ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Rikicin Manoma Da Makiyaya A Nijeriya

by Abubakar Abba
2 years ago
Tinubu

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya jaddada cewa; gwamnatinsa ta mayar da hankali wajen lalubo masu son zuba hannun jari a fannin kiwo a Nijeriya.

A cewar tasa, ta hakan ne za a iya kawo karshen yawan samun rikice-rikice a tsakanin Manoma da Makiyaya a fadin kasar tare da yakar yunwa da fatara da kuma kara habaka tattalin arzikin Nijeriyabaki-daya.

  • Nijeriya Ta Shirya Magance Matsalar Almajirai – Tinubu Ga Macron
  • Tinubu Zai Tafi Afirka Ta Kudu Daga Faransa

Tinubu ya bayyana haka ne, a cikin sanarwar da mai ba shi shawara na musamman a fannin sadarwa da tsare-tsare; Bayo Onanuga ya fitar a birnin de Janeiro,  na Kasar Brazil.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta ce, shugaban ya yi wannan furuci ne a jawabinsa, bayan sanya hannu da wani kamfanin sarrafa Nama (JBS), a birnin Rio de Janeiro na kasar Brazil ya yi.

Kamfanin, ya kasance daya daga cikin manyan kamfanoni a duniya da ke sarrafa Nama.

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

A cewar tasa, abin da muka mayar da hankali yanzu a Nahiyar Afirka shi ne, lalubo mafita a kan rikice-rikicen Manoma da Makiyaya, musamman don rage asarar rayuka da dukiyoyi da kuma kara dawo da martabar kiwo.

Har ila yau, ya bukaci kamfanin ya yi amfani da wannan dama wajen sanya hannun jarin na kimanin dala biliyan 2.5, inda ya bai wa kamfanin tabbacin cewa; za a samar musu da kyakkyawan yanayi na yin kasuwanci.

Shi kuwa, Ministan Ma’aikatar Bunkasa Kiwon Dabbobi; Idi Muhktar Mahia, wanda ya jagoranci wata tawaga da Tinubu ya tura zuwa taron kafin ya isa kasar ta Brazil, a jawabin da ministan ya yi wa Tinubu ya sheda masa cewa, ya kai ziyara ga wasu manyan kamfanoni a Brazil; domin duba yadda suke gudanar da ayyukansu da kayan aiki na zamani kan sarrafa Nama.

Kamfanin na JBS S.A, na sarrafa Shanu 33,000 tare da tsintsaye sama da miliyan takwas, wanda ya sanar da cewa; yana da kyau Nijeriya ta yi hadaka da su.

Idi ya kara da cewa, kamfanin na da ma’aikata sama da 200,000 da suka fito daga sama da kasashe 50, ciki har da Kasar Amurka Kanada, Mexico da kuma Saudiya.

Haka zalika, shugaban kamfanin Wesley Batista; ya bayyana jin dadinsa kan yunkurin wannan hadaka, inda ya sanar da cewa; mun ji dadi da za mu yi aiki da Nijeriya, domin kara habaka fannin kiwon kasar.

Haka nan, Batista ya bayar da tabbacin cewa; nan ba da jimawa ba ake sa ran, kamfanin na  JBS; zai fara gudanar da ayyukansa a Nijeriya.

Tinubu
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
Next Post
Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati 2024: Shugaban Kwastam, Alh. Bashir Adewale Adeniyi

Gwarzon Ma'aikacin Gwamnati 2024: Shugaban Kwastam, Alh. Bashir Adewale Adeniyi

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.