ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tabbas Mun Samu Tangarda Wurin Shigar Da Sakamakon Zaben 2023 –INEC

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
INEC

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta bayyana cewa tabbas ta samu matsala wurin saka sakamakon zaben shugaban kasa a na’ura, sannan kuma ba ta samu wani taimakon kuda ba daga wurin kowa sai dai gwamnatin tarayya wacce ita ce doka ya daura mata alhakkin yin hakan.

Shughaban hukumar INEC, Farfesa Mahmood Yakubu shi ya bayyana hakan a yayin da yake bayar da ba’asi kan na’urar da aka yi amfani da su a lokacin zaben 2023, a lokacin da yake yi wa kungiyoyin fararen huda bayanai kan nazarin zaben 2023.

  • ’Yan Bindiga Sun Kashe Shugaban JIBWIS, Sun Sace Mutane 50 A Kaduna
  • Badakala A Kano: An Gano Biliyan 4 Da Ta Yi Batan-Dabo A KASCO

Ya kara jaddada cewa abokan hulda sun bayar da tallafi ne kai tsaye ta hanyar kungiyoyin fararen huda wajen gudanar da ayyukan zabe.

ADVERTISEMENT

Shugaban INEC ya gode wa kungiyoyin farar hula da abokan huda ci bisa gagarumin goyon bayan da suka bai wa hukumar a zaben 2023.

Shugaban na INEC ya tunatar da cewa, kungiyoyi 228 (na gida 190 da 38 na kasashen waje) aka amince da su a matsayin masu sanya ido a zaben da ya gabata, 67 ne kawai suka mika rahotonsu ga hukumar kan zabe.

LABARAI MASU NASABA

2027: Sauya Sheka Zuwa APC Ba Zai Taimaki Tinuba Yin Tazarce Ba – Jam’iyyar ADC

‘Yan Adawa Sun Yi Gargadi Kan Barazanar Dakile Dimokuradiyya Mai Jam’iyyu Da Dama

Ya ce: “A kan wannan lamari, ya dace hukumar ta nuna jin dadinta ga kungiyoyin farar hula da abokan hulda bisa gagarumin goyon bayan da suke bai wa hukumar a lokacin zaben 2023.

Wannan ya zo ne ta hanyar shawarwarin kan fasahar sadarwa da ilimantar da masu jefa kuri’a da gudanar da tarurruka da taron kara wa juna sani da kuma buga takardu.

“A wannan hadin gwiwar ne hukumar ta tantance masu sa ido saboda samun jin ra’ayoyi kan zabe da kuma shawarwarin da suka dace wadanda suke taimaka sosai wajen gudanar da zabe. Domin a zaben shekarar 2023, hukumar ta samu korafe-korafe guda 538 (504 na cikin gida da 34 na kasashen waje) daga wurin masu sa ido. Bayan yin cikakken nazari kan korafe-korafen, kungiyoyi 228 ne kawai (190 na cikin gida da 38 na waje) suka cika ka’idodin da aka zayyana. Sai dai kawo yanzu kungiyoyin sa ido 67 ne (62 na cikin gida da kuma na kasashen waje biyar) suka gabatar da rahoton bincikensu wanda ke wakiltar kusan kashi 30 na kungiyoyin da aka amince da su a zaben. Muna kira ga duk sauran kungiyoyin sa ido da aka amince da su wadanda har yanzu ba su gabatar da rahotonsu ba su yi kokarin gabatar wa hukumar.”

Shugaban INEC ya bayyana cewa an samu nasarar tantance masu kada kuri’a ta hanyar amfani da na’urar BBAS, amma kuma an samu matsala wajen shigar da sakamakon zabe ta intanet ta wannan na’ura.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

2027: Sauya Sheka Zuwa APC Ba Zai Taimaki Tinuba Yin Tazarce Ba – Jam’iyyar ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Sauya Sheka Zuwa APC Ba Zai Taimaki Tinuba Yin Tazarce Ba – Jam’iyyar ADC

December 19, 2025
‘Yan Adawa Sun Yi Gargadi Kan Barazanar Dakile Dimokuradiyya Mai Jam’iyyu Da Dama
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Sun Yi Gargadi Kan Barazanar Dakile Dimokuradiyya Mai Jam’iyyu Da Dama

December 19, 2025
Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027
Tambarin Dimokuradiyya

NNPP Ta Buƙaci INEC Ta Yi Watsi Da Tarukan Jam’iyyar Da Kwankwaso Zai Jagoranta

November 28, 2025
Next Post
Yajin aiki: Tinubu Ya Roki Kungiyar Kwadago Da Ta Dan Kara Masa Lokaci

Tinubu Zai Karrama Matar Da Ta Tsinci Dala 80,000 Ta Mayar A Makka

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.