• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Bai Wa Iyalan Wadanda ‘Yan Bindiga Suka Kashe Kyautar 100m A Katsina

by Sadiq
3 years ago
Tinubu

Gwamna Aminu Masari na Jihar Katsina, ya ce dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu, ya bayar da gudummawar Naira miliyan 100 ga iyalan wadanda ‘yan bindiga suka kashe a baya-bayan nan a jihar.

Gwamnan wanda ya bayyana hakan a yayin taron yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC a Katsina, ya ce gwamnatinsa na yin iya bakin kokarinta wajen ganin an kawo karshen matsalar rashin tsaro da jihar ke fuskanta.

  • 2023: Mun Yi Nasarar Gwajin Na’urar Tantance Rajistar Zaɓe – INEC
  • Gwamnatin Nijeriya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Da Aka Yi Wa ‘Yan Banga A Katsina

A cewarsa, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC ya bayar da tallafin ne domin raba wa duk wadanda matsalar tsaro ta shafa a jihar.

Ya kuma yi addu’ar Allah ya gafartawa ‘yan agaji sama da 40 da ‘yan ta’adda suka kashe kwanan nan a jihar.

Ya kuma yi addu’ar Allah Ya tona asirin wadanda suka yi aika-aikar.

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu 

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

Gwamna Masari ya shaida wa taron cewa shugabanci ba abin wasa ba ne, ya kara da cewa, “Batu ne da ke bukatar mutanen da za su iya aiwatarwa.”

Ya yi kira ga jama’a da su tabbatar sun zabi APC a kowane mataki, inda ya ce jam’iyyar ta yi kyakkyawan aiki cikin shekaru bakwai da rabi na mulkinta.

“Lokacin da kuka yi wasa da jagoranci na dakika guda, za ku fuskanci sakamakon shekaru da yawa.

“Zaben 2023 yana tsakanin haske da duhu, kuma APC tana wakiltar haske.

“Damar da sauran mutane suka samu a baya, ba su yi amfani da ita wajen taimaka wa ‘yan Najeriya ba, amma kadan da muka samu, kowa ya ga abin da muka yi.

“Ba a taba samun lokacin da mata da matasa suka shiga harkar siyasa da zabe kamar yanzu ba, saboda shugaban kasa Muhammad Buhari ya kawo wasu tsare-tsare masu yawa.

“Musamman a nan Katsina an raba sama da Naira biliyan 37 a tsakanin masu karamin karfi a jihar cikin shekaru shida kacal.

“Saboda haka, ya kamata ku guji duk wanda zai yi muku karya. Ya kamata ku zabi APC a zabe mai zuwa,” in ji shi.

Gwamna Masari, ya ce da gwamnatocin baya sun yi abin da ya dace, da Nijeriya ba za ta fuskanci matsalar tsaro ba, musamman Boko Haram, satar shanu da jahilci.

A cewarsa, gwamnatocin baya sun samu dama amma sun gaza amfani da ita.

Don haka ya bukaci jama’a da kada su bari wani ya yi musu karya kan rashin tsaro ko talauci.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure
Manyan Labarai

Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 5, 2025
An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai
Manyan Labarai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86
Da ɗumi-ɗuminsa

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
Next Post
Yadda Aka Yi Wa ‘Yan Nijeriya 16 Kisan Gilla A Burkina Faso

Yadda Aka Yi Wa 'Yan Nijeriya 16 Kisan Gilla A Burkina Faso

LABARAI MASU NASABA

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025
Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

November 5, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 5, 2025
Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

November 5, 2025
Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

November 5, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.