• English
  • Business News
Thursday, July 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Masarautar Zazzau Da Sarakunanta (2)

by Idris Aliyu Daudawa
1 year ago
in Tarihi
0
Tarihin Masarautar Zazzau Da Sarakunanta (2)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jihadin Shehu Usman Dan Fodiyo
Kasar Hausa ta fara daga kewayen Gobir har ya zuwa gefen kasar Bauchi wadda a da can ake kira da kasar Gobir, wadda kuma a ke kira da tsantsan kasar Hausa (sune kasar Gobir, Zamfara, Kebbi, Katsina, Daura, Rano, Ningi da Kano wanda daga baya ne aka samu kasar Sakkwato) ta faka cikin wani irin nau’in hatsin baran addini, watau na hada bori da addinin Musulunci. A cikin wannan hali da ake ciki na bori, Allah Subhanahu Wata’ala ya karfafa zuciyar Mujaddidi Shehu Usman bn Fodiyo da tsaida sunna, kuma ya karfafa shi da samun nasara wajen fahimtar da jama’arsa.Shehu Usman Mujaddadi ya soma kiran jama’a a mahaifarsa Degel.

Sai dai kamar yadda bayanai a cikin littattafan tarihi suka nuna cewar, Mujaddadi Shehu Usmanu shi kansa bai fita zuwa yake-yake ba sai a wuri daya, watau kasar Gobir da kuma yadda Sakkwato ta samu asali.Littattafan tarihi sun kara bayanin haihuwarsa, cewar an haife shi a watan Safar shekara ta 1168 hijirar Manzon Allah,Annabi Muhammadu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi. Allah madaukakin Sarki ya kaddara samun Mujaddadi cikin Jama’an Annabi wanda ya kara tsaida addinin Allah da kafafunsa a zukatan Jama’a bayan karkata ta zo masu (kamar a wannan zamani inda kungiyar Izalatul Bidi’a wa’ ikamatussunna ta bayyana mana’ a yau).Yadda al’amari ya kasance kuwa shi ne, inda aka samu ya yi kokarin kawar da ire-iren wadannan shirkoki da bidi’o’i, duk da wasu sai kara kunno kai suke yi.

  • Tarihin Hadejia Da Sarakunanta (6)
  • Tarihin Hadejia Da Sarakunanta (4)

Shehu Usmanu bai gaza ba musamman ma taimakon Allah da ya samu ta wajen kokartawa har sai da addinin Allah ya daidaitu a zukatan jama’arsa.

Lallai Shehu Usmanu ya amsa sunansa na Mujaddadi kwarai da gaske. Domin ya tsayar da sunna amma kash! mabiyansa sun bijiro da salon son mulki da barna wadda ta fi ta baya. Abin ya kai ga sun kauce wa shari’ar musulunci,na kamanta shi da manzon Allah Muhammadu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi; ko kuma mai da shi abin roko da bautatawa.Haka ma Fulani sun karkata a kan duk wanda bai yi karatu wajen Shehu ba to karkatacce ne,ko da kuwa a ina ya sami ilminsa. Za mu iya samun wannan bayanai ne a wurare da dama da kuma nazarin manufofinsu a zahiri.Amma wasu rubuce-rubucensu na da wuyar samu, musamman yadda su ka farga da cewar jama’a na fahimtar barnarsu ta nazarce-nazarce a kan rubuce-rubucensu da kuma nau’in ayyukansu a zahiri.

A cikin littattafai da ayyuka wasunsu kuwa nada sauyi domin ba a mai da hankali a kansu ba ballantana A Dakatar da su, kuma an mai da su tamkar addinin Allah. Daga cikin wadannan ayyuka da littafai akwai ziyarar kabari da ire-iren shirkoki da bidi’o’in da ke wakana a wuraren, sai littafin Tarihin Fulani na Wazirin Sakkwato, wanda ya rubuta da harsunan Larabci da Hausa. A cikin nazartar littafin zamu iya fahimta barnar tun daga shafi na 8 zuwa shafi na 20 a cikin shi. Misali ya yi bayani kamar haka,”Bushara Da Shehu Usmanu, Allah shi yarda Da Shi:”Hakika bushara an yi da Shehu,Allah shi yarda da shi, tun kafin a san shi, ta abku kamar yadda shi kansa ya ambata cikin littafinsa wanda ya ke maganar kafin bayyanar shi, ta abku kamar yadda shi kansa ya ambata cikin littafinsa wanda yake maganar dangantakarsa zuwa ga Annabi, tsira da amincin Allah su tabbata gare shi,inda ya ce:“Hakika Annabi tsira da amincin Allah su tabbata gare shi an yo bushara da shi tun gabanin zakuwatai. Ni kuma na gode ma Allah an yi bushra da ni.” Haka kuma zancansa ga dangantakarsa zuwa ga Mahadi.Ya ce: “Hakika Mahadi amincin Allah ya tabbata bisa gare shi, an yo bushara da samu shi. Ni kuma na yi godiya ga Allah an yo bushara da ni…”sauran al’amurra kamar yin masa salati bayan anbaton sunansa kamar yadda ake wa ma’aiki Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, da nau’in tsarkakansa kamar na Manzon Allah (S.A.W) watau cewar shi Ma’asumi ne, duba shafi na 9 sakin layi na karke, da dai sauransu. Kamar yadda tarihi ya nuna Shehu Usmanu ya kaurace wa jama’ansa zuwa Gujuba a dalilin irin yadda suka juya wa al’amarin da’awarsa ya zuwa neman abin duniya.

Labarai Masu Nasaba

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Bude Sabon Shafin Internet Na Samar Da Hidimomi Na Kasa Da Kasa Na Beijing

Next Post

Sin Na Da Kananan Jirage Marasa Matuka Sama Da Miliyan 1.26 

Related

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)
Tarihi

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

5 days ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)
Tarihi

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

2 weeks ago
Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)
Tarihi

Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)

2 months ago
Tarihin Shugaannin Kasar Mali Na Farko A Daular Songhai (8)
Tarihi

Tarihin Shugaannin Kasar Mali Na Farko A Daular Songhai (8)

4 months ago
Tarihin Shugaban Ƙasar Mali Na Farko Sundiata Keita (2)
Tarihi

Tarihin Shugabannin Ƙasar Mali Na Farko A Daular Songhai (7)

4 months ago
A-Ula: Dadadden Birni Mai Cike Da Dinbin Tarihi Da Al’adu
Tarihi

A-Ula: Dadadden Birni Mai Cike Da Dinbin Tarihi Da Al’adu

9 months ago
Next Post
Sin Na Da Kananan Jirage Marasa Matuka Sama Da Miliyan 1.26 

Sin Na Da Kananan Jirage Marasa Matuka Sama Da Miliyan 1.26 

LABARAI MASU NASABA

Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza

Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza

July 31, 2025
Za A Kammala Aikin Titin Jirgin Ƙasan Kaduna-Kano A 2026 – Gwamnatin Tarayya

Za A Kammala Aikin Titin Jirgin Ƙasan Kaduna-Kano A 2026 – Gwamnatin Tarayya

July 31, 2025
Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

July 30, 2025
Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

July 30, 2025
Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

July 30, 2025
Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

July 30, 2025
Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

July 30, 2025
Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya

Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya

July 30, 2025
Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

July 30, 2025
Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno

Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno

July 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.