ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Masarautar Zazzau Da Sarakunanta (2)

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Zazzau

Jihadin Shehu Usman Dan Fodiyo
Kasar Hausa ta fara daga kewayen Gobir har ya zuwa gefen kasar Bauchi wadda a da can ake kira da kasar Gobir, wadda kuma a ke kira da tsantsan kasar Hausa (sune kasar Gobir, Zamfara, Kebbi, Katsina, Daura, Rano, Ningi da Kano wanda daga baya ne aka samu kasar Sakkwato) ta faka cikin wani irin nau’in hatsin baran addini, watau na hada bori da addinin Musulunci. A cikin wannan hali da ake ciki na bori, Allah Subhanahu Wata’ala ya karfafa zuciyar Mujaddidi Shehu Usman bn Fodiyo da tsaida sunna, kuma ya karfafa shi da samun nasara wajen fahimtar da jama’arsa.Shehu Usman Mujaddadi ya soma kiran jama’a a mahaifarsa Degel.

Sai dai kamar yadda bayanai a cikin littattafan tarihi suka nuna cewar, Mujaddadi Shehu Usmanu shi kansa bai fita zuwa yake-yake ba sai a wuri daya, watau kasar Gobir da kuma yadda Sakkwato ta samu asali.Littattafan tarihi sun kara bayanin haihuwarsa, cewar an haife shi a watan Safar shekara ta 1168 hijirar Manzon Allah,Annabi Muhammadu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi. Allah madaukakin Sarki ya kaddara samun Mujaddadi cikin Jama’an Annabi wanda ya kara tsaida addinin Allah da kafafunsa a zukatan Jama’a bayan karkata ta zo masu (kamar a wannan zamani inda kungiyar Izalatul Bidi’a wa’ ikamatussunna ta bayyana mana’ a yau).Yadda al’amari ya kasance kuwa shi ne, inda aka samu ya yi kokarin kawar da ire-iren wadannan shirkoki da bidi’o’i, duk da wasu sai kara kunno kai suke yi.

  • Tarihin Hadejia Da Sarakunanta (6)
  • Tarihin Hadejia Da Sarakunanta (4)

Shehu Usmanu bai gaza ba musamman ma taimakon Allah da ya samu ta wajen kokartawa har sai da addinin Allah ya daidaitu a zukatan jama’arsa.

ADVERTISEMENT

Lallai Shehu Usmanu ya amsa sunansa na Mujaddadi kwarai da gaske. Domin ya tsayar da sunna amma kash! mabiyansa sun bijiro da salon son mulki da barna wadda ta fi ta baya. Abin ya kai ga sun kauce wa shari’ar musulunci,na kamanta shi da manzon Allah Muhammadu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi; ko kuma mai da shi abin roko da bautatawa.Haka ma Fulani sun karkata a kan duk wanda bai yi karatu wajen Shehu ba to karkatacce ne,ko da kuwa a ina ya sami ilminsa. Za mu iya samun wannan bayanai ne a wurare da dama da kuma nazarin manufofinsu a zahiri.Amma wasu rubuce-rubucensu na da wuyar samu, musamman yadda su ka farga da cewar jama’a na fahimtar barnarsu ta nazarce-nazarce a kan rubuce-rubucensu da kuma nau’in ayyukansu a zahiri.

A cikin littattafai da ayyuka wasunsu kuwa nada sauyi domin ba a mai da hankali a kansu ba ballantana A Dakatar da su, kuma an mai da su tamkar addinin Allah. Daga cikin wadannan ayyuka da littafai akwai ziyarar kabari da ire-iren shirkoki da bidi’o’in da ke wakana a wuraren, sai littafin Tarihin Fulani na Wazirin Sakkwato, wanda ya rubuta da harsunan Larabci da Hausa. A cikin nazartar littafin zamu iya fahimta barnar tun daga shafi na 8 zuwa shafi na 20 a cikin shi. Misali ya yi bayani kamar haka,”Bushara Da Shehu Usmanu, Allah shi yarda Da Shi:”Hakika bushara an yi da Shehu,Allah shi yarda da shi, tun kafin a san shi, ta abku kamar yadda shi kansa ya ambata cikin littafinsa wanda ya ke maganar kafin bayyanar shi, ta abku kamar yadda shi kansa ya ambata cikin littafinsa wanda yake maganar dangantakarsa zuwa ga Annabi, tsira da amincin Allah su tabbata gare shi,inda ya ce:“Hakika Annabi tsira da amincin Allah su tabbata gare shi an yo bushara da shi tun gabanin zakuwatai. Ni kuma na gode ma Allah an yi bushra da ni.” Haka kuma zancansa ga dangantakarsa zuwa ga Mahadi.Ya ce: “Hakika Mahadi amincin Allah ya tabbata bisa gare shi, an yo bushara da samu shi. Ni kuma na yi godiya ga Allah an yo bushara da ni…”sauran al’amurra kamar yin masa salati bayan anbaton sunansa kamar yadda ake wa ma’aiki Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, da nau’in tsarkakansa kamar na Manzon Allah (S.A.W) watau cewar shi Ma’asumi ne, duba shafi na 9 sakin layi na karke, da dai sauransu. Kamar yadda tarihi ya nuna Shehu Usmanu ya kaurace wa jama’ansa zuwa Gujuba a dalilin irin yadda suka juya wa al’amarin da’awarsa ya zuwa neman abin duniya.

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)

Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya

Zazzau
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

MASU ALAKA

Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Tarihi

Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)

May 30, 2026
Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya
Tarihi

Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya

February 22, 2026
Tarihin Sarkin Zazzau Ja’afaru Dan Isiyaku 1936-1959
Tarihi

Tarihin Sarkin Zazzau Ja’afaru Dan Isiyaku 1936-1959. (2)

January 11, 2026
Next Post
Sin Na Da Kananan Jirage Marasa Matuka Sama Da Miliyan 1.26 

Sin Na Da Kananan Jirage Marasa Matuka Sama Da Miliyan 1.26 

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.