• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Takaitaccen Nazari A Kan Noman Nau’o’in Abinci 7

by Abubakar Abba and Sulaiman
12 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Waiwaye Game Da Shirin “Kauyuka Dubu Goma” Da Daidaita Yanayin Kauyukan Kasar Sin

•Yadda manoma suke aiki a cikin gonakin kauyen Cailu

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Allah ya albarkanci Nijeriya da lokuta biyu na yin noma, wato lokacin rani da kuma damina; wanda a lokacin damina kamar yadda aka saba, ana fara samun ruwan sama ne daga watan Afrilu zuwa na Oktoba.

 

Hakan, na bai wa manoma damar yin shuka tare da girbe nau’ikan amfanin gonan da suka shuka.

  • An Samar Da Naira Biliyan 2.5 Don Bunkasa Ma’adanai A Nijeriya
  • Zaben Shugabanni: Sabon Rikici Ya Kunno Kai A PDP

Manyan amfanin gonar da aka fi nomawa a kakar damina sun hada da; Masara, Shinkafa, Kubewa, Kankana, Tumatir, Tattasai da kuma Rogo.

 

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

1- Masara: Ta kasance daya daga cikin manyan amfanin gona a Nijeriya da ake nomawa a lokacin rani, wadda kuma ake sarrafawa zuwa nau’ikan abinci daban-daban.

Ya fi kyau a shuka Irinta daga watan Afirilu zuwa na Mayu, duba da cewa lokacin ne a ake fara samun mamakon ruwan sama.

Yana da kyau a sani cewa, Masara na bukatar ingantacciyar kasar noma mai kyau tare da danshi mai yawa; sannan dole ne a kula da cire mata Ciyawa, domin ta samu ta girma cikin sauri.

2- Shinkafa: Ita ma na daya daga cikin manyan amfanin gona a Nijeriya, wadda ake shuka Irinta da damina; ana kuma sarrafa nau’ikan abinci ir-iri da ita. Kazalika, ya fi dacewa a shuka Irinta daga watan Afrilu zuwa na Yuli, musamman ganin cewa; a lokacin ne ake samun ruwan sama mai yawan gaske.

Haka zalika, Shinkafa na bukatar a yi mata gyaran gona kafin a shuka Irinta tare da cire mata Ciyawa, don ta samu damar girma da sauri.

3- Kubewa: Ita ma na daya daga cikin kayan lambun da ake nomawa da damina, sannan kuma tana dauke da sinadarin da ke gina jikin Dan’adam.

Kazalika, ta fi dacewa a shuka Irinta daga watan Afrilu zuwa na Yuli; duba da cewa a cikin wadannan watanni ne aka fi samun mamakon ruwan sama.

Har wa yau kuma, tana bukatar kasar noma mai kyau tare da yawan cire mata Ciyawa; don a samu ta yi girma da wuri.

4 Kankana: Ita ma a Nijeriya, ana bukatar a shuka Irinta a lokacin damina; kamar yadda aka sani ne kuma tana dauke da sinadarin da ke gina jikin Dan’adam, ana kuma sarrafa ta zuwa nau’ika daban-daban.

Akasari, an fi shuka Irinta ne daga watan Afrilu zuwa na Mayu; sannan kuma ana bukatar a yi mata gyaran gona kafin a shuka Irinta tare da cire mata Ciyawa, don ta girma da wuri.

5- Tumatir: Yana daya daga cikin kayan lambu da ake shuka Irinsa a Nijeriya a lokacin damina, wanda kuma ya fi kyau a shuka Irinsa daga watan Afrilu zuwa na Mayu tare kuma da shuka Irinsa a kasar noma mai kyau da cira masa Ciyawa, don a samu ya girma da wuri.

6- Tattasai: Shi ma ya kasance daya daga cikin kayan lambun da ake shuka Irinsa a Nijeriya, musamman a lokacin damnina. An fi so a shuka Irinsa daga watan Afrilu zuwa na Mayu, kazalika kuma yana bukatar kasar noma mai kyau tare da danshi, sannan dole a kula da cire masa Ciyawa, domin ya girma da wuri.

7- Rogo: Shi ma ana shuka Irinsa a Nijeriya a lokacin damnina, sannan kuma ana sarrafa shi zuwa nau’ikan abinci daban-daban.

Mafi akasari, an fi bukatar a shuka Irinsa daga watan Afrilu zuwa na Yuni, kana kuma yana bukatar ingantacciyar kasar noma da kuma waje mai matukar danshi, don ya girma da wuri.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kakar Da Ta Fi Dacewa Da Noman Wake A Nijeriya

Next Post

An Ceto Ɗalibai 20 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Binuwe

Related

Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji
Noma Da Kiwo

Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji

1 day ago
Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje
Noma Da Kiwo

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

6 days ago
Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir
Noma Da Kiwo

Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir

1 week ago
Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona
Noma Da Kiwo

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

2 weeks ago
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

2 weeks ago
Abinci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

3 weeks ago
Next Post
An Ceto Ɗalibai 20 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Binuwe

An Ceto Ɗalibai 20 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Binuwe

LABARAI MASU NASABA

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

August 9, 2025
An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

August 9, 2025
Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

August 9, 2025
Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

August 9, 2025
Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

August 9, 2025
Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

August 9, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Jerin Ƴan Wasa Mata Da Suka Samu Kyautar Dala 100,000 Daga Gwamnatin Nijeriya

August 9, 2025
Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

August 9, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

August 9, 2025
ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.