• English
  • Business News
Thursday, May 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Rikicin Manoma Da Makiyaya A Nijeriya

by Abubakar Abba
6 months ago
in Labarai
0
Tinubu Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Rikicin Manoma Da Makiyaya A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya jaddada cewa; gwamnatinsa ta mayar da hankali wajen lalubo masu son zuba hannun jari a fannin kiwo a Nijeriya.

A cewar tasa, ta hakan ne za a iya kawo karshen yawan samun rikice-rikice a tsakanin Manoma da Makiyaya a fadin kasar tare da yakar yunwa da fatara da kuma kara habaka tattalin arzikin Nijeriyabaki-daya.

  • Nijeriya Ta Shirya Magance Matsalar Almajirai – Tinubu Ga Macron
  • Tinubu Zai Tafi Afirka Ta Kudu Daga Faransa

Tinubu ya bayyana haka ne, a cikin sanarwar da mai ba shi shawara na musamman a fannin sadarwa da tsare-tsare; Bayo Onanuga ya fitar a birnin de Janeiro,  na Kasar Brazil.

Sanarwar ta ce, shugaban ya yi wannan furuci ne a jawabinsa, bayan sanya hannu da wani kamfanin sarrafa Nama (JBS), a birnin Rio de Janeiro na kasar Brazil ya yi.

Kamfanin, ya kasance daya daga cikin manyan kamfanoni a duniya da ke sarrafa Nama.

Labarai Masu Nasaba

Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027 

A cewar tasa, abin da muka mayar da hankali yanzu a Nahiyar Afirka shi ne, lalubo mafita a kan rikice-rikicen Manoma da Makiyaya, musamman don rage asarar rayuka da dukiyoyi da kuma kara dawo da martabar kiwo.

Har ila yau, ya bukaci kamfanin ya yi amfani da wannan dama wajen sanya hannun jarin na kimanin dala biliyan 2.5, inda ya bai wa kamfanin tabbacin cewa; za a samar musu da kyakkyawan yanayi na yin kasuwanci.

Shi kuwa, Ministan Ma’aikatar Bunkasa Kiwon Dabbobi; Idi Muhktar Mahia, wanda ya jagoranci wata tawaga da Tinubu ya tura zuwa taron kafin ya isa kasar ta Brazil, a jawabin da ministan ya yi wa Tinubu ya sheda masa cewa, ya kai ziyara ga wasu manyan kamfanoni a Brazil; domin duba yadda suke gudanar da ayyukansu da kayan aiki na zamani kan sarrafa Nama.

Kamfanin na JBS S.A, na sarrafa Shanu 33,000 tare da tsintsaye sama da miliyan takwas, wanda ya sanar da cewa; yana da kyau Nijeriya ta yi hadaka da su.

Idi ya kara da cewa, kamfanin na da ma’aikata sama da 200,000 da suka fito daga sama da kasashe 50, ciki har da Kasar Amurka Kanada, Mexico da kuma Saudiya.

Haka zalika, shugaban kamfanin Wesley Batista; ya bayyana jin dadinsa kan yunkurin wannan hadaka, inda ya sanar da cewa; mun ji dadi da za mu yi aiki da Nijeriya, domin kara habaka fannin kiwon kasar.

Haka nan, Batista ya bayar da tabbacin cewa; nan ba da jimawa ba ake sa ran, kamfanin na  JBS; zai fara gudanar da ayyukansa a Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Makiyaya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwarzon Ɗan Kasuwa Na Shekarar 2024: Benedict Peters

Next Post

Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati 2024: Shugaban Kwastam, Alh. Bashir Adewale Adeniyi

Related

Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 
Labarai

Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

1 hour ago
Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027 
Manyan Labarai

Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027 

2 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

INEC Ta Samar Da Sashen Ƙirƙirarriyar Basira Domin Inganta Harkokin Zaɓe 

4 hours ago
Ingancin Tattalin Arzikin Sin Mai Bude Kofa Na Bayyana Sosai Duba Da Yawan Zuwan Baki Masu Sayayya
Ra'ayi Riga

Ingancin Tattalin Arzikin Sin Mai Bude Kofa Na Bayyana Sosai Duba Da Yawan Zuwan Baki Masu Sayayya

5 hours ago
Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi
Labarai

Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi

6 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Kashe Naira Tiriliyan 1.5 Don Magance Matsalar Abinci — Minista
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Kashe Naira Tiriliyan 1.5 Don Magance Matsalar Abinci — Minista

6 hours ago
Next Post
Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati 2024: Shugaban Kwastam, Alh. Bashir Adewale Adeniyi

Gwarzon Ma'aikacin Gwamnati 2024: Shugaban Kwastam, Alh. Bashir Adewale Adeniyi

LABARAI MASU NASABA

Modric Zai Bar Real Madrid Bayan Kammala Gasar Cin Kofin Duniya Na Kungiyoyi

Modric Zai Bar Real Madrid Bayan Kammala Gasar Cin Kofin Duniya Na Kungiyoyi

May 22, 2025
Yawan Wutar Lantarkin Da Sin Ke Iya Samar Ta Amfani Da Karfin Ruwa Ta Kai Matsayin Koli A Duniya

Yawan Wutar Lantarkin Da Sin Ke Iya Samar Ta Amfani Da Karfin Ruwa Ta Kai Matsayin Koli A Duniya

May 22, 2025
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

May 22, 2025
Darussan Koyi Daga Salon Bunkasa Kasa Na Sin

Darussan Koyi Daga Salon Bunkasa Kasa Na Sin

May 22, 2025
Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027 

Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027 

May 22, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Faransa

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Faransa

May 22, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

INEC Ta Samar Da Sashen Ƙirƙirarriyar Basira Domin Inganta Harkokin Zaɓe 

May 22, 2025
Ingancin Tattalin Arzikin Sin Mai Bude Kofa Na Bayyana Sosai Duba Da Yawan Zuwan Baki Masu Sayayya

Ingancin Tattalin Arzikin Sin Mai Bude Kofa Na Bayyana Sosai Duba Da Yawan Zuwan Baki Masu Sayayya

May 22, 2025
Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi

Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi

May 22, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kashe Naira Tiriliyan 1.5 Don Magance Matsalar Abinci — Minista

Gwamnatin Tarayya Ta Kashe Naira Tiriliyan 1.5 Don Magance Matsalar Abinci — Minista

May 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.