• English
  • Business News
Tuesday, July 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Bai Wa Iyalan Wadanda ‘Yan Bindiga Suka Kashe Kyautar 100m A Katsina

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Tinubu Ya Bai Wa Iyalan Wadanda ‘Yan Bindiga Suka Kashe Kyautar 100m A Katsina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Aminu Masari na Jihar Katsina, ya ce dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu, ya bayar da gudummawar Naira miliyan 100 ga iyalan wadanda ‘yan bindiga suka kashe a baya-bayan nan a jihar.

Gwamnan wanda ya bayyana hakan a yayin taron yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC a Katsina, ya ce gwamnatinsa na yin iya bakin kokarinta wajen ganin an kawo karshen matsalar rashin tsaro da jihar ke fuskanta.

  • 2023: Mun Yi Nasarar Gwajin Na’urar Tantance Rajistar Zaɓe – INEC
  • Gwamnatin Nijeriya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Da Aka Yi Wa ‘Yan Banga A Katsina

A cewarsa, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC ya bayar da tallafin ne domin raba wa duk wadanda matsalar tsaro ta shafa a jihar.

Ya kuma yi addu’ar Allah ya gafartawa ‘yan agaji sama da 40 da ‘yan ta’adda suka kashe kwanan nan a jihar.

Ya kuma yi addu’ar Allah Ya tona asirin wadanda suka yi aika-aikar.

Labarai Masu Nasaba

Mai Gaskiya Ya Koma Gida: Za A Yi Jana’izar Buhari A Daura

Da Ɗumi-Ɗumi: Shettima Ya Isa Katsina Da Gawar Buhari

Gwamna Masari ya shaida wa taron cewa shugabanci ba abin wasa ba ne, ya kara da cewa, “Batu ne da ke bukatar mutanen da za su iya aiwatarwa.”

Ya yi kira ga jama’a da su tabbatar sun zabi APC a kowane mataki, inda ya ce jam’iyyar ta yi kyakkyawan aiki cikin shekaru bakwai da rabi na mulkinta.

“Lokacin da kuka yi wasa da jagoranci na dakika guda, za ku fuskanci sakamakon shekaru da yawa.

“Zaben 2023 yana tsakanin haske da duhu, kuma APC tana wakiltar haske.

“Damar da sauran mutane suka samu a baya, ba su yi amfani da ita wajen taimaka wa ‘yan Najeriya ba, amma kadan da muka samu, kowa ya ga abin da muka yi.

“Ba a taba samun lokacin da mata da matasa suka shiga harkar siyasa da zabe kamar yanzu ba, saboda shugaban kasa Muhammad Buhari ya kawo wasu tsare-tsare masu yawa.

“Musamman a nan Katsina an raba sama da Naira biliyan 37 a tsakanin masu karamin karfi a jihar cikin shekaru shida kacal.

“Saboda haka, ya kamata ku guji duk wanda zai yi muku karya. Ya kamata ku zabi APC a zabe mai zuwa,” in ji shi.

Gwamna Masari, ya ce da gwamnatocin baya sun yi abin da ya dace, da Nijeriya ba za ta fuskanci matsalar tsaro ba, musamman Boko Haram, satar shanu da jahilci.

A cewarsa, gwamnatocin baya sun samu dama amma sun gaza amfani da ita.

Don haka ya bukaci jama’a da kada su bari wani ya yi musu karya kan rashin tsaro ko talauci.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCBuhariKatsinaKyautar Miliyan 100MasariTinubuYakin ZabeYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Shugaban EFCC A Gidan Yarin Kuje 

Next Post

Yadda Aka Yi Wa ‘Yan Nijeriya 16 Kisan Gilla A Burkina Faso

Related

Mai Gaskiya Ya Koma Gida: Za A Yi Jana’izar Buhari A Daura
Manyan Labarai

Mai Gaskiya Ya Koma Gida: Za A Yi Jana’izar Buhari A Daura

6 hours ago
Da Ɗumi-Ɗumi: Shettima Ya Isa Katsina Da Gawar Buhari
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Ɗumi-Ɗumi: Shettima Ya Isa Katsina Da Gawar Buhari

7 hours ago
Tinubu Ya Isa Katsina Don Tarbar Gawar Buhari
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Katsina Don Tarbar Gawar Buhari

7 hours ago
Buhari Na Cikin Ƙoshin Lafiya Kwana Ɗaya Kafin Rasuwarsa – Mamman Daura
Manyan Labarai

Buhari Na Cikin Ƙoshin Lafiya Kwana Ɗaya Kafin Rasuwarsa – Mamman Daura

8 hours ago
Buhari Da Ya Daɗe Da Rasuwa Idan A Asibitocin Nijeriya Ake Duba Shi – Adesina
Manyan Labarai

Buhari Da Ya Daɗe Da Rasuwa Idan A Asibitocin Nijeriya Ake Duba Shi – Adesina

9 hours ago
HOTUNA: An Tsaurara Tsaro A Gidan Buhari Da Ke Daura
Hotuna

HOTUNA: An Tsaurara Tsaro A Gidan Buhari Da Ke Daura

10 hours ago
Next Post
Yadda Aka Yi Wa ‘Yan Nijeriya 16 Kisan Gilla A Burkina Faso

Yadda Aka Yi Wa 'Yan Nijeriya 16 Kisan Gilla A Burkina Faso

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

July 15, 2025
An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

July 15, 2025
Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

July 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

July 15, 2025
Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

July 15, 2025
Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

July 15, 2025
Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

July 15, 2025
Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba

Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba

July 15, 2025
Bayan Shekaru 6 A Hannun Boko Haram, Wasu Yara Biyu Sun Kuɓuta

Bayan Shekaru 6 A Hannun Boko Haram, Wasu Yara Biyu Sun Kuɓuta

July 15, 2025
Mai Gaskiya Ya Koma Gida: Za A Yi Jana’izar Buhari A Daura

Mai Gaskiya Ya Koma Gida: Za A Yi Jana’izar Buhari A Daura

July 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.