• English
  • Business News
Wednesday, July 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Rikicin Manoma Da Makiyaya A Nijeriya

by Abubakar Abba
8 months ago
in Labarai
0
Tinubu Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Rikicin Manoma Da Makiyaya A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya jaddada cewa; gwamnatinsa ta mayar da hankali wajen lalubo masu son zuba hannun jari a fannin kiwo a Nijeriya.

A cewar tasa, ta hakan ne za a iya kawo karshen yawan samun rikice-rikice a tsakanin Manoma da Makiyaya a fadin kasar tare da yakar yunwa da fatara da kuma kara habaka tattalin arzikin Nijeriyabaki-daya.

  • Nijeriya Ta Shirya Magance Matsalar Almajirai – Tinubu Ga Macron
  • Tinubu Zai Tafi Afirka Ta Kudu Daga Faransa

Tinubu ya bayyana haka ne, a cikin sanarwar da mai ba shi shawara na musamman a fannin sadarwa da tsare-tsare; Bayo Onanuga ya fitar a birnin de Janeiro,  na Kasar Brazil.

Sanarwar ta ce, shugaban ya yi wannan furuci ne a jawabinsa, bayan sanya hannu da wani kamfanin sarrafa Nama (JBS), a birnin Rio de Janeiro na kasar Brazil ya yi.

Kamfanin, ya kasance daya daga cikin manyan kamfanoni a duniya da ke sarrafa Nama.

Labarai Masu Nasaba

Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

A cewar tasa, abin da muka mayar da hankali yanzu a Nahiyar Afirka shi ne, lalubo mafita a kan rikice-rikicen Manoma da Makiyaya, musamman don rage asarar rayuka da dukiyoyi da kuma kara dawo da martabar kiwo.

Har ila yau, ya bukaci kamfanin ya yi amfani da wannan dama wajen sanya hannun jarin na kimanin dala biliyan 2.5, inda ya bai wa kamfanin tabbacin cewa; za a samar musu da kyakkyawan yanayi na yin kasuwanci.

Shi kuwa, Ministan Ma’aikatar Bunkasa Kiwon Dabbobi; Idi Muhktar Mahia, wanda ya jagoranci wata tawaga da Tinubu ya tura zuwa taron kafin ya isa kasar ta Brazil, a jawabin da ministan ya yi wa Tinubu ya sheda masa cewa, ya kai ziyara ga wasu manyan kamfanoni a Brazil; domin duba yadda suke gudanar da ayyukansu da kayan aiki na zamani kan sarrafa Nama.

Kamfanin na JBS S.A, na sarrafa Shanu 33,000 tare da tsintsaye sama da miliyan takwas, wanda ya sanar da cewa; yana da kyau Nijeriya ta yi hadaka da su.

Idi ya kara da cewa, kamfanin na da ma’aikata sama da 200,000 da suka fito daga sama da kasashe 50, ciki har da Kasar Amurka Kanada, Mexico da kuma Saudiya.

Haka zalika, shugaban kamfanin Wesley Batista; ya bayyana jin dadinsa kan yunkurin wannan hadaka, inda ya sanar da cewa; mun ji dadi da za mu yi aiki da Nijeriya, domin kara habaka fannin kiwon kasar.

Haka nan, Batista ya bayar da tabbacin cewa; nan ba da jimawa ba ake sa ran, kamfanin na  JBS; zai fara gudanar da ayyukansa a Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Makiyaya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwarzon ÆŠan Kasuwa Na Shekarar 2024: Benedict Peters

Next Post

Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati 2024: Shugaban Kwastam, Alh. Bashir Adewale Adeniyi

Related

Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari
Labarai

Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

7 hours ago
VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano
Labarai

VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

7 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

10 hours ago
Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China
Labarai

Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

11 hours ago
Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba
Ra'ayi Riga

Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba

12 hours ago
Bayan Shekaru 6 A Hannun Boko Haram, Wasu Yara Biyu Sun Kuɓuta
Labarai

Bayan Shekaru 6 A Hannun Boko Haram, Wasu Yara Biyu Sun Kuɓuta

13 hours ago
Next Post
Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati 2024: Shugaban Kwastam, Alh. Bashir Adewale Adeniyi

Gwarzon Ma'aikacin Gwamnati 2024: Shugaban Kwastam, Alh. Bashir Adewale Adeniyi

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

July 15, 2025
Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

July 15, 2025
VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

July 15, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

July 15, 2025
An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

July 15, 2025
Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

July 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

July 15, 2025
Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

July 15, 2025
Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

July 15, 2025
Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

July 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.