ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Bai Wa Iyalan Wadanda ‘Yan Bindiga Suka Kashe Kyautar 100m A Katsina

by Sadiq
3 years ago
Tinubu

Gwamna Aminu Masari na Jihar Katsina, ya ce dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu, ya bayar da gudummawar Naira miliyan 100 ga iyalan wadanda ‘yan bindiga suka kashe a baya-bayan nan a jihar.

Gwamnan wanda ya bayyana hakan a yayin taron yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC a Katsina, ya ce gwamnatinsa na yin iya bakin kokarinta wajen ganin an kawo karshen matsalar rashin tsaro da jihar ke fuskanta.

  • 2023: Mun Yi Nasarar Gwajin Na’urar Tantance Rajistar Zaɓe – INEC
  • Gwamnatin Nijeriya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Da Aka Yi Wa ‘Yan Banga A Katsina

A cewarsa, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC ya bayar da tallafin ne domin raba wa duk wadanda matsalar tsaro ta shafa a jihar.

ADVERTISEMENT

Ya kuma yi addu’ar Allah ya gafartawa ‘yan agaji sama da 40 da ‘yan ta’adda suka kashe kwanan nan a jihar.

Ya kuma yi addu’ar Allah Ya tona asirin wadanda suka yi aika-aikar.

LABARAI MASU NASABA

Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Gwamna Masari ya shaida wa taron cewa shugabanci ba abin wasa ba ne, ya kara da cewa, “Batu ne da ke bukatar mutanen da za su iya aiwatarwa.”

Ya yi kira ga jama’a da su tabbatar sun zabi APC a kowane mataki, inda ya ce jam’iyyar ta yi kyakkyawan aiki cikin shekaru bakwai da rabi na mulkinta.

“Lokacin da kuka yi wasa da jagoranci na dakika guda, za ku fuskanci sakamakon shekaru da yawa.

“Zaben 2023 yana tsakanin haske da duhu, kuma APC tana wakiltar haske.

“Damar da sauran mutane suka samu a baya, ba su yi amfani da ita wajen taimaka wa ‘yan Najeriya ba, amma kadan da muka samu, kowa ya ga abin da muka yi.

“Ba a taba samun lokacin da mata da matasa suka shiga harkar siyasa da zabe kamar yanzu ba, saboda shugaban kasa Muhammad Buhari ya kawo wasu tsare-tsare masu yawa.

“Musamman a nan Katsina an raba sama da Naira biliyan 37 a tsakanin masu karamin karfi a jihar cikin shekaru shida kacal.

“Saboda haka, ya kamata ku guji duk wanda zai yi muku karya. Ya kamata ku zabi APC a zabe mai zuwa,” in ji shi.

Gwamna Masari, ya ce da gwamnatocin baya sun yi abin da ya dace, da Nijeriya ba za ta fuskanci matsalar tsaro ba, musamman Boko Haram, satar shanu da jahilci.

A cewarsa, gwamnatocin baya sun samu dama amma sun gaza amfani da ita.

Don haka ya bukaci jama’a da kada su bari wani ya yi musu karya kan rashin tsaro ko talauci.

MASU ALAKA

Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya
Manyan Labarai

Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya

July 24, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
Manyan Labarai

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 24, 2026
Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC
Manyan Labarai

Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC

July 23, 2026
Next Post
Yadda Aka Yi Wa ‘Yan Nijeriya 16 Kisan Gilla A Burkina Faso

Yadda Aka Yi Wa 'Yan Nijeriya 16 Kisan Gilla A Burkina Faso

LABARAI MASU NASABA

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

July 24, 2026
Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

July 24, 2026
Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

July 24, 2026
An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

July 24, 2026
NNPP Za Ta Kwace Mulki A Jihar Imo – Kwankwaso

Jam’iyyar NDC Ta Shirya Tsaf Domin Kafa Gwamnati A 2027 —Kwankwaso

July 24, 2026
Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

July 24, 2026
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

July 24, 2026
Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.