ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Bai Wa Iyalan Wadanda ‘Yan Bindiga Suka Kashe Kyautar 100m A Katsina

by Sadiq
3 years ago
Tinubu

Gwamna Aminu Masari na Jihar Katsina, ya ce dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu, ya bayar da gudummawar Naira miliyan 100 ga iyalan wadanda ‘yan bindiga suka kashe a baya-bayan nan a jihar.

Gwamnan wanda ya bayyana hakan a yayin taron yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC a Katsina, ya ce gwamnatinsa na yin iya bakin kokarinta wajen ganin an kawo karshen matsalar rashin tsaro da jihar ke fuskanta.

  • 2023: Mun Yi Nasarar Gwajin Na’urar Tantance Rajistar Zaɓe – INEC
  • Gwamnatin Nijeriya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Da Aka Yi Wa ‘Yan Banga A Katsina

A cewarsa, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC ya bayar da tallafin ne domin raba wa duk wadanda matsalar tsaro ta shafa a jihar.

ADVERTISEMENT

Ya kuma yi addu’ar Allah ya gafartawa ‘yan agaji sama da 40 da ‘yan ta’adda suka kashe kwanan nan a jihar.

Ya kuma yi addu’ar Allah Ya tona asirin wadanda suka yi aika-aikar.

LABARAI MASU NASABA

Mulkin Tinubu A Shekara 3:Ina Aka Fito? Ina Aka Dosa?

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

Gwamna Masari ya shaida wa taron cewa shugabanci ba abin wasa ba ne, ya kara da cewa, “Batu ne da ke bukatar mutanen da za su iya aiwatarwa.”

Ya yi kira ga jama’a da su tabbatar sun zabi APC a kowane mataki, inda ya ce jam’iyyar ta yi kyakkyawan aiki cikin shekaru bakwai da rabi na mulkinta.

“Lokacin da kuka yi wasa da jagoranci na dakika guda, za ku fuskanci sakamakon shekaru da yawa.

“Zaben 2023 yana tsakanin haske da duhu, kuma APC tana wakiltar haske.

“Damar da sauran mutane suka samu a baya, ba su yi amfani da ita wajen taimaka wa ‘yan Najeriya ba, amma kadan da muka samu, kowa ya ga abin da muka yi.

“Ba a taba samun lokacin da mata da matasa suka shiga harkar siyasa da zabe kamar yanzu ba, saboda shugaban kasa Muhammad Buhari ya kawo wasu tsare-tsare masu yawa.

“Musamman a nan Katsina an raba sama da Naira biliyan 37 a tsakanin masu karamin karfi a jihar cikin shekaru shida kacal.

“Saboda haka, ya kamata ku guji duk wanda zai yi muku karya. Ya kamata ku zabi APC a zabe mai zuwa,” in ji shi.

Gwamna Masari, ya ce da gwamnatocin baya sun yi abin da ya dace, da Nijeriya ba za ta fuskanci matsalar tsaro ba, musamman Boko Haram, satar shanu da jahilci.

A cewarsa, gwamnatocin baya sun samu dama amma sun gaza amfani da ita.

Don haka ya bukaci jama’a da kada su bari wani ya yi musu karya kan rashin tsaro ko talauci.

MASU ALAKA

Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya
Manyan Labarai

Mulkin Tinubu A Shekara 3:Ina Aka Fito? Ina Aka Dosa?

June 5, 2026
Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
Manyan Labarai

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

June 5, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Yadda Aka Yi Wa ‘Yan Nijeriya 16 Kisan Gilla A Burkina Faso

Yadda Aka Yi Wa 'Yan Nijeriya 16 Kisan Gilla A Burkina Faso

LABARAI MASU NASABA

Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

June 5, 2026
Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 5, 2026
Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya

Mulkin Tinubu A Shekara 3:Ina Aka Fito? Ina Aka Dosa?

June 5, 2026
Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

June 5, 2026
Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

June 5, 2026
Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.