, kungiyoyi 228 (na gida 190 da 38 na kasashen waje) aka amince da su a matsayin masu sanya ido a zaben da ya gabata, 67 ne kawai suka mika rahotonsu ga hukumar kan zabe.

LABARAI MASU NASABA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

Ya ce: “A kan wannan lamari, ya dace hukumar ta nuna jin dadinta ga kungiyoyin farar hula da abokan hulda bisa gagarumin goyon bayan da suke bai wa hukumar a lokacin zaben 2023.

Wannan ya zo ne ta hanyar shawarwarin kan fasahar sadarwa da ilimantar da masu jefa kuri’a da gudanar da tarurruka da taron kara wa juna sani da kuma buga takardu.

“A wannan hadin gwiwar ne hukumar ta tantance masu sa ido saboda samun jin ra’ayoyi kan zabe da kuma shawarwarin da suka dace wadanda suke taimaka sosai wajen gudanar da zabe. Domin a zaben shekarar 2023, hukumar ta samu korafe-korafe guda 538 (504 na cikin gida da 34 na kasashen waje) daga wurin masu sa ido. Bayan yin cikakken nazari kan korafe-korafen, kungiyoyi 228 ne kawai (190 na cikin gida da 38 na waje) suka cika ka’idodin da aka zayyana. Sai dai kawo yanzu kungiyoyin sa ido 67 ne (62 na cikin gida da kuma na kasashen waje biyar) suka gabatar da rahoton bincikensu wanda ke wakiltar kusan kashi 30 na kungiyoyin da aka amince da su a zaben. Muna kira ga duk sauran kungiyoyin sa ido da aka amince da su wadanda har yanzu ba su gabatar da rahotonsu ba su yi kokarin gabatar wa hukumar.”

Shugaban INEC ya bayyana cewa an samu nasarar tantance masu kada kuri’a ta hanyar amfani da na’urar BBAS, amma kuma an samu matsala wajen shigar da sakamakon zabe ta intanet ta wannan na’ura.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Next Post
Yajin aiki: Tinubu Ya Roki Kungiyar Kwadago Da Ta Dan Kara Masa Lokaci

Tinubu Zai Karrama Matar Da Ta Tsinci Dala 80,000 Ta Mayar A Makka

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Gwamnan 2025 Sanata Uba Sani: Mai Haɗa Kan Al’ummar Da Suka Rarrabu

Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025, Injiniya Abdullahi Sule

October 24, 2025
Ƴansanda Sun Sake Kama Sowore Bayan An Bayar Da Belinsa

Ƴansanda Sun Sake Kama Sowore Bayan An Bayar Da Belinsa

October 24, 2025

Gwarzon Gwamnan 2025 Sanata Uba Sani: Mai Haɗa Kan Al’ummar Da Suka Rarrabu

October 24, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Sheriff Oboreɓwori: Gwamnan Da Ya Ginu Kan Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Al’umma

October 24, 2025
An Kafa Cibiyoyi 296 Na Koyon Fasahar Zamani A Faɗin Nijeriya

An Kafa Cibiyoyi 296 Na Koyon Fasahar Zamani A Faɗin Nijeriya

October 24, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Ma’aikatan INEC Uku Da Wasu

Ƴan Bindiga Sun Sace Ma’aikatan INEC Uku Da Wasu

October 24, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

October 24, 2025
Nnamdi Kanu Ya Sake Bayyana A Kotu Ba Tare Da Lauya Ba, Zai Kare Kansa Da Kansa

Nnamdi Kanu Ya Sake Bayyana A Kotu Ba Tare Da Lauya Ba, Zai Kare Kansa Da Kansa

October 24, 2025
Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

Ƙungiyoyin Ma’aikatan Jihar Kaduna Sun Yabawa Gwamna Sani Kan Amincewa Da Sabon Albashin  Ma’aikata

October 24, 2025
Ƙarfin Niyyar Manzon Allah (SAW) Da Matakinsa Na Aƙlul A’ala

Ƙarfin Niyyar Manzon Allah (SAW) Da Matakinsa Na Aƙlul A’ala

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.